Showing 225001 words to 228000 words out of 403653 words
zafi suke mun, kana kara sanya ciwon cikina ya dawo sabo fa". Ni kam na ce ciwon ciki ko rashin kunya?.
Wani irin abu ya ji tamkar an caka mashi allura, yadda ta yi maganar tamkar kara ingiza zuciyarsa ta yi, can kasan maƙoshinsa ya furta. "Am so sorry, amma dai yau ki barni na ji ɗumin kayana, ba kema haka kike so ba?".
A miliyan ta zaro idanunta waje. "Ni kuma Yah Jaish? Yaushe nace maka ina son hakan?". Tana magana tana zaro idanu da mamaki a saman face ɗinta.
Matso da ɗan bakinsa saitin kunnenta ya yi. "Ai kina jin daɗi ne idan ina taɓasu shiyasa nace kema kina so, kuma ba ke kika faɗo jikina ba?".
Yunƙura ta yi zata miƙe tana faɗin. "Ni na faɗo jikinka ne kawai dan ka rarrasheni na ciwon da cikina yake mun, amma bari na koma seat ɗina in zauna, in cigaba da kukana idan mun koma gida mommata ko Yah Omar su rarrasheni tun da dama su suka saba rarrashina idan ina kuka, kai dama babu ruwanka dani kace..............."
Bata kai karshen maganar ba ta yanke tsit sakamakon jawota da ya yi ta faɗo saman lion chest ɗinsa ya kuma haɗe bakinsu waje guda, zazzafar kiss ya shiga bata babu kama hannun yaro.
Ita ma mayar mashi da martani ta fara yi har da zura tongue ɗinta a cikin ɗan bakinsa tana kara tayarwa da baban Allah tsumin samartakansa. (Bari in yi sauri in je in faɗawa Queen Zarina ga shi nan Mahnoor zata kwacewa saurayinta samartakansa ta zo ta rabasu, ni ba zan ci amana ba, dole in sanar da Queen dan akwai amana🥱)
Cigaba da bata kiss masu zafa ya rinƙa yi tare da mayar da hannayensa saman tula tulan nata yana aikin matsesu. Dik suka rikita juna a cikin mota, ita ma kun san ta jima tana kewar kiss ɗinsa.
Cikin dabara ya zame ɗan bakinsa daga cikin tata. A hankali ya shammaceta ya mayar da shi saman nipples ɗinta, bata yi zaton hakan ba sai ta ji ɗan zafi ya ziyarceta.
Ai bata san lokacin da ta waro idanunta waje ba, a saman kansa ta ɗaura hannayenta dikka biyu ta fara aikin zuba mashi kukan shagwaɓa dake kara rikirkita shi tana kara ingiza zuciyarsa yana yin abu da zafa zafa.
Wannan ƴar shagwaɓa da take zuba mashi ba ƙaramin kara tura zuciyarsa gaba wajen ingiza mashi ya kai babbar level yake yi ba.
A miliyan ta kwace kanta daga garesa tare da zabura zata bar jikinsa a lokacin da ta ji saukar hannunsa a saman mararta. Riƙota ya yi tare da dawo da ita jikinsa yana girgiza mata kai alamar kada ta tashi bai iya furta word ba, jikinsa dik a mace.
Ba dan ta so ba ta koma ta kwanta, sai dan bata son ta yi jayayya da shi. Matseta ya yi a jikinsa yana wani irin fitar da numfashi kamar wanda yake............ .
Shiru ta lafe har na tsawon awa guda bai iya motsawa ba, ƙoƙarin danne samartakansa kawai yake yi dan kada ya yi aika aika a cikin mota, da ma dai a gida ne sai ya saki ji.
Sai da suka yi awa ɗaya da rabi a wajen kafin ya ɗan iya motsawa ya tada kujeran motar, ya kara rungumota da kyau a jikinsa yana sauke ajiyar zuciya, ya fara ƙoƙarin kunna motar dan su tafi.
"Yah Jaish bari na koma saman seat ɗina in zauna sai mu tafi". Ta faɗi hakan ba tare da maganar ta fito daga cikin zuciyarta ba, dan ita ma bata son barin jikin nasa, ta dai faɗa ne kawai.
Kai ya girgiza mata alamar a'a kawai ba tare da ya furta word ba, sai ma kara matseta da ya yi a jikinsa yana ɗan shasshafa bayanta da hannu ɗaya, sannan ya tashi motar a kan su tafi............
••••••••••••••••••••••••••••••••🔥🔥🔥
DR RAJ.
A ƙagare yake da san jin amsar da Zee zata bashi , dan yana.......
P_R_I_N_C_E_S_S__T_E_E_M_A...✍️🔥🕊️
For more information 08161390581 Whatsapp me only!!.
🤍KADA KU MANTA WANNAN DADDAƊAR LABARIN DAGA ALKALAMIN FATEEMA ZAHRA MUSA A-K-A PRINCESS TEEMA TAKU TA AMANA YAKE🔥💘
ALLAH KA KARA MANA SON MANZON ALLAH 🔥🤍
========🔥🔥🔥=========
MALLAKIN🔥
P_R_I_N_C_E_S_S__T_E_E_M_A...✍️🔥🕊️
اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ❤️
DR RAJ.
A ƙagare yake da san jin amsar da Zee zata bashi, dan yana sanin me zai yi next. Ita kuwa sai da ta tsaya shiru a kallah na tsawon 5 mins tana kallansa kafin ta girgiza mashi kai alamar a'a bata san shi, sannan ta ɗan kwace hannunta da yake rike da shi, rage tsawonta ta yi ta duka ta raɓa gefensa ta wuce.
Shock rooted him to the spot, his mind struggling to process the reality before him. Was it truly Akka’s blood that had dared to confess love, only to be rejected? The thought felt strange, almost unreal.
For almost thirty minutes, he remained standing there, lost in deep thought. Deep down, he knew Zee had feelings for him, he had seen it in her eyes. But the way she responded had unsettled him. After a while, he convinced himself that she was only playing hard to get and that he could win her over.
With a composed demeanor, he walked back to the sofa and sank into it, replaying the intense moment when their eyes had locked. Pulling his phone from his pocket, he dialed Yah Ramish’s number, eager to know whether he had finally given Leesharh to the blood or he was still stalling, just as he always did. wlh Ramish ɗan duniya ne, idan ba kana da hakuri ba zaka iya rataye kanka saboda bakincikinsa, mutum kamar dutse, in ya yi magana ba canzawa, ko da yake ba za'ayi mamaki a tin da kanin Smart ne, duk jirgi ɗaya ya kwasosu ya kawosu dama, ƴan rainin wayo da kawunansu kamar na Akka ...........🥱
Sau biyu yana kiransa bai ɗaga kiran ba sai a karo na uku, murya can ƙasa ƙasa ya ce Hello. Dr ya fahimci barci ma yake yi, amma sai ya daure wajen cewa. "Yah Ramish good evening".
A mainakon ya amsa gaisuwar tasa sai ya ce. "Is there any special reason why you're calling me at this time?"........ Shiru Dr ya ɗan yi, kamar zai katse kiran ya kyalesa ya cigaba da barcinsa sai kuma ya daure ya ce. "Yah Ramish dama batun blood ɗin nan ne, please mana ka bata ka ji our hero?.........".
Bai gama rufe baki a maganar ba ɗiff Ramish ya katse kiran, ajiyar zuciya ya sauke yana mamakin halin yayan nasa, mutun ne babu ɗigon tausayi a ransa. Ajiye wayar a gefensa ya yi ya cigaba da tinanin Zee abinsa.
•••••••••••••••••••••••••••••••••🔥🔥
Sanye take da sleeping dress riga da wando masu zubin pajamas, tana tafiya tana taunar chewing gum kamar wata wadda abin suka motsa. Daga bedroom na mama Haulat ta fito, tana tafiya tana wani kwarkwasa da rangwaɗa, ji take yi ta fi kowa tun da ta yi kwalliya, yanzu mama Haulat ta koya mata yanga, kamar ba Mahreen tamu ta bappa ba, har yauki take yi, kun santa da shegen san kwalliya tin a kauye, to da ta zo yanzu kullun cikin kwalliya mai kyau da ɗaukar hankali take, ta zama big girl mai class yar gayu.
Sai dai har yau har gobe tana kukan sauyawar da Jaish ya yi, ya tashi daga hammanta izuwa Jaish, kuma kullun idan ta gansa bata gajiya da yi mashi magana, ko ya amsa ko karya amsa sai ta yi mashi.
Kai tsaye part na mama ta nufa dan ta je wajen Zee, yanzu sun fara sabo da su Zee, kuma Zee tana koya mata karatu bata da matsala, rike take da takardanta ma a yanzu, ta yi jagwalgwalan rubutunta kamar tafiyar tsutsa shi ne zata kaiwa Zee ta duba mata.
Har zata shiga part ɗin mama sai ta kalli kofar part dake fuskantar nasu mama ɗin a buɗe. Mamaki ne ya ɗan kamana ganin cewa bata taɓa kallan kofar a buɗe ba, da sauri ta dakata daga shiga side ɗin mama, babu ko tsoro a ranta, bata san bedrooms ɗin su waye a wajen ba kawai ta nufa abinta, tana tafiya babu ɗar ɗar bare waige waige. Kai tsaye ta shige ciki.
Babu ko sallama ta afaka masu cikin parlournsu. Suna zuane a saman sofa suna aikin latsan waya, Obaid ya tada kai da cinyar Omaid yana video call da Sharifat, shi kuma Omaid yana waya da ɗaya daga cikin class mate ɗinsu, su da basa murmushi saboda muguntar da ta yi masu yawa sai ga Omaid yana ɗan murmusawa alamar waya ta yi daɗi kenan.
Shirye suke cikin sleeping dress ɗinsu iri ɗaya, kayan ya yi matikar yi masu kyau, Omaid ya tara gashinsa ta yi tsawo, shi kuma Obaid ya yanke arab hairn nasa, ya yi irin askin guyson, kuma ya yi kyau, ga shi dikkansu sun yi gyaran fuska, ƴaƴan momma fa ɗaukar wanka a jininsu yake, wlh dik kalar wankan da suka ɗauka kyau suke yi wa wankan.
Ganin mutum a tsakiyar parlon nasu yasa Obaid sarkin zafa ya miƙe zaune yana binta da kallo tare da katse call da yake yi, shi kuma Omaid kallan wutsiyar ido ya bita da shi suna mamakin zubin halittarta, a cewarsu ta yi siririya sosai.
"Who are you?". Omaid ya faɗa ba tare da ya kalli in da take tsaye ba, kallan gefe ya bita da shi.
To ita dai ba jin turanci take yi ba, dan haka bata san me suka faɗa ba, da ɗan gara ma larabci ne yanzu ta iya dik da ba wani mai zurfi sosai ba, amma zata iya maganar minti uku cikakke da kai da larabci, abin da yasa kuma ta yi saurin iyawa saboda zamanta da su mama Haulat, babu wani yare da zasu iya magana da juna dole sai larabci, hakan yasa ta yi saurin iyawa.
So bata san me suka faɗa ba, sai bata amsa su ba, ta tsaya shiru tana binsu da kallo, taga zubin halittar Jaish a tattare da su, kun san tun da suka zo basu haɗu da ita ba.
Obaid sarkin zafa ne ya daka mata tsawa cikin harshen larabci. "Zaki faɗa mana wacecce ke da abin da ya kawoki part ɗinmu ne ko sai na tashi na kakkaryaki?". Yana magana yana kara ɗaure fuska.
Sarai ta ji wannan magana da ya faɗa, kun san bata barin ko ta kwana, jin zai daketa da ya faɗa yasa ta sanya hannu ta rike waist ɗinta da kyau, kallan up and down ta bisu da shi kafin cikin tsiwa ta ce.
"Tun da kai ka halicceni ba sai ka dakeni in gani ba! Kana tinanin ma barinka zan yi ka taɓa ni ne? Wlh baka isa ba, ramawa zan yi". Tana jajjagen masifar tata kuma tana kallon kofar fita, ta gama yin ready kis take jira ta yanka waje a miliyan.
Kun san Obaid dama shi baya da hakuri ko kaɗan, aikuwa ransa ya gama ɓaci, a gabaɗaya kingdom of power babu wanda yake yi masu nasiha cikin ruwan sanyi ma ya zauna lafiya sai Jaish bayan Momma, amma saboda tsabar aljanun kanta na guguwar bishiyar kuka ce zata tsaya a tsakiyar parlournsu, su tambayi meya kawota har ta ce zata faɗa masu magana, wlh yau sai dai wata ba ita ba koma ƴar uban wanene ne.
Sai huci yake yi ya miƙe tsaye, Omaid ne ya yi saurin rike hannunsa yana faɗin. "Kai mezaka yi mata?". A fusace ya amsa da. "Mekake tinanin zan yi mata? Ni ka sakeni dan Allah hai".
"Obaid kana tinanin in ka taɓa wannan tsinken tsintsiyar zata rayu ne? Ka rabu da ita kada ka je ka yi kisan kai, ka ganta fa kamar sandar mopa...........".
Ana ƙoƙarin bashi hakuri a taushesa amma yarinyar nan tun Omaid bai gama rufa baki ba ta cafke zancen da cewa. "Tun da dik cikinku babu ɗan iskan da ya yi mun halitta sai ku rufe babin batun halittata, da kake ce mun sanda kai ya kake? Da shegen idanunka manya manya kamar na shaiɗan"......... Kai jama'a ko a ina Mahreen ta taɓa ganin shaiɗan har tasan idanunsa manya ne? Omaid kai ma ka shiga layin littafin Mahreen.
Ai sake Obaid Omaid ya yi, wato ya je ya lallasata kenan tin da ita bata san mutunci ba. Tana tsaye ya nufota cikin zafa, sai da ta bari ya kusanta sai ta yanka waje a miliyan. Ai da gudu ya rufa mata baya, shi kuma Omaid ya cigaba da yin wayarsa abinsa.
Kai tsaye part ɗin momma ta nufa da gudun gaske. Tana sanyo kai suka ci karo da guyson da ya fito daga bedroom ɗin momma zai koma nasa dare ta yi. Karo suna yi a in da ya ɗan yi baya yana dafe goshinsa da ta bugesa.
Ita kuwa da yake tasan abin da ta tsokano sai bata tsaya ba, a guje ta raɓa gefensa zata wuce, da sauri ya riko hannunta, cikin natsuwa ya ce. "Lafiya kike gudu haka a cikin daren nan?".
Ƙoƙarin kwace hannunta ta yi dan ta ruga da gudun ta karisa ciki.
Shi kuma bai gama rufe baki ba sai ga Obaid ya iso wajen da gudu. Da karfi ya sanya hannu zai fisgota daga rikon da guyson ya yi mata yana wani huci. A hanzarce guyson ya dakatar da shi ta hanyar cewa. "Ku dakata mana, lafiya Obaid ka biyota? Me ta yi maka?".
Har lokacin ƙoƙarin kwace kanta take yi ta gudu. Ɗaure fuska sosai Obaid ya yi, cikin ɓacin rai ya zayyana mashi dik abin da ya faru, daga karshe ya ce wlh idan bai karyata pieces ba ba zai iya yin barci ba yau. Dik da guyson yana rike da ita yana ƙoƙarin kashe wutar da ta kunna bakinta bai rufu ba, dan kuwa tana jin Obaid ya ce sai ya karyata cikin tsiwa ta ce.
"Ka karyani tun da ni itace ce, da wani shegen ido kamar na shaiɗan na faɗa na kara faɗa".
Me guyson zai yi idan ba murmushi ba, shi ya rasa wace iriyar yarinyace, ji fa, ana ƙoƙarin kashe wuta tana kara kunna wani.
A fusace Obaid ya matsota yana faɗin. "Yah Omar dan Allah ka kyaleni in karya yarinyar nan".
"Dakata dakata Obaid, wai baka ga mace bace? Me zaka daka a wajen? Su mata ai babu gurbin duka a jikinsu ko?...........".
Guyson bai gama rufe baki ba ta capki zancen da cewa. "Kai kana tinanin kana da karfin dukana ne da kake wani tadada jijiyoyin wuya? Wlh ni na ci dubu sai ceto, kuma kai ma ka sakeni tun da baka da wani karfi mai kukan ciwo kawai". A karshen maganar tata da guyson take yi, wai bashi da karfin tare mata faɗa tin da yana kukan ciwo, larabcin nata ne a karkace.
Sarai Guyson ya fahimci kalamanta, ya fahimci zaginsa ta yi, amma da yake shi ɗin damone sarkin hakuri, sai ya yi kamar bai ji ba, yasan idan ya barta da Obaid wlh ko momma ba iya kashe wannan wuta zata yi ba, dan ko an bashi hakuri ya tafi sai ya sakar mata kunama ko kwari, basa yafiya ai, dan haka solution kawai ya kashe wutar a nan mai gabaɗaya.
Capka Obaid ya kai mata da karfi zai shaki wuyarta Guyson ya yi saurin janyeta da karfi sai ta tafi ta faɗa saman kirjinsa, a hanzarce ya ce. "Obaid ka kyaleta mu yi magana mana".
"Ni Yah Omar ka barni in take bakin yarinyar nan sai hakwaranta sun cire gabaɗaya". "Aa Obaid, ba za'ayi haka ba, ka bari za ta baka hakuri..........". Bai kamala kai karshen maganar ba ya dakata sakamakon turesa da karfi da ta yi har ya yi baya kamar zai faɗi. Cikin tsiwa ta ce. "Kai ɗan iska ne ashe? Allah ya isa da ka rungume ni". Tana magana tana galla mashi harara.
A zabure Obaid ya nufeta yana dunkule hannunsa ɗaya zai kai mata duka a baki, damo sarkin hakuri bai gaji ba ya sake shiga tsakaninsu, bai damu da kalamanta ba, dan yasan yarinya ce, kuma girman kauye ce, fin haka ma zata aikata, kuma shi wlh burgesa take yi sosai, yana san mace mai confidence kamar Aunty MieMiensu, hakan yasa in dai ya shigo bai ganta a wajen momma ba sai ya tambayi ina take, tun da suka sha gyara suka fito a ƴan gayu take burgesa take kuma yi mashi kyau, shiyasa ya zage ya tsaya rabata faɗa da Obaid.
Ran Obaid ne ya kai ƙololuwa wajen ɓaci, dan haka sai ya sakar mata kunama guda biyu. Tana ganinsu ta zunduma ihu tare da daka sufa ta ƙanƙame guyson, kamar ba yanzu ta turesa tana kiransa da ɗan iska dan ya janyeta daga capkar Obaid ba, sai ga shi yanzu da kanta ta rungume shi tana ihu kamar zata tashi gidan da kuka, tana faɗin ya taimaka mata.
A lokacin momma ta tafi wajen King ta je ta rarrashesa ko zai sauko, so bata nan. Part na su Jaish kuma ba kusa da na momma yake ba shiyasa basu ji ihunta ba.
Da gudu Omaid ya iso wajen dan ya ji ihun, a tunaninsa lallasata Obaid yake yi yasa take kuka haka, so gudun kada ya kasheta yasa ya biyo