Showing 114001 words to 117000 words out of 403653 words
alama King ya gada wajen hegen feeling 🥱😅 ba ruwana kar ace na ce, bari in yi ta nan🥱)
Gyara kayan jikinta momma ta yi, ta ɗauki babyn Khadija ta sauko kasan bed ɗin, King ya yi aiki iya aiki sai ya kwanta yana binta da ido har ta zago ta side da yake, dukawa ta ɗan yi, kyakkyawar sumbata ta bashi a kumatu tare da ce mashi good night.
Zata juya ya yi saurin riko hannunta, idanunsa a kan face ɗinta, kamar mai raɗa ya ce. "Zaki dawo?".
Me king yake nufi da zata dawo?...….......🙄 Kash ashe fa surukina ne baban Guyson ɗina, bari dai na yi shiru to kada ace na yi rashin kunya na je ɗakin sirirki da daddare na kallan mashi sirrinsa....🤭🥱😅
Momma da yake itama tana cikin yanayi mai sugar sai ta amsa da zata dawo. Sake hannunta ya yi tare da yi mata alamar ta matso da hannu. Yana yi kamar wanda yake a cikin maye.
Ba musu ta matsa dab da face ɗinsa, sumbata ya bata a kumatu kai ɗumi yana kallan face ɗinta, miƙewa ta yi tana ɗan sakar mashi murmushi ta nufi waje. Sam king bai kalli babyn Khadija da kyau ba.
Kai tsaye ɗakin mama Haulat ta nufa da babyn, yunwan dare ya tashesa. A saman dadduma ta isko mama Haulat tana karatun Alqur'ani mai girma, kwantar mata da babyn ta yi a saman bed, sannan ta ce. "Ki bashi madararsa yana jin yunwa, sannan da safe ki sameni a ɗaki ina da magana dake". Bata jira amsarta ba ta yi saurin ficewa dan ta koma wajen dearlyn love ɗinta su cigaba daga in da suka tsaya, dan basa gajiya da juna, momma tana shan gyara, kayan gyaranta daga Dubai ake kawo mata su, shiyasa King baya raga mata.................🥱
••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••🔥
4:00 na asuba, Jawad ne ya fara farkawa daga nannauyar barci da ya ɗaukesa tin karfe 3 na dare, barcin awa ɗaya ya yi, yanzu haka bai so farkawa ba ya daure ya tashi saboda tafiya da yake gabansu.
Bai waiwayi Chuchu ba ya wuce toilet dan ya yi wanka ya yi shirin zuwa masallaci ya zo ya gabatar da rakatainil fajir.
Sai zuba barchin wahala Chuchu take yi, ta jima bata samu barci irin na yau ba. After some minutes ya fito ya shiga dressing room.
Arabs jallabiya ya sanya a jikinsa launin ash colar, cikin bedroom ɗin ya dawo. A hankali ya haye saman bed dan ya tasheta. Hannunsa dikka biyu yasa ya tallabota a kirjinsa, fuskarta ya zubawa idanu yana matukar jin tausayinta, Allah sarki ta sha kuka da kunci a lokacin da aka ce Rizwan za'a aura mata, bata gama warkewa daga wannan kukan ba ta ɗaura da na ɓatar Auta, har ta yi rama idanunta sun kara girma.
Ya ɗan ɗauki lokaci yana kallanta kafin ya matso da face ɗinsa dab da ita, ya ci burin dik ranar da ya mallaketa ba zai taɓa ɗaga mata kafa ba sai ya ɓareta a ledarta saboda ta jima kyanta yana rikitasa, ya jima yana mafarkinta suna chaskale, sai dai shi kansa a yanzu ba zai so ya yi mata komai ba saboda tashin hankalin da suke a ciki.
Sumbatar ɗan bakinta ya yi hakan yasa ta ɗan motsa, kamar mai raɗa ya furta "Jannawad".
Cikin magaggin barci idanunta a rufe ta ɗan yi miƙa kaɗan tare da amsa mashi da na'am.
"Tashi ki yi wanka ki yi sallah sai mu tafi ko?".
Eyelashes ɗinta ne suka fara kerma alamar tana san buɗe idanunta, sannan ta ɗan tsuke bakinta kaɗan. Sosai ya ji hakan a ransa, sai ya ji mamar ya manna mata kiss.
A hankali ta waro idanunta a kansa, haka kawai ta tsinci kanta da sakar mashi cool murmushi. Sam bai yi expecting hakan daga gareta ba, ya yi zatan da kuka zata tashin masa kamar yadda ta yi barcin, amma sai yaga akasin haka. Wani irin bargon farinciki ya ji ta lulluɓesa har ya sauke nannauyar ajiyar zuciya.
A shagwaɓe ta ce. "Yah Jawad barcin fa bai isheni ba".
Tsintar kansa ya yi da jin tongue ɗinsa ta yi mashi nauyi, kura mata idanu ya yi sosai, tin da aka fara maganar bikin Rizwan sai yau ya ji sanyi ta ratsa ransa.
"Yah Jawad tinanin me kake yi?". Ta sake jefa mashi tambayar tana kai hannunsa saman kyakkyawar sajensa dake kwance luff.
"Tinaninki nike yi my Jannawad". Cikin salon soyayya ya faɗi hakan ........ Kara ƙayata murmushinta ta yi, a hankali ta fara shafa sajensa izuwa saman lallausan kumatunsa.
Wani irin shock ya ji har tafin kafarsa, tsikar jikinsa ne ta fara tashi yana jin wani irin bakon yanayi.
"Yah Jawad Allah ina sanka sosai". A ɗan shagwaɓe ta faɗa. Da kyar ya iya cewa. "Da gaske?". Ya jefa mata tambayar yana kallanta kamar zai cinyeta da ido.
Ɗan turo baki ta yi tare da girgiza mashi kai alamar a'a ba da gaske ba tana wurga mashi kallo mai cike da hararar soyayya, sanna ta zame hannunta daga kan kumatunsa irin ta yi fushin nan.
"Sorry my Jannawad, kada ayi fushi dani, zumar soyayyarki na lasa yasa word ɗina suke kubce mun"............... Bata yi mashi magana ba, ta mayar da kanta saman kirjinsa ta kwnatar, ta rungumesa da kyau tana turo baki.
"Meyafaru kuma rigimammiyata?". Ya yi maganar yana kai hannunsa saman face ɗinta.
"Ni Yah Jawad mun ɓata fa".
"Ba zaki iya ɓatawa dani ba ai". With confidence ya yi maganar. "Meyasa ka ce haka". Ta tambaya tana riko hannunsa dake saman kumatunta.
Matso da face ɗinsa dab da ita ya yi, kamar zai raɗa mata magana a kunne, sai kuma ya canza hanya a in da ya kai ɗan bakinsa saman nata. Cike da so da kauna haɗe da salo ya fara bata hot kiss, abin da ya jima yake tsumayi, in baku manta ba har gizon yana yi mata kiss idanunsa suke yi mashi a baya kafin aurensu.
Yana yawan mafarkin yana kissing na ɗan bakin nan nata, ashe zai yi hakan da izinin Allah. Bata hana shi ba, dan ita ma tana dakon wannan rana, lips ɗinsa suna burgeta sosai, dan haka sai ma ta tayashi, cikin nitsuwa ta fara bashi kiss mai zafi ita ma.
Ba ƙaramin kara rura wutar sha'awarta a ransa ta yi ba, zame hannunsa dake cikin nata ya yi, cikin nitsuwa ya mayar saman kanta, a hankali ya zame hukar kayan barcin dake jikinta, gashin kanta ya fara watsawa yana ƙara matseta a jikinsa.
Ita kuma hannunta ɗaya ta zira a bayansa, ɗayan kuma a saman shoulder ɗinsa, ta kara narkewa a jikinsa tana binsa da salo na musamman, ta datse idanunta irin wai kunyarsa take ji, shi kuma ya kura mata ido yadda abin zai fi kara mashi armashi.
Sun ɗauki a kallah 5 mins haka kafin cikin dabara ta zame bakinta daga nasa, dan ta lura bashi da niyar saketa. A fili ya furta alhamdulillah, dan ya ɗanɗani abin da ya jima yake tsumaya. Ƙoƙarin barin jikinsa ta fara yi ba tare da ta buɗe idanunta ba. Dan rashin kunya wai kunyarsa take ji.
Da sauri ya rikota, kamar zai saka mata kuka ya ce. "My Jannawad ina kuma zaki tafi".
Da sauri ta buɗe idanunta jin yau ya yi magana a shagwaɓe, sai ta ji kamar bashi ba, ya yi mata kamar muryar guyson. Sarkafewa idanunsu ya yi cikin na juna, kamar zata yi kuka a shagwaɓe ta ce. "Yah Jawad wanka zan je in yi in ɗauro alwala fa".
"Kasancewarki a jikina ya fi wankar, lokacin sallama da saura, Please stay with me ko da na 20 mins ne kin ji?".
"Mezaka bani to idan na tsaya?". Ta yi maganar tana ɗaga mashi gera......"Mekike san in baki?"........ Manuniyar yatsarta ta ɗaga ta saita kirjinsa da shi. "Kai nike so".
Haɗe goshinsu waje guda ya yi. "Ni ai mallakinki ne my Jannawad"......
"Yah Jawad kasan me?". Kai ya girgiza mata alamar a'a bai sani ba. Ɗan kawar da kallonta daga saman face ɗinsa ta yi, kamar mai raɗa ta ce. "Your lips is so sweet wlh, kuma fa....." Sai kuma ta yi shiru ta ƙasa ƙarisa maganar.
"Kuma fa me?". Cike da farincikin jin maganarta ya yi tambayar, sai ya ji kamar ya maida ta cikinsa dan daɗi.
Bata yi magana ba, sai ta ɗan miƙe kaɗan, ta kai mashi sumbata a saman lips ɗinsa. Ya fahimci wani kiss ɗin take so kuma tana jin kunyar faɗa mashi, wanda ya yi mata bai isheta ba, dan haka sai bai bari ta zame bakinta daga sumbatar ba ya capki lips ɗinta ya dasa daga in da ya tsaya.
Ajiyar zuciya ta sauke dan ta ji daɗi, ya iya kiss mai mantar da mutum in da yake shiyasa ta nemi kari. A hankali ya kwantar da ita a saman bed ɗin bakinsu manne da juna. Rumfa ya yi mata da kirjinsa, ya sanya hannunsa a wuyarta yana ɗan shafawa izuwa shoulder ɗinta, a matse yake yana san taɓa tula tulanta amma yana shakkar yin hakan.
Ita kuma ta tura hannayenta a cikin gashin kansa, cike da kaunarsa ta fara wasa da gashin, bukata ya biya ta mallaki abin kaunanta.
Dai'dai lokacin da suke zuba wannan soyayya tasu shi kuma uncle Jahiz yana hospital wajensu Khadija, asuban farko ya tafi wajensu. Zee ta farfaɗo sai dai ta ki yin magana a gabansa, mamakinsa ne kuma ya hanata yin magana, saboda shi ne best player ɗinta a ƴan kwallan kafa, bata taɓa tsammanin zata gansa a zahiri ba, sai ma take ganin abin kamar mafarki kamar kuma zafin ciwo yasa yake yi mata gizo tin da shi ne a ranta.
Sai dai kuma fa, ganinsa ya tayar mata da hankali a in da ya dawo mata da mutuwar babanta sabo, ta tina yadda suke kallansa ita da babanta a tv a tare. Yau kwananta uku da farfaɗowa, sai dai a kullum ya zo wajenta kuka kawai take yi idan ta gansa, taki yarda ta bashi dama ya yi magana da ita.
Idan kuma ya bar hospital ɗin sai ta yi shiru har tana tambayar nurses ina ƴar uwarta da ɗanta? Kullun amsa ɗaya suke bata shi ne ɗanta yana cikin family part, ita kuma Khadija tana ƙarƙashin kulawar likitoci har yanzu.
Kullum Zee bata gajiya da tambaya, jikinta yana ta kara warwarewa tana samun lafiya yadda yakamata, dan kwararrun likitoci ne suke kula da ita.
•••••••••••••••• FOREST•••••••••••••••••🔥
Shiru ta tsaya tana kallansa bata motsa ba, yana isa gabanta ya jefar da takobin hannunsa a ƙasa ya ɗagata sama ya matsar da ita daga wajen, yana matsar da ita kifiyar da aka saitata aka harbeta da shi ya wucesu sai cikin ruwan koramar.
Sauketa ƙasa ya yi tare da juyawa ga in da aka yi harbin kifiyar, sai dai kash bai ga ko alamar mutum ba, wanda ya yi harbin ya gudu ya bar waje. Amma wa kuke tinanin ya yi wannan harbin?.
Dawo da kallonsa a kanta ya yi. Har lokacin bata motsa ba, idanunta a kansa babu ko kyaftawa. Ɗan lumshe idanunsa kaɗan ya yi. "Ki yi hakuri ranki ya daɗe". Har yanzu fa bai iya tina face ɗinsa ba'a rufe take ba.
Ganin bata motsa ba yasa ya kai hannunsa saman shoulders ɗinta ya ɗan girgiza a hankali yana ambatar sunanta. Wani irin dogon numfashi ta ja tare da saukewa a hankali. A fili ta furta. "Hoorain ban taɓa ganin kyakkyawa irinka ba, anya baka fi kowa kyau a duniya ba kuwa?".
Ai a miliyan ya kai hannu saman face ɗinsa, jin bai rufe face ɗin nasa ba yasa ya ɗan yi ƙasa da kai yana ɗan ciza laɓɓansa alamar bai so haka ba.
My people's dik yadda zan zayyana maku haɗuwar Hoorain ba zaku fahimta ba, kamar shi ya yi kansa, kyakkyawan gaske.
Ga tsawo da cikar halitta, yana da kafaɗa mai faɗi, ƙirji mai tsari, ya sa ya zama kamar wanda aka zana. Fatar face ɗinsa fara ce kamar madara, hakan tana bayyana yadda yake mai tsafta da kamshi. yana da laushi da kyan gani, kamar ba mayaki ba, sai sheki skin ɗinsa yake yi, alamar yana kula da kansa sosai. Fuskarsa tana da siffar mai ladabi, very innocent haka, da ganin yana yin face ɗin zaka fahimci ba zai yi yawan magana ba, hancinsa mai tsari kuma dogo mai ban sha'awa, leɓɓansa na sama yana da ɗan kauri kaɗan, na ƙasa kuma ɗan laɓalaɓa haka, irin laɓɓan yana da masifar kyau. Idanunsa suna da siffa mai ɗaukar hankali, suna kama da almond, tare da fari mai tsabta da ban sha'awa
Gashin kansa baƙinkirin ko, yana taɓo idanunsa kaɗan ta gaban goshinsa, amma yana da tsawo ta bayansa, yana wani irin sheki yana curlyn kamar na baby's, kamar yadda ake gani a yanayin fashion na zamani.
Yana da kwantaccen saje bakin kirin ɗan madaidaici a gefe da gefen face ɗinsa. Yanayin nutsuwa mai ɗaukar hankali, akwai cikakkiyar kamala a face ɗinsa, amma yana cike da kwarjini da karsashi, tafasasshen jini na zakunan mayaƙa, ga ƙarfin zuciya. Wannan da baya sanya hukar yaki idan yana cikin jama'a, ba ya buƙatar yin ƙoƙari dan ya jawo hankalin mutane a kansa, kwarjininsa na halittarsa zata ja mutane kusa da shi. Hoorain ya haɗu matuka gaya.
Ganin ya yi ƙasa da kansa bai furta komai bane yasa cikin hanzari ta kai hannayenta dikka biyu a saman lallausan kumatunsa, cike da tsantsar kaunarsa ta fara faɗin. "Hoorain ka yi magana mana".
Auta ta so shi bata san kamanninsa bama bare ace yanzu ta gansa a yadda bata zata ba, dan ya wuci kyan da ranta yake ayyana mata, ai wani sabon kaunarsa ne ya kara narkuwa a cikin zuciyarta.
Ba kamaramin sabon bakon alamari ya ji ba a lokacin da ya ji saukar hannayenta a saman kumatunsa, ƙasa iya ɗago kansa ya yi bare ya kalleta, ya rasa ma a wani matsayi zai ajiye kansa.
"Hoorain dan Allah ka yi mun magana ka ji? Ka yi magana ko zuciyata zata yi sanyi". Kamar zata yi kuka ta yi maganar.
Shiru babu alamar zai ɗago kansa ma bare ya yi mata magana. Matsawa dab da shi ta yi. "Ka ji babu daɗi ne dan na kalli face ɗinka?".
Nan ma bai amsata ba.
"Ka yi hakuri ban zata dan na kalli face ɗinka zaka ɓata rai har kaki yi mun magana ba". Ta kai karshen maganar tare da zare hannayenta daga kumatun nasa, ranta ya ɗan sosu, da sauri ta juya zata bar wajen saboda wani irin kuka da ya zo mata mai wuyar dakatarwa, tana san shi amma yana walaƙantata har haka, ta yi magana yaki amsa mata, idan da yasan yadda wannan abin yake ƙona mata rai da ko kusa ko alama ba zai yi mata ba.
Tana juyawa sai ji ta yi ya capki hannunta, cak ta tsaya tare da ƙoƙarin jiyowa garesa, da karfi ya fisgo ta faɗa saman warriors chest ɗinsa, saboda wani irin wutar santa dake azalzalar zuciyarsa, yau ya kai makurar da ba zai iya dannewa ba, zuciyarsa ta yi cikar da in bai bari ta yi amai ta amayar da abin dake cikinta ba zata iya fashewa, yau dai babu wani dama da zuciyarsa zata iya sake bashi, ji yake tamkar ya mayar da ita cikin ransa ko zai huta da abin da yake ji a ransa.
Bata ankara ba ta jita saman faffaɗar kirjinsa, da sauri ta waro idanunta waje, abin da bata taɓa zata ba. Tana ƙoƙarin tantance gaskiya ce ko karya ta tsinkayo sayayyar voice a cikin kunnenta yana faɗin.
"I'm so so sorry ranki ya daɗe, tuba nike yi, ba zan iya cigaba da danne abin da yake cikin zuciyata ba, ba zan iya shanyewa ba, dan haka ina mai baki hakuri da kalaman da zasu fito daga cikin bakina, ban san a yadda zaki ɗaukesu ba, na san matsayina da naki ba ɗaya bane, amma dik da haka ba zan iya ƙasa faɗa ba, ki yi hakuri, ki yi hakuri, ki yi hakuri".
"Ina.............. Wayyo ya Auta zata ji idan ya bayyana mata sirrin dake ransa? Abin da ta jima tana tsumayi! Ya waɗan nan masoya zasu tsinci kansu a yau? To su dai suka sani, sai Monday, bari in je in kora maltinata mai sanyi in huce, nima zuciyata ta kwanta ta nitsu............🥱
P_R_I_N_C_E_S_S__T_E_E_M_A...✍️🔥🕊️
For more information 08161390581 Whatsapp me only!!.
🤍KADA KU MANTA WANNAN DADDAƊAR LABARIN DAGA ALKALAMIN FATEEMA ZAHRA MUSA A-K-A PRINCESS TEEMA TAKU TA AMANA YAKE🔥💘
ALLAH KA KARA MANA SON MANZON ALLAH 🔥🤍
=========🔥🔥🔥===========
MALLAKIN🔥
P_R_I_N_C_E_S_S__T_E_E_M_A...✍️🔥🕊️
اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ❤️
18
Ina sanki, ina sanki soyayya maras misaltawa, soyayya mara iyaka, ina kaunarki, ina jinki a jinin jikina, a kowace second zuciyata tana bugawa da sunanki, kece kawai nike kallah in ji ni a wata duniya ta daban, kina so na ko baki sona wannan dik bai dameni ba, abin da nasani kawai shi ne ina sanki, kuma zan iya mutuwa a kanki, sannan zan cigaba da sanki har bugun numfashina na karshe!!". In out of control ya rinƙa zuba kalaman!.
Tin da ya fara magana zafafan hawayen murna suka fara wanke mata fuska, fabaɗaya ji take yi kamar bata duniya, har wani iri take ji a cikin zuciyarta tamkar an ɗaura mata ice block ciki. Sambatun zafafan kalaman kaunarta ya cigaba da zuba mata babu kakkautawa, yau ya samu damar amayar da abin da ya kwashi shekaru yana cinsa a zuciya.
Jin ɗumin hawayenta suna zuba a kyawawan fararen kafafunsa ne yasa ya dakata da zuba mata kalaman kauna, a hanzarce ya ɗan rabata da jikinsa dan ya tabbatar da kuka take yi ko akasin hakan.
Ganin da gaske hawaye