Showing 261001 words to 264000 words out of 403653 words
shiryu kuwa?. Auta zata mallaki Hoorain kuwa a yadda King ya datse dik wata alaƙarsun nan?. Muje dai zuwa, zamu ga shin Smart ne zai yi nasara ko King!.
🔥🔥KINGDOM OF POWER🔥🔥
P_R_I_N_C_E_S_S__T_E_E_M_A...✍️🔥🕊️
For more information 08161390581 Whatsapp me only!!.
🤍KADA KU MANTA WANNAN DADDAƊAR LABARIN DAGA ALKALAMIN FATEEMA ZAHRA MUSA A-K-A PRINCESS TEEMA TAKU TA AMANA YAKE🔥💘
ALLAH KA KARA MANA SON MANZON ALLAH 🔥🤍
========🔥🔥🔥=========
MALLAKIN🔥
P_R_I_N_C_E_S_S__T_E_E_M_A...✍️🔥🕊️
اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ❤️
44
🔥🔥KINGDOM OF POWER🔥🔥
Tafiya take yi tana waige waige ta fito daga part ɗin mama ta nufi part ɗin momma domin ta duba Zee, har yanzu uncle Jahiz bai dawo mata da babynta ba, yana can ɓangaren Aunty MieMie suna hira, Aunty MieMie ta rike baby gam, ta ce sai dai uwarsa ta biyo shi part ɗinta, ma'ana sai dai Khadijah ta dawo part ɗinta da zama, dan ita ta samu yaro, dama bata da shi, uncle Jahiz ya ɗauka wasa take yi, aikuwa ta nuna mashi da gaske take yi, dan fa ta dage Allah ba zata bada babyn nan ba, uwarsa kawai ta dawo part ɗin da zama dan yaron ya shiga ranta.
Sai waige waige take yi dan bata gama sanin hanya ba, hanyoyin akwai sarƙakiya, idan ba ka san cikin family part sosai ba zaka iya ɓacewa, shiyasa take ta waige waige, taga hanyar shiga part ɗin King and Akkas part, sai ta ruɗe ta rasa ina zata bi.
Unexpect suka ci karo da mutum, ya fito daga bedroom ɗin King, King ne ya kirasa a yazo a kan batun Spender, so shi ne dalilin zuwansa. Karo suka yi ta ɗan yi baya tana goge goshinta da ta buge da kirjinsa, da yake ita ta fi Zee ladabi da kuma hankali sai ta durkusa kasa tare da ɗaga mashi gaisuwa.
Ido uncle Abbas ya zuba mata yana mamakin ganinta, dan shi bai san ta a kingdom ɗin ba. Jin bai amsa mata bane yasa ta ce. "Kayi hakuri ban ganka bane shiyasa"...... Jin kalamanta yasa ya yi saurin ce mata. "Babu komai tashi ki je abinki".
Miƙewa ta yi tana yi mashi godiya tare da satar kallansa ta ƙasa ido, gaba ta yi ba tare da tasan ina ta dosa ba, dan bata gane hanyar part ɗin momma ba. Da kallo uncle Abbas ya bita baya san kawar da kallansa daga kanta. Har ta ɗan yi nisa ta tsinkayo muryarsa yana faɗin. "Zo ina da tambaya"........ Juyowa ta yi ta dawo gabansa, tana ƙoƙarin tsugunnawa ya yi saurin cewa. "A'a ba sai kin durkusa ba, magana zamu yi a tsayen ma is okey".
Ƙasa ta yi da kanta tana amsa mashi da okey cikin harshen turanci. "Zan iya sanin wacece ke?". Ya jefa mata tambayar yana ɗan sunkuyo da kansa ya kalli face ɗinta. Lokaci guda ta ji gabanta ya faɗi, sai ta ji wani irin fargaba mai razanarwa, tsoronta ɗaya kada yasa a hukuntata dan bata da wata alaƙa da masarautar, kada ya ce waye ya kawosu? To waye zata ce mashi tun da ita ko sunan uncle Jahiz bata sani ba bare ta faɗa mashi sunan wanda ya kawosu.
Ganin ta yi shiru ta rasa abin faɗe yasa ya ce. "Zaki iya tafiya". Dan ya lura tambayarsa ya saka ta a cikin damuwa, lokaci guda hakan ya bayyana a face ɗinta. Ai yana cewa ta tafi ta yi gaggawar juyawa har kamar zata yi tuntuɓe, da kallo ya bita yana jin kamar wani abin a ransa, mamakinsa ɗaya shi ne a ina aka samo waɗan nan black beautys ɗin?.... Ni kam na ce to dama mu Nigerians ai shegen shiga rai ne da mu ato, dik in da muka je sai mun ratsa zuciyar mutane, bare ma mu arewacin Najeriya ai daban muke.
Har sai da ta kurewa ganinsa sannan ya ja dogon numfashi tare da wucewa ya nufi elvator domin ya yi ƙasa ya koma part ɗinsa, mammie na can tana jiransa ya dawo ta zazzage mashi jajjagen masifar da ta jajjaga ta ajiye mashi. Shi kuwa yana nan zuciyarsa ta shiga wani yanayi. Babbar magana, muje zuwa my people's, ba'a fara komai ba, RAWANIN ZALINCI zai baku mamaki gaba kaɗan, fatana dai Allah ya ara mana lokaci!!.
Sai da Khadijah ta shiga almost part uku a cikin amma bata iya gane part ɗin momma ba, daga karshe ta lallaɓa ta koma part na mama ta yi kwanciyarta zuciyarta cike da tunanin ina Zee? Bata damu da tunanin ina babynta kamar yadda ta damu da tunanin ina Zee ba?. Dan ta san halin yar uwar tata da shegen zuciya bata ɗaukar raini.
A ɓangaren guda kuwa, mammie dai ta yi jigilar aikin gasawa Sarina jiki, Sarina anji jiki, dan ma Allah ya taimaketa a ba kan tsini ta isko Smart ba, ai da bata rage ba, amma dik da haka ta jibgu ba karya, jiki dik ya yi ruɗu ruɗu ya kumbura, ta sha ruwan zafi kam ba karya.
Idan muka waiwaya gefe guda kuma, a can hospital ɗin Kingdom ɗin, a lokacin da King ya saki Hoorain, kwance yake a saman bed na hospital ɗin, sai da ya yi good two days kafin ya dawo cikin hankalinsa, amma fa har lokacin baya iya tafiya, tin da yake a rayuwarsa ba'a taɓa yi mashi irin wannan horo mai bala'in tsananin ba, wannan ɗakin duhu wlh karshen azaba ne, amma kuma da yake ba bawa yake sanyawa kansa so ba, dik wannan wahala da suka bashi wlh soyayyar Auta ninkuwa ya yi a ransa, sai ya ji ma tamkar buɗe kirjinsa suka yi suka zuba mashi santa na wannan azaba da suka yi mashi.
A ranar da ya farfaɗo ma da sunanta ya farfaɗo a bakinsa, sai dai yana buɗe idanunsa da Abbonsa ya fara yin tozali, ya ji matuƙar daɗin ganin mahaifin nasa, sai dai kuma da buɗar bakinsa ya ce. "Abbo Hoonaira bata sake zuwa wajena ba ne?". (Yana tinanin tin da ta je wajensa a ɗakin duhu kenan bata sake zuwa ba, dan tun wannan rana da ta je wajen nasa King ya zo ya ɗauketa, zafin ɗaukarta da aka yi yasa zuciyarsa ta tsananta ciwo, dalilin suman da ya yi kenan sai yau ya farfaɗo.)
Ɗan girgiza kai Abbo ya yi irin alamar tausayawa ɗan nasa, shi ma ya rame sosai, dama ga tsufa, ga ciwo, ya sha wahala dattijon arziki, zuciyarsa ta rauta a kan Hoorain da Auta sosai, sai yake jin kamar ba zai iya sanya karfi wajen rabasu ba, ga shi kuma ya yi wa King alkawarin zai rabasu, dama a tinaninsa karfi zai sakawa Hoorain ɗin, zai ce mashi ya zaɓa ko shi ko Auta, kowa dai yasan dole Abbonsa zai zaɓa ko da hakan zai yi sanadiyar rayuwarsa tun da iyaye dai ba'a haɗasu da komai, to commander ya ji jikinsa ya mutu a kan wannan mataki da yake san ɗauka.
"Abbo dan Allah ka amsa mun, Hoonaira bata zo bane?". Ya faɗa cikin raunatacciyar murya. Jinjina mashi kai commander ya yi alamar e bata zo ba, ya kasa iya furta word, dan ba shi da abin faɗe. Tafukan hannunsa Hoorain ya buɗe tare da matsar da hannunsa kusa da hannun Abbon nasa, da yake commander yana zaune a saman chair na masu jinyar majinyata. Hannun Abbon nasa ya riko cikin nasa. Cikin wata iriyar wahalalliyar murya irin na wanda ya sha azaba, da kyar da kyar ya fara magana cike da dakiya da jarumta, wlh ba dan assistant commander ne shi ba, ya saba da wahala saboda irin horan da ya karɓa, Allah da ba zai iya ɗaukar wannan horo ba, ba'a taɓa sanya mutum a ɗakin duhu ya wuce kwana uku ya fito a raye ba, kwana ɗaya idan mutum ya yi aka fitar da shi sai ya sha jinya na satittika, kuma kafafunsa basa iya takawa, amma shi almost week, ya fito kuma bai yi wani dogon jinya ba ya farfaɗo, ba shakka yana da jarumta sosai, commander ya iya renon ɗan nasa, ya mayar da shi zaki ɗaya tamkar da dubu.
"Abbo ina san Zunaira, ina santa fiye da yadda nike san rayuwata, a da kafin in bayyana mata soyayyata a gareta ina jin kamar zan iya dannewa in mutu da santa, amma tin daga ranar da na bayyana mata na gane cewa tabbas ba zan iya hakuri na danne sonta har in koma ga Allah ba, please Abbo ka taimaka mun, dik wani hukunci da zaku yi mun ku yi mun na yarda, amma dan Allah kada ku rabani da Zunaira, ba zan iya jurar wannan zafin ba, gara mun zafin wuta a kan wannan zafi, ban taɓa neman wani abin a wajenka na rasaba, shiyasa a kullum nike kara yin alfahari da kai, a yanzu ma ga buƙatata na kawo maka dik da nasan kai ma baka da iko a kan hakan". Ya kai karshen maganar wasu zafafan hawaye da suka cika mashi idanu ne suka zubo ta gefe da gefen kunnensa saboda yana kwance ne. Idanunsa jajir kamar wuta, kirjinsa na suya matiƙa, yana jin zafi tamkar an ɗaura shi a saman wuta, ya rasa a ina zai sanya ransa ya ji daɗi.
Wani irin zabura commander ya yi, dan tin da yake da Hoorain bai taɓa ganin hawayensa (tin da ya yi wayo kenan ba tin yana jariri ba) lallai girman san da Hoorain yake yi wa Zunaira ya wuci misali, yau saboda santa ya yi kwallah? Innalilahi wa inna ilahir rajiun, yanzu da wani idanu commander zai kallesa da kudurinsa na rabasu?. Take commander ya ji ko mutuwa zai yi sai dai ya mutu amma ba zai iya cewa Hoorain ya rabu da Zunaira ba, ba shi da wannan kwarin gwiwa, Hasbunallahu wani'imal wakil, shi ne kalaman da commander yake ta mainaitawa a ransa.
A dai'dai wannan gaɓa guyson ya kawo mashi waya domin su yi waya da Auta, ai saboda farinciki Hoorain bai san lokacin da ya miƙe zaune tare da tsige drip dake manne a hannunsa ba, murna a wajensa ba'a magana. Yana magana da ita zafafan hawaye suna bin ƙuncinsa, wlh sai da guyson ya taya shi zubar da hawaye, ya tausaya masu matuƙa, sai yake jin tamkar ya ɗaura masu aure kawai, sai dai bashi da damar yin hakan, sai kawai ya hau tayasu da addu'a, ga azumi ya kawo kai, sai ya yanke shawara a cikin zuciyarsa a kan zai sanar da King zai tafi saudiya ya sauke farali, idan ya je ya yi alkawarin tun ranar da ya dira har ya dawo sunansu ne zai kasance a bakinsa, addu'a ba dare ba rana zai yi masu, wannan hali da suke ciki dole a yi saudiya da sunansu, in ba haka ba akwai matsala, shi yasan idan ba Allah ba babu wanda ya isa ya canza rantsuwar King a kansu!!.
Bayan sun gama magana da ita ko in ce wancan baturiya ta kwace wayar ne ya bawa guyson wayarsa tare da dawo da kallansa a kan Abbonsa. "Abbo ina wayata?". Ya faɗa yana goge hawayensa. Allah Akbar, my people's soyayya idan ba'ayi dace ba wlh musifa ce, yau assistant commander of dangerous warriors ne yake hawaye a kan mace? Macen ma under 15 ba wata macen azo a gani ba, innalilahi akwai matsala fa.
Kasa jurar ganin halin da yake ciki guyson ya yi, dan ya ga kamar Hoorain fa ya samu matsala, da gudu ya juya ya bar room ɗin, dan yana da raunin zuciya bawan Allah. Shi kansa commander ji yake yi tamkar ya taya ɗan nasa hawaye, dan wani irin tausayinsa ne ya kama shi matuƙa. Hannu kawai ya kai yana taya shi goge hawayen yana faɗin. "Hoorain ya isa kukan nan haka ka ji? In Sha Allah Allah yana tare da kai, idan gimbiya matarka ce babu wanda ya isa ya zama barazana ko shamaki a tsakaninku, ina da yakinin Zunaira matarka ce, ka yi hakuri".
Rungume Abbon nasa ya yi, cikin zafin zuciya da raɗaɗi ya ce. "Abbo dole waɗan nan hawaye ba zasu dakata daga zuba daga idanuna ba har sai na dakatar da na Hoonairata, saboda a cikin zuciyata na ji kuka take yi a yanzu, dan Allah ka bani wayata domin in kirata in dakatar da nata hawaye zaka ga nawa ma sun dakata". Out of control yake maganar. A dai'dai lokacin da ya yi wannan magana tabbas kuka Auta take yi, dan a lokacin tana bawa Smart labarin abin da yake a tsakaninsa da my heronta. Soyayyar gaskiya daban take, ya so ta tin tana jaririya ai dole ya iya fahimtar halin da take ciki.
Abbo ya fahimci Hoorain fa baya cikin hayyacinsa dan haka sai ya ce. "Ka yi shiru wayarka tana hannunsu Ansar, yanzu zan sa a karɓo maka, ya isa haka ka ji?..........".
Commander bai gama tufe baki ba sai ga sallamar Ansar and Anwar aminan kwarai sun shigo, da ka gansu zaka fahimci suna cikin damuwa da tashin hankali, ba jimawa suka bar hospital ɗin, wanka suka je yi, dama suna a tare da shi suna taya commander jinya bayin Allan, su suka yi jinyar commander ɗin ma har ya warke, yanzu kuma suna taya shi yin na Hoorain.
Hoorain yana ganinsu ya zabura yana faɗin su bashi wayarsa. Ansar ne ya ciro wayar daga aljihunsa tare da na Auta da yake wajensa ya miƙa mashi yana faɗin. "Our lion lafiya kuwa?".
Ai ina bai amsa masu ba, kunna wayarsa ya yi, jikinsa har yana ɓari ya shiga contacts, sai kuma me? Ya rasa wani number zai kira, dan bashi da numberta na Paris, wayarta ma ai gata a hannunsa. Da karfi ya ɗaga wayar tasa ya yi wurgi da ita dan takaici, sai dai Ansar ya yi gaggawar capke wayar bata isa kasa ba, da tarwatsewa zata yi, ransa ne ya kara jagulewa, zuciyarsa tana tafasa ya juya ya kifa kansa da jikin bango yana wani irin huci mai fita da karfi karfi.
Gabaɗaya sai da suka yi matuƙar tausaya mashi, take jikinsa ya kara tsananta zafi sosai, zazzaɓi ne ta rufesa sosai. Miƙewa tsaye daga kan chair commander ya yi tare da tallabo ɗan nasa da kyau domin ya taushesa, ya san shi da ɗan banzar zuciya, tsoronsa kada ya je ya haɗiyi zuciya dan ɓacin rai ya mutu su shiga uku, idan Hoorain ya mutu ina zai sanya ransa?. A gaggauce su Ansar suka matsa kusa da shi dan su taushi zuciyar zaki kada ta buga. Sai huci yake yi bai iya cewa komai, ya dai datse idanunsa gam alamar baya san ganin kowa. A dai'dai wannan lokacin kuma Smart yake rarrashin Auta yana yi mata alkawarin zata mallaki Hoorain while shi ma commander alkawari ya shiga yi wa Hoorain a wannan lokaci a kan in dai yana raye to da izunin Allah zai mallaki Zunaira, ya yi hakuri ya daure har ya samu lafiya. Sai dai ina, Hoorain bai iya amsawa ba, bayan wannan huci babu wani abin da zaku ji yana fita daga garesa.
A ɓangare guda kuwa, Chuchu dai ta lallaɓa ta gudu ta koma part ɗin Akka da zama, tun safe take can, har dare taki komawa part ɗinta, da yake yau Jawad ya je office to bai dawo da wuri ba, saboda aikin King na gina wasu makarantu dan marasa galihu, so wannan aiki ta tsayar da shi, sai ana kiran mangariba ya shigo gida. A gaggauce ya yi wanka ya wuce musque. Bai dawo ba sai da ya yi sallar isha'i a wajen, sannan ya dawo gida.
Part na King ya fara zuwa, sai da suka gaisa suka ɗan yi hira kaɗan kafin ya wuce wajen momma domin su gaisa, dan tun safe basu haɗu ba. Ita ma suka ɗan taɓa hira na kamar ten minutes, sannan ya yi mata sallama ya fito, yasan yana da mara lafiya, hankalinsa dik yana a kanta, dan ma dai ba laifi ta samu sauki saboda wadataccen kulawa da ta samu daga wajensa.
Bedroom ɗinsa ya nufo yana tinanin yadda zai yi da ita yau, dan gaskiya batu na Allah a matse yake, yana hannu, ita kuwa tsoronsa take ji, jiya ya yi ya yi da ita ta bashi haɗin kai, amma ta murje idanu ta ce bata san wannan zance ba, ko taɓata taki yarda ya yi, da ya taɓata zata saka mashi kuka, ya rasa me zai yi mata, ga shi su kuma jarabarsu fa ba irin wadda za'a iya dannewa ta dannu bane, shiyasa kuka ga suke yawan san shan cappuccino, dan yana ɗan sassauta masu, kun gano su ko?.
Ya yi mamakin ganin bata a cikin bedroom ɗin, ya kuma san bata part na momma, dan da tana can momma zata ce mashi gata nan su wuce a tare. Toilet ya nufa cike da tinanin ina ta tafi? Wanka ya yi ya fito ya shirya cikin sleeping dress ɗinsa masu kyau. Waje ya fito sai tashin kamshi yake yi, kai tsaye ya nufi part na Akka, dan yasan bata wajen mummynta, bata cika zuwa can ba, in bata wajen momma to tana wajen Akka.
A yayin da yake nemanta shi kuma Jaish yana kwance saman bed ɗinsa barci ta gagaresa, tin ranar da wannan abin ya shiga tsakaninsa da Mahnoor bai kara yarda sun haɗa hanya da momma ba, tsabar rashin kunya da safe idan ya tashi barci kafin ya tafi office sai ya kirata a waya su gaisa, haka da rana da yamma ma, wai shi kunya yake ji, ita kuwa momma ta ɗauke Mahnoor daga part ɗinsa, ta kafa mashi tarkon da sai ya kawo kansa, shiyasa ko ya kirata a waya dan su gaisa yana ɓuyan mata bata wani damuwa, dan ta san halin kayanta, tasan maganinsa.
Mahnoor baiwar Allah sai da ta yi kwana guda a sume, sannan ta