Showing 297001 words to 300000 words out of 382072 words
wanda ya samu ganin shi saura kan hakkuri ya basu kan hakan.
Hjy karima ta dawo ta samu abinda ya faru hankalinta a tashe kafin kuma ta fara sababin cewa an munafunce ta tunda ba a kirata ba tun lokacin.
Ba dai wanda ya biye mata don bashine a gabansu ba su yanzu dole kuma ta dawo aka hade kan jin yaya za ayi dole su baffah ne da modibbo zasu biyan shi.
Anan kuma suke jin labarin cewa suma din su Alh Nuhu har baffah buhari ma ashe an tafi dasu Abujan ga gidajen su da aka kulle zance ya gama bazuwa cikin gari ko ina ko a lokacin.
Da farko sun dauka zancen wasane duk kazafine ko barazana don mahaifin nasu zai iya fitar da kanshi kan ko menene ya tasa haka kuma su basu yarda cewa wanan laifin shi ya aikata ba dukda wa yanda suka san lokacin sun fada masu gaskiya kan hakan.
Hankali yakai kololuwan tashi kowa ya nufi inda yafi mai sauki ya zauna inda mafi yawan su a gidan gadon su suke don matan ga baki daya nan suka nufa suka zauna a nan diyan nasu da suke ganin basu iya zama cikin wanan gidan a yanzu suke samun su ayi maganan da za ayi din a lokacin wanan rikicin.
Sauri nakeyi na isa gida dan hold on daya tsayar dani a hanya don nasan lokacin umma tana can ta tayar da hankalin ta ganin ban saba kai hakan ba gashi kuma na kasa samun layin umma din.
Ina mamaki tun lokacin dana sawo kai na hango motoci a kofan gidan don motocin kawai kansu abin kayar da gabane saidai sanin dan filin namu in baki mata ba na fada a baya cewa motoci na yawan parking a wurin don hilan dake akwai garemu na parking.
Haka na karaso a gajiye na parker motana dab da gidan mu inda nakan aje motan in shiga gida har Abdul duk a nan yakan aje motanshi.
Haka kawai na dinga jin gabana yana yawan faduwa ban yiwa wa yanda na sama tsaye wajen magana ba .
Ila dai nafito da ledan dana sayo masu tsaraban idi,iroko dana tafi din ledan a shake yake da kayan marmari sai dayan da tsaraban Ammar ne a cikin sa daya dameni in sayo mashi unders na maza .
Tun daga dan matakalan steps din mu wani kamshi ya daki hancina amma haka na daure na karasa ina mamakin wanan wani irin kamshine kuma ko maniyace ta saka a part din su.
Na turo kofan da sallama kamar yadda na saba shiga da sallamana gidan umma i am back na fada tun turo kofan don nasan ranan zansha fada sosai a wurin umma kan rashin kiranta in sanar da ita inda nake a lokacin.
Saida maganan ya makale min don hango umma zaune tana sharan kwalla da nayi ga wasu mutum biyu a zaune tare da ita .
Saidai sam basuyi kama da iyalan jinsin mu ba don mu din ba bace muke ba don daga hancin mu da giran idanun mu haka manyan idanuwa.
Ban damu da ko suwaye a zaune ba lolacin na karasa da sauri zuwa wurin umma din ina tambayan ta da yarbanci su waye me sukazoyi me sukai mata kuma ?
Kabo anty sahiba Ammar ya fada daga inda yake zaune a takure na amsa da Ele wooo sai na juya da pigin ina tambayan shi .
Waitin dey come do here sunyiwa umma wani abune maimakon umma din ta ji dadin damuwan da nayi da ita din sai kuma ta juya fada dani kan in natsu mana.
Wanan shine wanda yasan komai na mahaifin ku sai yanzu ya gane inda muke da wanan maganan ya taso ya dade yana neman mu sai yau ya samu zuwa inda muke.
Oda na fada ina mikewa don ni na gaji da burgan mutane a yanzu garemu basu nememu ba a cikin wahala sai lokacin da dadi yazo muna kowa ya taso yana fadin shi shine .
Duk bina sukayi da kallo yayin da umma ke fadin ba zaki gaida su da zuwa ba wai meyasa kike hakan wani lokaci.
Sai lokacin na dago kai na kallo inda suke daga inda nake tsaye nace you are wellcome ina wuce wa abina .
Cikin kunan rai umma din ta kara dakatar dani lokaci guda cikin daga murya lokacin har nakai kofa ina daga labule zan murda handle din kofan dakin.
Na juyo ina fadin e dakun umma bafa wurina sukazo ba wa yan nan asalima ban taba jin ko labarin su ba don haka me zan tsaya nayi duk a cikin yarbanci muke magana suna kallon yadda muka juye a yanzu muka zama yaren karfi da yaji ba zakace mu din jinin Abbamu bane mutum mai turaci da rike kabilan shi na fulatanci.
Yau sai ga iyali shi sun gani sun gani sun rikide sun koma wasu kabila ko al,adanmu sun juye mun koma kamar kabilun kudu sak.
A take idanun shi suka kawo ruwa lokaci guda ya fara magana da tun da ya gabatar da kanshi gun umma basu samu daman yin wani magana ba suke kuka daga shi har ita kuwa din.
Look miss Sahiba munzo nan kan pieces ne ba wani abinda kike tunane bane ya kawo mu asalima munzo ne don mu roke ku gafaran abinda ya faru mukayi maku gaisuwan rashin mahaifi dan uwa jigo a garemu watau mahaifin ku.
Wani kallo na jefo mai dan yan kan na kiris su tashi min a lokacin badon gyaran Allah ba jifa wai gaisauwa sukazo yi muna na mahaifin mu a yau din nan.
Kamar yasan abinda nake kallon su dashi naji yace don a lokacin da abin ya faru munzo daga can Hong Kong inda ya barmu da niyar zaizo yayi aiki a nan sai labarin mutuwan shine ya rikemu.
Munzo mun nemi dcp Ali lokacin don shi mukafi sani a cikin yanshi amma sai ya dauka wani abune na daban ya kawomu gareshi lokacin .
Don ya zaci munzo kan wani zancen kudine ko wani abu da zamu karba a wajen marigayi din mun nemi mu ganku sai aka fada muna kuma wai kun bata.
Wanan zancen ya daure muna kai a karshe dai haka muka gaji muka koma ba tare da mun gane komai ba akan ku wurin su sai gashi lokacin da kuka fara wanan case kwatsam labari ya riske mu.
Yasa na turo a tsayawa case din sai kuma naji ance wai ke kince kin yafe komai daga garesu illa fili kawai kuke so a baku.
Ni kuma nace ban yarda ba a yanzu komai da suke ganin sun sameshi a yanzu sai sun mayar dashi ko kuma su hadu da mumunan fushi a garemu.
Musan wanda ya mutu lokacin sane yayi amma ta sanadin su ya tafi don haka mu a wurin mu sune suka kashe shi don haka muma iyalan shi ba zamu kyalesu ba a yanzu da gaskiya ya fito.
Fuskan shi ko muryan shi nake kallo a lokacin na rasa wani daga ciki ya dauke min hankalina haka ?
Saidai maganan shi na karshe da yayi cewa su iyalan Abban mu ba zasu kyale a yanzu ba yasa naji wanan kalamin a wani bambarakwai.
Su iyalin shi ta ina ya akayi suka zama iyalin shi din yanzu don haka duk wanda zai kiraku akan waye ya daukaka kara a babban kotun Abuja kuce dashi.
Babban yaron shine mukhatar usman marwa ya daukaka kara a yanzu don ku kungama naku fanin an gani yanzu nawa fanin ne wanan .
Ku gafarce zance a karshe dani da abokina na rashin zuwa gareku a lokacin daya dace ace munzo mun taimaka maku alokacin da kuke cikin wahalan rayuwa.
Duk da hakan ba laifin mu bane an boye muna komai daya shafe kune a lokacin don haka kada ku zargemu da laifin hakan gare ku.
Da fatan zaku fahince mu don Allah ku yafe muna kan abinda son zuciyar wasu yasa muka aikata maku na rashin zuwa gareku na tsawon lokaci.
Saiya dukar da kai yasa kyale yana sharan hawayen dake zubo mai lokacin a idon shi ganin hakan yasa na juya zuwa dakina da sauri.
Saman godo na fada ina wani kuka mai tsuma zuciya kafin na koma tunane alokacin don ina ganin mu munfi kowa matsala aduniyan nan.
Daga wanan zuwa wanan matsalan sai yaush ne zamu koma kamar kowa mu shiga yan uwa muma mu san muna da dangi kamar kowa a duniya ?
Sallaman su na fara ji suna ma umma sallama hakan baisa na fito ba har yakai na daina jin muryoyin su a falon namu haka yasa na gane cewa mu kadaine a gidan lokacin.
Ban fito falon ba sai safe na tashi don zuwa wurin aiki har lokacin akwai rashin walwala ga umma dole na tsaya naga ta karya kumallo.
Bayan mun gama karyawa ne na mike naje na shirya sallama nayiwa umma na fita zuwa aiki misalin sha daya rana sai ga wayam umma ya shigo mmin
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ANA DARA GA , , , , , , , ,
8️⃣9️⃣BY, , , , , , , , , , , ,
ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , , , , , ,
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AL AKHIR, , , , , , , , , , ,
ONLINE PAID NOVEL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA BA TARE DA HAKKIN KOWA BA DON BIYA KI TURA DARI BIYAR 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK 08036959257
ALLAH SARKI AI RAINA BAYA BACI YANZU DON KIN FITAR DON NASAN AKWAI RANAN HADUWA SEE U👋👋👋👋
Kira bisa kira haka muke samun kira a lokacin saidai amsa dayane shine bamu san wanan zancen bamu don haka dole mutum ya kyale mu.
Karshe ma kashe layukan wayan mu nayi sai can dare nake kunnawa in shiga median naga sakonin da suka shigo min a yinin ranan.
A irin hakane har ya Abubakar ya samu ganina a online yai min magana na bashi amsa da muna kalau ga dalilin kashe wayan namu a lokaci.
Yake fadin cewa hankalin shi ya tashi kwarai da rashin jin layukan mu a kunne sun dauka wani abun kuma ya faru damu don shi a yanzu hankalin shi baya kwanci.
Muna kalau na bashi amsa tare da tambayan shi iyalan shi dasu Faiza ya amsa a gundure da alaman akwai abinda yake cin zuciyan shi a lokacin.
Yake tambayana wanan din ya kara dawowa ban san wa yake magana a kaiba yasa na tambaye shi yace wanan dai da umma tace yaron baffah marigayine shi daya bullo yanzu a kan case din ku.
Banda time din wanan a yanzu don ban san meya kawoshi gare mu ba a yanzu din don haka bai a gabana na bashi amsa.
Cikin mamaki yace dani sister kin san ko waye wanan mutumin a yanzu kuwa duk da mahaifin kune ya dagashi a baya har ya zama haka a yanzu .
To shidin shine mai ma,adanai fiya da lissafin a cikin kan nan shine Mukhatar usman marwa da kike ji nima cikin mamaki din nace shine wanan din yace kwarai kuwa mahaifin kune ya dagashi har ya zama haka a yanzu din.
Ashine dalilin shi na son shiga zancen ku a yanzu din a iya binckena a kanshi na gano bada wata manufa yazo gareku yanzu ba.
Illa son da yake ya rama alherin mahaifin ku a gareku yanzu din sai dai ya dauki zancen kashin baffa da akayi da zafi don haka yake son a gano kaomai daga wanda ya hada plan cewa a kashe shidin yake son sani yanzu.
Sai naji yayi shiru na sake fadin hello yace ina jinki sai dai ni jikina na bani cewa daddy a wanan katon ba zai iya tsalake wanan sharian ba shima idan ya tsalake na kaduna.
Brother ban gane may kake nufi ba yanzu yace eh wanan karon kinsan tunda case din yakai su Abuja shariace za ayi sosai ba irin na kaduna ba.
Wanda a karshe zai iya shafan kowa gaba daya nasan zasu durkushe ba zasu rage dako allura ba a hannun su.
Wait a minutes nifa zan kirashi in fada mai wanan abin ya isa haka a yanzu sunan family din mune zaici gaba da baci ko yaushe a karshe kuda ke tasowa daga baya mutane zasu zo basu yarda da kuba ma.
Kai ya gyada min yace masha Allah da kike da wanan fahintan haka kike da tunane irin na maza kike da tausayi da jin kai irin na mahaifin ki.
Duk wanda ya kashe wani zaisu hadu a gaban Allah wata rana don shima bazai zauna gadin duniya ba ai dole yaje inda ya tura dan uwan shi.
Yau dukiyan da sukai haka don kanshi idan an nema babu ko rabin shi a hannun wasun su don ba dukiyan Allah da Annabi bane don haka Allah ba zai barshi a hannun su ba .
Da ace na tsaya na saurari wanan mutumin da na karbi lambashi a lokacin nasan zai mun amfani a yanzu zan kirashi in fada mai abar zancen haka ya bar duk mai hannu a ciki da Allah.
Saidai ko umma ina jin bata karbi layin shi ba har ya tafi ranan au yazo wurin ku ke nan ma ashe nace yazo ranan da dare na dawo na sameshi a gidan mu tare da umma.
Indan hakane zan tsanata binciken nomban shi ko zamu samu zan turo maki ki gwada yi mashi magana aji ko zai yarda ya janye zancen a yanzu.
Duk da ya kamata ace na dauka don mahaifin modibbo yana cikin zancen ya kara ban wanan shawaran sai sam ban dauki hakan a zuciyana ba.
Illa kawai yadda naga iyalan su suna cikin wani hali a lokacin yasa wani imani da tausayin hakan nasu ya kama zuciyana don nasan zafin irin hakan tun ina karamata.
Kawai nasan wanda ya mutu ya mutu ne wanan sharian tsakanin su da Abban mune gobe kiyama don ko ance su dawo da wanan dukiyan a yanzu ba samun shi za ayi duka a hannun su ba.
Haka dai mukayi sallama da ya Abubakar din da yake faman ban hakkuri kamar kullun yana kara tausan zuciyana kan abinda akai muna din.
Mun gama na kashe wayana saidai maimakon in kwanta in huta sai barcin ya gagareni na fada tunanen duniya kuma.
Wata zuciya tana izani kan me zance abar zancen a yanzu bayan su da farko basu tausaya muna ba sunyi son ranau sun rabamu da mahaifin mu.
Su suna tare da nasu a cikin jin dadin rayuwa wanda mu sam bamu samu hakan ba don bamu san dadin mahaifi ba a yanzu.
Iya abinda Allah ya debowa Abban mu ke nan a lokacin wata zuciya nawa ya fada min don mutum bai wuce lokacin shi ai.
Washegari na fadawa umma kaf yadda mukayi da ya Abubakar din tayi dan shiru kafin tace yana da wuya yanzu mukhatar ya janye wanan zancen yadda ya dauke shi da zafi haka.
Saidai a gwada yi mai maganan amma abune mai wuya yanzu ya yarda don irin amanan dake tsakanin shi da mahaifin ku a baya don marigayin ya daukeshi tankar wani dan uwa da suka fito ciki daya dashine.
Amma mu munfi kusa da Abba din a yanzu hukuncin Allah muke so a kansu bana mutum ba tun farko ma da ansan wanan abu zai shafi har inda ba a zata ba da anbar zancen dukiya iyaka su dai san muna raye a duniya bamu mutu ba.
Yanzu ko gashi Ana dara ga dare yayi don shi ma modibbo dayasan da hannun mahaifin shi cikin case din nan da bai yarda tun farko ya tazzara zancen haka ba ko don rufin asirin mahaifin shi din.
Umma kike ganin bai sani ba yayi hakan yasan komai shidai mutum ne mai tsayawa yayi aikin shi da gaskiya kawai don ko yanzu bawai ya damu da abinda zai faru kan mahaifin nasa bane ai tunda yayi ba daidai ba ai kinji abinda ya fada ranan kan daddy.
Yace yana ganin daddy yasan komai shine dalilin da baison a daga zancen nan a yanzu to kowa keda hannu a cikin case din nan dolene ya fuskanci hukunci daidai abinda yayi don haka a bari ayi sharian daya dace.
Har na shirya na fita zuwa wurin aiki muna zancen da umma nan muka barta gida ita kadai kowa ya fita zuwa nasa tsabgan.
Saidai ina isa zan shiga office dina idona yayi arba da oga sha,aban tsaye suna magana su ukku haka yasa nagane ashe yana kasan ke nan.
Office dina na shiga direct ganin hankalin su ya dauku ga maganan da sukeyi a lokacin na shiga na zauna na fara aikin daya dace a lokacin
Banfi minti biyar da zama ba oga Jimo ya shigo office din da wasu