Showing 351001 words to 354000 words out of 397328 words
Anna da gaske ne uncle Sul an masa mata? Rabin jikina idan hakane wallahi sai na kashe shi, me ya sa bai taɓa faɗa min ba tunda muke da sssshiiiiiiii?"
Kawai ta ƙarashe tana faɗawa jikin ta da fashewa da kuka, zaro idanu Nawal ta yi tace" Kika ce ba kya son shi? Me za ki yi da shi?"
Ɗagowa ta y ta dube ta tace" Ni ba kukan son shi nake ba, jin zafina da bai gaya min ba, ai na ɗauka mun zama aminai da shi ko?"
Sai kuma ta yi ƙwafa ta shiga haurawa da gudu tana ƙoƙarin kiran lambar sa, ko da ya ɗaga kiran cikin kuka da tashin hankali tace" Kawun Yusrah, ashe dama ba ka da kirki, ba ka da amana, ba ka da tausayi da alƙawari, wallahi ka bani mamaki, kuma da nasan za ka min haka da ban yarda mun zama ƙawayen ba ma, kuma ka sani daga yau kar ka sake kirana, can ka je ka ji da ƴar ƙauyen matar da aka maka, amma kar ka sake kiran lambar Manal, idan ba haka ba za ka gane Manal ƙanwar canal Aswan ce, dan sai na kashe ka har lahira."
Ƙit ta yanke kiran ta jefa wayar kan gado tana safa da marwa, can kuma sai ta ji abun ya sake tsaya mata kawai ta faɗa kan gadon ita ma ta fashe da kuka. Uncle Sul kuma ai tuni ta cira masa hankali ta kai shi saman bakwai sannan ta yado ga ƙasa, ya kira wayar ta yafi bila adadin ta ƙi ɗagawa, ya kira ta Nawal ma amma sai ta ɗauki abun a wasa kawai ita ma take cewa ai hushi take da shi, take kawai uncle Sul ya sa ma ran shi AA ne ya shiga tsakanin su, dama ai haushi yake ji idan ya ga yana ma Manal ɗin wasu abubuwa, sai ya ce ji yake kamar ya mare shi dan dai yana kawun Y. Turaki ne, kenan shine yanzu ya farraƙa su ta sauƙi ko, to ai ko shima ƴa ya bashi ya aura, wallahi sai dai a yi karɓe karɓe, ya karɓe ƴar shi sai ya ɗauki ƙanwar shi shima, idan ya dawo masa da ita ya maida masa ƴar ta sa har gida da kan shi, ka ji jaraba kai irin ta jikan Anza.
*AA MENSION*
Dare mai ɗumi, safiya mai sanyi da nutsuwa ita Yusrah ke ciki a wannan rana, ƙirjinta na harbawa a duk lokacin da ya motsa ya saka idanuwansa cikin nata, sun yi barci a cikin jikin juna mai daɗi da saka nutsuwa, tunda ta sha maganin samun sauƙin zugi ya rungumeta a jikinsa yana shafa gashin kanta yana yi mata da daɗaɗɗen kalamai sai barci mai nutsuwa ya ɗauketa ya zama hatta mafarkinta nasa ne wanda ta jima bata ji kuzarin ta ya dawo irin na yau ba.
Da ya fita sallar asubahi bayan ya so mayar da su ruwa tsaf ta samu ta miƙe ta ɗauko sabon zanin gado na uku kenan dan ta yarda jikan Anza ya ketata ba kaɗan ba saboda ɗigo-ɗigon jinin da ya dinga zubo mata ta warware shi ta yaye wanda suka kwana sama a nutse ta shiga shinfiɗawa har ta gama ta kwashe suturunsu ta kai wajen da ya dace ta kunna garwashi ta saka turaran wuta ta ajiye a ɗakin sannan ta yi bayi bayan ta ɗauki towel sabo ta shige ta rufe.
Sosai ta kula da jikinta, tana gamawa ta yi wankanta ta zo ta saka suturarta ta yi sallah sannan ta koma saman bed, ta ji shigowarsa ta farko da irin yadda ya hayo gefen gadon ya zauna ya manna mata kiss a leɓenta sannan ya sake gyara mata rufar ya miƙe ya fita, a hankali har barci ya sake fizgeta, sai farkawar nan da ta yi a wannan karon ta same shi zaune saman gadon yana yi mata murmushi ta ji tamkar ta saka ihun daɗi dan farin ciki, inna lillahi, wai dama haka soyayyar take mai sunan soyayya? Inna lillahi, ashe babu wanda ya kai jikan Anza tausayi da iya soyayya....yo wai ita in bata yiwa maza bautar soyayya ba ma ai sai ta shiga uku, yaron a tsaye yake, a gine yake yaron, baban soyayya ne ta yarda dan ta gani da idanuwan ta.
Abincin da ya miƙo mata a saman wani ɗan table fari tas ne ya sakata lumshe idanuwanta zuciyarta na sake harbawa sannan ta masa alamun bari ta sake yin bruch ta dawo, sauka ta yi tana tafe a hankali, jikinta da rigar barci doguwa mai siririn hannu, gashin kanta a kame a tsakiya ya baje sosai hakan ya sa ya rakata da kallo har ta ɓacewa ganinsa, sai ya ɗauke idanuwansa ya yi murmushi yana shafa gemunsa haɗi da ayyana _'Jikan Anza ba fa tuwo bane, kuma ai abun naka ne, ka yi haƙuri ta warware ka ji?'_
Yana zancen zucin ta fito daga bayin ta nufo shi a nutsen nan, hakan ya sa ya saki murmushi ƙasa ƙasa ya ce" Ba ka yi jiran banza ba ɗan Aliyu, yarinyar akwai salihin kyau da diri ma sha Allah."
Yusrah ta bi leɓensa da kallo a hankali ta ce" Na'am?"
Ya gyara zama yana saka musu table ɗin a tsakiya ya ce" Cewa na yi baiwar Allah ƴar Anna abin tausayi, zo in ciyar da ke kin ji?"
Yusrah ta yi murmushi ta zauna da kyau tana kallon abincin ta ce" Wanene ya yi wannan girkin? Na san dai ba kai bane, kuma bai yi kama da na oder ba."
Shi ma yana murmushin ya ce" Kin san yau ne zaki zaɓi chef ɗin da zata ringa maki abinci, to sun zo ne su uku, ɗaya zata yi na kari, ɗaya na rana, ɗaya na dare sai ki ji wacce nata ya fi kwanta maki a rai, amma fa kowace ta iya sosai."
Ido Yusrah ta zaro tana kallonsa ta ce" Ban gane ba, wai masu girki?"
Ya gyaɗa kansa shi ma yana kallon nata ya ce" Eh, masu girki, su masu gyaran gidan Anna ta ce sai nan da sati wai."
Da mamaki Yusrah ta kame bakinta tana kallonsa ta ce" To ni me zan yi kenan Aban Safwan? Ai sai in yi ƙiba jikina ya ringa min ciwo."
Jikin nata ya bi da kallo kafin ya yi murmushi ya ce" Ke kike da aikin yi kuwa, zaki kwanta ki huta, idan kin tashi ki kula da lafiyar jikin ki da fatarki, ki ɗauki time ɗin kallo kafin in zo, idan na zo zaki kasance a jikina har wata safiyar, sports kuwa sallah ma ai sports ne."
Haɓa ta dafe kafin ta ɗauki sallalami tana tafa hannaye ya amshe sallalamin yana kallonta ya ce" Lafiya?"
Bayan ta saki bakin da ta riƙe ta ce" To ai abun ne abun mamaki wai ƙato a aljanna, yanzu fisabililah Aban Safwan ina zaune ƙalau haka a rayuwa ai har na lalace, to aikina fa?"
Goshi ya dafe yana kallonta ya ce" Ke kin ga, Y.Turaki kar ki raina min wayo, ke da na faɗa miki babu abinda zaki yi, hutawa zaki yi saboda in na zo mu sha sukuwarmu lafiya lau ba tare da kin gaji ba, kuma aiki ai sai kin yi wata guda na amarcin kafin in duba in gani, ni aikin ma ban san na me ye ba, amma zan duba dai in gani, ha buɗe bakinki ki ci."
Murmushi ta yi ta buɗe bakin ya saka mata dankalin turawa a bakin nata ta tauna a nutse ta haɗiye ta dube shi a hankali ta ce" Aban Safwan ba na ƙi ba fa, gani na yi abincinka ba zan iya bari wata ƙatuwar ta dafa min ba sai a halin rashin lafiya, shine kawai dama ka ga sai ta dafa musu nasu ko?"
Ya wani ƙanƙance idanuwansa yana kallonta sai kuma ya yi dariya yana faɗin" Kai jama'a, na yarda ɗari bisa ɗari, inna lillahi zata ma ƙato wayo."
Dariyar ta kamata ita ma , suka maida hankali suna ciyar da juna abincin, sun yi nisa da cin abincin wayarsa dake ajiye saman bed ɗin ƙirar samsung wacce ake ninkewar nan ke ta tsuwa tana neman agaji.
Da farko sharewa ya yi, har ta tsinke, da aka sake kira ne ta ɗauko dan ta miƙa masa idanuwanta suka ga lambar Nabihat,
ƙwarai ta gane lambar ne saboda Nabihat na yawan kiran aunty Intisar har ta gane ƙarshen lambar da farkon ta, miƙa masa ta yi, shi ma yana dubawa ya ɗan yi tsam kafin ya ɗaga ya kara a kunnensa ya amsa haɗi da ɗan saurarawa.
Me ta ce? Me ta ce shi ya ji, har ta gama maganarta yana sauraro ya buɗi baki zai fara magana Yusrah ta miƙe a nutse ta ɗauki hijabinta na sallah ta zumbula ta nufi hanyar falo saboda ta bashi waje ya yi wayar, domin ba zata so jin komai a cikin wayar nan tasa ba, abinda ya fi ɗaga mata hankali irin abinda take ji a zuciyarta, anya kuwa wannan halaya zata haifa mata ɗa mai ido? Hasbunallah wani'imal wakil.
Ta ɗora hannu zata buɗe ƙofar ta ji hannunsa saman nata, a hankali ya juyo ta inda yake tsaye ya zamo ta juyo tana kallon fuskarsa, bai sauke wayar daga kunnensa ba, bai kuma kashe kiran ba a hankali ya ɗago haɓar Yusrah idanuwansa cikin nata ya haɗe bakinsa da nata ya shiga kissing.
Bata san dalili ba, duk irin azabar da ta ci jiya mantawa ta yi dan shagalta ko kuwa zuciyarta ce ke raya mata gwara ta sha wahalarsa da irin zafin da ƙirjinta ke yi mata saboda tunanin watanta? Ita dai a hankali ta samu kanta da saka hannunta wajen wuyansa ta amshi leɓensa a hankali ta shiga kissing idanuwanta na fitar da hawayen da bata san ko na menene, anya kuwa bata fi shi afkawa a kogin abinda ya furta yana ji a kanta ba kuwa? Gani take yi abin yana neman taɓa nutsuwarta da dukkan farin cikinta.
Shi da kansa bai san ya ya ya rabu da wayar ba, ya dai san abinda ya mayar aiki a gabansa shine ya ga ta daina hawayen nan har suka ƙarasa suka zube saman doguwar kujerar karatu ta ɗakin barcin ta haye saman ƙirjinsa ya rungumeta sosai a jikinsa a hankali tana sauke ajiyar zuciya har barci ya nemi kwasheta, shi kuwa zuciyarsa cike da tunani da wasi wasi a kan maganar auren nan, abu ɗaya ya sani in dai ta kasa kwantar da hankalinta da maganar nan sai dai a yafe masa ba zai yi mata abinda bata so ba, ba zai kaita inda zata ringa kuka ba dan wallahi baya tunanin in har zai jure hakan a rayuwa.
*_SAJEERAH_*🖊️
*Alhamdulillah.*
03/07/2024, 20:39 - samiraharounayacouba: 👩❤️👨🧕👩❤️👨🧕👩❤️👨🧕👩❤️👨🧕👩❤️👨🧕
*WATA TAFIYA*
👩❤️👨🧕👩❤️👨🧕👩❤️👨🧕👩❤️👨🧕👩❤️👨🧕
_RUBUTAWA, TSARAWA_
*SAJIDA NIJAR*
_TARE DA_
*SAMIRA HAROUNA*
_VIVE LE NIGER_ 🇳🇪
*LITTAFIN KUƊI*
_Assalama alaikum masoya 'yan mutan niger, ga wata sabuwa da yardar Allah, *WATA TAFIYA*, hak'ik'a nasan kun san daga jin *WATA TAFIYA* tare da gwarazanmu a cikin wata sabuwar *TAFIYA* kun san abun zai ƙayatar, ba sai mun cika ku da surutu ba, kun san hannayen mutanen naku na Nijar, dan haka ku garzayo a yi da ku._
_*Farashin mai sauk'i ne* naira d'ari biyar (500) kacal, yan niger kuma dala d'ari ne (500fcfa) zaka samu wannan littafi mai *WATA TAFIYA* ta daban da zata birge ku._
_Domin tura na ka tura ta wannan account *2097292243 Lubabatu Shehu U.B.A Bank*. IDAN KA YI TRANSFERT SAI KA TURA SHAIDA TA WANNAN NUMBER 93 81 16 18._
_'Yan niger kuma sai ku tura katin MOOV ko Airtel ta wannan lambar *94-98-56-52*._
_Bismillahir rahamanir-rahim_
*89*
Suna kwancen nan saman kujera barci na ridar ta shi kuma yana kallon sama da tunanin alaƙar shi da Nabihat ta yiwu ko ba za ta yiwu ba wayar ta sake ruri, sai da ya ji kukan wayar na fitowa daga inda yake kwance ne ya tabbatar kenan wayar ta riga su sauka saman kujerar, a hankali ya ɗan cicciɓa yana lalubowa da niyyar zai mata ba daɗi, idan ma saka ta ake yi to bai san rainin hankali, ya za ta kira shi a wannan lokacin ma bayan ta san yanzu ba gauro bane?
Yana jawo wayar ya duba screen ya ga sunan uncle Sulaiman ne, ɗan tsam ya yi dan ya tabbatar babban abu zai sa ya kira shi warhaka, da ma Arif ne zai iya kiran sa ko ba dalili dan ya hauda shi sama, ɗagawa ya yi yana ci gaba da shafa Yusrah a sanyaye saboda jin da gaske bacci ya ɗauketa dan har wani numfashi take fitarwa irin tasha kukan nan hahhhhhakk! Yana ɗagawa yace _"Kawun Y. Turaki, ya da kira da safe haka? Kai ko kunyar ƴar ka ma baka ji?"_
Uncle Sulaiman da yadda ya ga safe haka ya ga dare duk a susuce yace _" Oga, tambayar ka zan yi, kuma dan Allah ka faɗa min gaskiya tsakanin ka da Allah."_
_" Tofa, jikan Anza sarkin laifi, me kuma na yi yau?"_ Cewar Aswan yana taɓe baki, uncle Sul yace _" Jiya me ka faɗawa Manal a kaina? Me ka ce mata dan Allah oga?"_
Da mamaki ya fara yin jim, sai kuma ya basar yace _" Manal kuma? Me ta ce maka na faɗa maka?"_
_" Ni dai dan Allah ka faɗa min?"_ Ya faɗa cike da ƙaguwa, a tausashe AA da baya son tashin Yusrah a bacci yace _" Wai na faɗa maka me? Me ta ce na ce maka? Ban fa son rainin wayo irin na jama'a wallahi, kashe wayar na kirata dan kutumar buru'..."_
Da wani irin rauni uncle Sul ya tare shi da faɗin _" A'a, a'a oga, dan Allah kar ka kirata ka sake ɗaga mata hankali, hakan zai sa ta sake jin haushina, jiya ta kirani a waya ran ta ɓace, ba fa irik sunan da bata kirani da shi ba, ta kirani marar kirki, marar amana, marar tausayi da alƙawari, Aswan har alƙawarin kasheni ta yi fa idan na sake kiran ta a waya, ya zan yi dan Allah yanzu ta saurareni? Me na mata? Me ya sa ba zata tsaya mu tattauna ba? Zan ƙara kiran ta yanzu, idan bata ɗaga ba zan shigo garin yau na same ta, ina so nasan dalilin kukan nan nata a waya da kuma abinda ya faru."_
Da fari yana maganar Aswan yana murmushi ne yana ciccila idanuwa irin abun nan ko a jikin ka, amma da ya ji kamar muryar uncle Sul ɗin na rawa irin kuka zai yi ko ma take yi, da kuma raunin sa sosai akan maganar Manal ɗin da yadda daga ƙarshe ya nuna zai ji dalilin kukan ta, hakazalika zai baro karatun da ya fi masa komai mahimmanci a yanzu ya zo dan kawai ganawa da ita, sai ya ji ai wannan kamar larurar gidan sa yake son bayyana masa a kaikaice, sannan abinda ya koro shi daga tsaye kamar ma a zaune ya samu uncle Sul din ko? Wannan shakka babu ciwo ɗaya ke damun su, sai dai bai sani ba suma ko sun bayyana ma junan su, ko kuma raɓe-raɓen za su ci gaba da yi ne har sai wani abun ya shi o tsakiya da zai ɗaga hankulan su suma kamar dai su.
Da matuƙar tausayawa da fahimtar shi sosai yace _" *Kawunmu*, na fahimci ciwon ka, Manal dai ƙanwata ce ko? Kuma ni nasan ba abinda ka mata buru'uba ce irin ta ƴaƴan Anna ta motsa, ka zama namiji sosai akan Manal, idan ba haka ta dinga saka ka a uku kenan."_
Uncle Sul ya tambaye shi da _" Kenan shawara ka ke bani na zamar mata dodo? Ni fa so nake na ji ko kaine ka haɗani da ita, dan dama ba tarayyar mu kake so ba."_
Murmushi Aswan ya yi mai sauti yace _" Me ye tsakanin ka da ita? Soyayya kuke?"_
Da sauri kamar marar gaskiya yace _" A'a, a'a wallahi, kawai dai mun shaƙu ne da ita, kuma kaga yadda muke aminai bai kamata muna samun saɓani ba ai."_
Jinjina kai Aswan ya yi yace _" Aboki, ga ƴar ka kwance a ƙirjina tana bacci, ta canza min rayuwata fiye da tunanin ka, ta ya zan kasa saka maka wannan halaccin? Ba dai Manal ba? Son ta ka ke yi, kuma in dai nine Yayan ta sannan ɗan Aliyu na farko, to daga yanzu ka rubuta ka ajiye na baka Manal halak malak, kai ko bayan raina nasan ɗan Anza zai cika wannan burin nawa, daga ƙarshe... Allah ya muku albarka kai da *Y.A. Turaki*, fatan alkairi."_
Uncle Sul borin kunya ya so yi da irin tambayoyin nan na ban gane ba? Me ka ke nufi? A yi haka? Amma da Aswan ya yanke kiran sai ya daka wani ihu a ɗakin sa na makaranta tare da juyi yana cabke wayar shi da ya cilla sama, sai kuma ya dakata yana saka lambar Manal zai kira yana faɗin "Zan sake kira ɗin ƙanwar AA fitananniya, kin daɗe baki kasheni ba ƙanwar masifaffe, kuma wallahi yanzu da Yayan ki ya bani ke, na san dai ba maganar banza zai min ba, dan haka kin badu ko ba kya so, daga yau na daina kwana da hawan ruwan ki, *Minalu tawa* kawai."
Kira ya dinga yi bata ɗaja ba saboda wayar ma na ɗakin su can sama su kuma suna falo, tsabar bata yanayin daɗin yau a falon ma take karya kumallon ta, shi ma ba wai ci bane take tana dai tsakura tana kai wa baki, amma kallo ɗaya za ka mata ka gane ba ta yanayin daɗi, har Goggo ma da za ta