Showing 264001 words to 267000 words out of 382072 words

Chapter 89 - ANA DARA COMPLT BY MAKAWA

MAKAWA   

29 Jun 2024

28440

iya ganina gaba daya yanayin fuskana ya sauya raina ya baci bakikirin idanuwana duk sun kankance na fara fadin .
Kuna ina a lokacin da aka watsar damu a cikin duniya ko lokacin da suka kashe muna mahaifin mu a kan abin duniya wani mataki a ka dauka a lokacin har batan umma damu da ba,a san ida tashiga ba na tsawon lokacin nan.
Yanzu lokaci yayi da komai zai baiya kara muradin mu a yanzu ba karban dukiyane kawai ba don nemawa mahaifana yancin sune da aka tauye a lokacin na dawo yanzu koda nan karbi komai nasu ba dolene abiwa mahaifana hakkin su a yanzu kan duk wanda ke da hannu a cikin cuta masu.
Na kare magana ina jefa mata wani irin kallo na ke kinsan koni waye kuwa a yanzu ?

ZAINAB IDRIS MAKAWA



ANA DARA GA , , , , , , , ,

7️⃣8️⃣ BY, , , , , , , , , , , ,

ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , , , , , ,

BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AL WAJID , , , , , , , , ,

ONLINE PAID NOVEL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA BA TARE DA HAKKIN KOWA BA DON BIYA KI TURA DARI BIYAR 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK 08036959257

ALLAH SARKI AI RAINA BAYA BACI YANZU DON KIN FITAR DON NASAN AKWAI RANAN HADUWA SEE U👋👋👋👋


Kallon mamaki suke bina dashi don abinda na fada yanzu a gaban su kafin gwoggo hari ta koma ga kallon danta tana fadin .
Kaga abinda yasa tun farko nace dakai mu fitar da bakjn mu a cikin wanan zancen ke nan ka matsa min saina gamsu na taushi zuciyan su yanzun dai kaji wani sabon fitinan da suke son su jawo a cikin ahalin mu kuma wai su yaya Nuhu suka kashe masu mahaifi.
To ke banda abinki mairo ai naga a lokacin da abin ya faru kina cikin hayacin kuma tare dake akai komai baki fadi hakan ba sai yanzu.
Wani murmushin takaici umma ta sake wanda ban taba ganin tayishi ba a fuskan ta cikin yan dakiku ta koma kuma ta daure fuskan ta murtuk kamar wace bata taba yin dariya ba.
Tace ga dalilin rashin fadan yanzu kin bada amsan shi da kanki hjy Hari kallon ta gwaggo hari din tayi na bam fahinceki ba fa ?
Ehh lalai na yarda dangin miji dangin mijine a yanzu harira don wanan abin da kuka nuna muna keda yayan ku yau da ace nice yar uwan ku bashi ba da dole zaku tsaya ku fahince mu.
Amma gashi gaba daya ku kafan kun kasa fahintar gaskiya a yanzu inka debe wanan dan gidan dcp daya yarda da gaskiyan mu ya amince damu har ya dauko mu wancan lokacin ya kawo mu nan kaduna muka zauna gidan mahaifin shi na kusan shekara biyu.
Amma a karshe ba ai komai ba saima na fahinci akarshe kamar yasan da kome ya faru a lokacin don yadda ya tura keyan mu da rana tsaka muka bar mashi gidan shi ba zaton haka ba tsamani a gare mu.
Kai mairo ke nan wanan kuma sabon sherin dashi kikazo yanzu ke nan har yaushe wani mai hankali zai yarda da wanan zancen.
Dakata mami don Allah wanan abin fa abin tsayawane a duba masu shi idan bata da hujjan fadan hakan ba zata fada ba a yanzu.
Ina tsaye sororo kamar wata wawuya a inda nake ina kallon mamaki tun yanzu ke nan dama kuma saida na zaci hakan zai faru don ba zasu taba yarda da wanan maganan ba.
Gwaggo na fada daga inda nake ta waigoni gami kura min ido na fara fadi a cikin kakkausan murya ina kallon ta nace.
To ina son kowa ya sani ni nan ban tashi zuwa da wanan zancen a yanzu saida na shirya wa hakan don duk wanan zancen nasan da yawan ku zakuyi shi dama a shirye nake da ko waye a cikin ku yanzu kotu sai muje shi ba a kan komai sai kan biwa mahaifana hakkin su don ina da shedu mai karfi akan hakan.
Mami ki tashi muje yanzu na fahinci wanan zancen zance ne da duk wani mai hankali zai zauna yayi duba a cikin sa bisa ga abunda suka fada a yanzu.
Mama mun gode da bamu lokacin ku da kukayi a yanzu na fahince ku na gane me kuke nufi kuma ina bayan ku har gobe dari bisa dari idan bukatan haka ya taso a gare ku.
Mun gode da fatar mu daka dade kanayi tun kafin kasan ko mu suwaye agare saidai kamar yadda mahaifiyar ka ta bukata ka fitar da bakin ka cikin wanan zancen don zaman ka lafiya a cikin yan uwa.
Murmushi yayi ya dan kalli umma din kafin ya juyo ya kalli fuskana a inda nake sosai fuskanshi dauke da alaman tambayoyi bila,adadin yana fadin zamu tafi saidai kuyi tunane me kyau akan hakan.
Haka zalika nima na tsura mai manyan idanuwa da a yanzu suke min bushe suke kuma matukar firgita mai kallon su a lokacin.
Da kyat na iya budan bakina da yai min nauyi saboda kuncin da zuciyana ke ciki a lokacin da kyat na iya furta mungode da kulawa kawai na juya na koma kitchen.
Ban tsaya naga fitan su daga gidan ba saidai naji tashin motar su subar kofan namu sai lokacin na sauke ajiyan zuciya ina runtse idanuwana a hankali cikin kunci.
Karan wayan umma naji ta dauka suna gaisawa har lokacin itama bata sake ba don yanayin da take maganan ya nuna hakan.
Naji tana fadin Allah ya kaimu anjima din to shike nan zamuzo din insha Allahu nagama hada muna breakfast na fito dashi falon na dora saman dining ban tsaya ci ba na koma daki nashiga wanka.
Kodana fito na shirya ban dawo falon ba zama nayi a daki ina kara bin dairy din Abban da kallo ina kara tara irin bayanan da yayi a cikin dan littafin sirin nasa.
Kafin inji muryan ya Abubakar ya shigo suna gaisawa da umma lokacin yana kara mata bayanin abinda ke faruwa a lokacin.
Sahiba ta fitane ya tambaya yana son ji idan ina ciki umma tace dashi ina ga ta kwantane tun fitan hjy hari daga gidan nan ta shiga dakin.
Mikewa nayi zaune saida nayi kamar minti uku a zaunen sanan namike naje gaban mirrow na dan gyara kafin in fito ina saye da wani dogon riga baki rigar jallabiyan matane irin mai sharp din nan na zaman gida wanan tafiyan da mukayi ne na dawo dashi sai dan gyalen daya daura a kaina nasa kamshin turare oud na matane ke tashi a jikina.
Sallamu Alaikum na fada daga bayan shi ina fitowa a cikin dakin yayi firgigit kafin ya juyo yana karba min tare sakin wani zazzafan ajiyan zuciya da har nake iya jin shi a lokacin.
Saida na zauna na fuskance shi na fara gaida shi cikin dakewa ya amsa min yadda ya saba don ko yaushe shi fuskanshi baka taba ganin fara,an afuskan shi.
Kullun kamar yana a cikin damuwa zaka ganshi ko wani ujula dake gaban shi bayan ya amsa min ne ya soma fadin .
Kiyi hakkuri domin jiya nazo maku da baki haka kwatsam babu sanarwa nima hakan bayin kaina bane daurowa hakan ya kama don in wanke kaina daga zargin da suka fara yi min akan ku.
Cikin lokaci daya yayi min duk wanan gajeren bayanin lokaci guda ido na dago na kalleshi nace zuwa dasu nan din a yanzu baida wani illa tunda aiki ya fara a yanzu ai.
Ok yace yana dan zakudowa daga kujeran yaci gaba da fadin yau akwai meeting da za ayi a can gidan kakan mu mallam Amadu inda kowa zai hadu kamar yadda suka bukata.
Shine nazo na sanar maku don na kira mama a waya na fara fadamata saidai kamar bayanin da nayi mata din ba zaku gane ba.
Sai kuma naga ai ba zaku san wajen ba shine yanzu nazo da kaina in baku addres din wajen inda gidan kakan namu yake ko zaku iya zuwa .
Don by all means ina son ku kasance a wanan wajen don hakan zai kara kwantar wa mutane da hankali don wasu da dama sun dauka cewa shirine dai akayi akan hakan.
Amma sai yadda kuka gani idan zaku iya zuwa wajen shine yanzu nakewa mama bayanin komai kika fito.
Saida na janye daga kallo shi kafin ince dashi whu not idan har kana bukatan muje wajen zamu zo ai da umma ne ko nida Ammar kawai.
Yes dole saida mama zaku ai don itace shedan komai a yanzu zaku sameni a wajen don haka kada kuji komai zan kuma kawo jimi,an tsaro don kada hakan ya jawo wani fitina a wajen.
Ok hakan yayi zamu zo insha Allahu na fada na fara laluban wayana ina turawa bello sako don kada in matan da addres din gidan har lokacin duka na tura mai.
Bayan tafiyan shi na dubi lokaci kafin inkai kwance sai lokacin naji umma tayi magana tana fadin.
Yanzu kina ganin cewa zuwan mu wajen bazai jawo wani matsala ba ke nan nace umma zuwan mu din yana da amfani tunda har ya fadi hakan zamu umma ba abinda zasu iya muna a yanzu don mun riga damun kafa sheda a kansu magana yana hannun security .
Dakin taron ya hadu sosai kan wanan kiran na gagawa da aikai masu har ma wanda ba,a zata zasuzo ba sun zo a wanan ranan.
Addua tsohon yayi ya fara gabatar masu da zancen ya kare da fadin kowan ku nan yanzu dai yana da labarin baiyanan iyalan Sambo da suka dawo a yanzu.
Sun kuma dawo da wani sabon zancen cewa tana karan Nuhu da yan uwan shine kan kashe masu mahaifi da kuma wawashe masu dukiyan shi.
Nan take wurin ya kaure da maganganu kowa da abinda yake fada a lokacin don wasu dai sam basu yarda da zancen da mukazo dashi ba wai wanan sherine da kazafi don kawai a batawa iyayyen su suna.
Tsohon yayi ta bada hakuri akan suyi shiru suji karshen maganan shi saidai kus kus yayi yawa a wurin abinda ya fada ne yasa su shiru wasu har da waige a lokacin.
Don cewa yayi yanzu haka zancen nan da akeyi suna cikin garin nan zaune sanan abinda bamu sani ba shine ashe sun dade garin nan zaune yarinyar tana aiki a nan.
Su Daddy da gwaggo hari a kusan lokaci daya suka iso wurin don sun iske kowa ya cika yana batsewa a lokacin.
A hankali na danno kan motana wajen motan data kara daukan hankalin wa yanda ke saitin window din da kofan cikin wurin dake wagale don yawan motocin dake shigowa haraban a ranan.
Motan ta dade ba a bude ba har yakai sun kagu da suga wanda Allah yaiwa ci gaba a cikin ahalin su ya mallaki wanan motan haka.
Can na bude lokaci guda da Ammar dake dayan gefen don umma a baya ta zauna ita Ammar ya zagayo ya budewa umma side din da take zaune ya karban mata handbag din ta ta fito.
Imnalillahi wa inna alaihim raji,un baffa ya fada tare da fadin shike nan ma gasu sun iso dada shike nan ma yanzu zance ya kare ke nan tunda sunzo.
Gaba daya wanda suke wurin suka mayar da hankalin su kan fararen Alhalin dake shigowa daga get din suna kallon ikon Allah.
Nan surutu ya fara tashi suna fadin wallahi mairoce kuwa lalai da gaskiya ita din ce kai amma akwai kama duniya haka.
Muka karaso nikan wallahi banji komai ba sai ummace nake jiyewa yadda ta saka damuwa tunda muka tunkaro wajen duk da nace da ita ta dake don Allah.
Assalamu Alaikum na fada tare da daga masu hannu kafin mu karasa inda manya suke zaune a lokacin muka zube kasa muka fara gaidasu wuri ya kara kaurewa da surutu lokaci daya.
Umma dake gurfane a gaban su baffa Amadu suna gaisawa a cikin mutunci muka mike tsaye tsaye kerere a a tsakiyan wurin bayan umma ina bin kowa na wajen da kallo.
Suma din kallon nawa sukeyi a cikin mamaki sai magana sukeyi kasa kasa akan mu kujerun roba farare aka bamu muma mu zauna muka dago umma muka zauna a tare lokaci guda kafin tsohon ya samu wurin ya natsu ya fara magana.
Sannu ku da zuwa tsohon ya kara fada tare da sake murmushi a fuskanshi haka yan uwa ke zuwa suna gaisawa da ita muna zaune hankalina ya koma a wayana da nake turawa felix sako a lokacin.
Kiran Adnan ya shigo na dauka bluetooth dina na gyara na fara magana ina masa bayanin da har ya kaini ga tashi tsaye na dan gusa daga can ina magana.
Eh shegiya tasan abinda ta taka wanan da ganin tama kila a turai take zaune ko irin rikkakun yan daban nan na lagos take zaune dasu.
Gungun wasu samarine ke fadin haka daga gefe daya daga cikin su har da diyan su Alh Nuhu dasu Alh gyade da sauran su.
Bayan tsoho ya samu wurin yayi shiru da kyat ya kallemu yacewa Umma Mairo baki kyauta muna ba da kika shige cikin duniya haka shiru baki kara waiwayan gida ba tsawon lokaci haka har muna daukan ko kun mutune mairo ?
Bayan nan kwanan nan kuma mukaji bayanan ku wurin bukin yar gidan Ali dcp sai kuma mukaji shiru sai kwanan nan muka sake jin wai yarki tayi karan yan uwan mahaifinta a kotu kan wasu dalilai.
Umma tana shiru sai faman goge hawayen dake zubo mata a fuskanta da takeyi Ammar yana dan lalashin ta ta hanyan dan buga mata kafada yana mika mata abin gogewa.
Tambaya tsohon ya kara jefowa umma dake kurum bata bashi amsa ba sai hawayen da take sakewa .
Can na dago kai na dan kalleta ina magana a harshen yarbanci nake fadin ta tashi mu tafi zaifi da wanan hawayen da take sakewa haka.
Baffa hamzane ya taso daga inda yake zaune yaje wurin tsohon sukai magana kus kus dashi na dan lokaci kafin ya dago yana fadin.
Mun san a yanzu gaskiya ba zata iya magana ba duba da a nan duk an hadu kuma a duba yawan shekarun da aka dauka ba a tare dole yau din nan a fama mata mutuwar mijin ta gaskiya.
Don haka a barta ta huta daga baya sai a zabi wasu da zasu zauna da ita su fahinci dalilin ta da tsoho ya tambauye ta don haka ayi hakkuri har su sauko.
Wanan ai ba zai yuyu ba, ba inda zata tafi tunda har taso ta wullakanta muna mahaifan mu don wani bukatan ta can na banza datazo dashi .
Wani kuma daga cikin su yace wani yasata barin gidan dama da,a yanzu dawowan nasu zai jefa zukatan mutane da dama cikin tashin hankali.
Kawai tunda an hadu yau din kuma tazo tayi bayani kawai kowa yaji tayi magana shine abin ji don ba zamu yarda mahaifin mu ya halaka ba saboda su.
But na mike ina kallon mai maganan na nunashi da yatsa na fara fadi a cikin harshen turanci kada kayi kokarin sukan mahaifiyan mu a nan.
Don mahaifiyan mu ba sa,ar yin ka bane idan kana son jin wani abu ka bari sai ranan da kotu ta bukaci zuwan mu kaji.
Lokaci daya suka fara tayar da hayani wurin ana tattaresu don kaucewa fita sai shar suke faman zubawa kamar zasu zo su duke mu.
Tafawa nayi na sake mikewa tsaye don naji suna fadin yau ko mu ko su a wurin ba wani sanaya ko duban halaka a tsakani yasa na mike na fara tafawa a hankali ina zagayan su .
Good, ku kawo inda nake son kuke au ashe ku har kuna da uban da kuke gani kuna jin dadi bayan mu naku uban ya mayar damu marayu ya kuma jefamu cikin duniya wullakance.
Kowa wurin yayi shiru yana kallona don abindana fada din naci gaba da jefa masu kallon tsana ina tsaye kyam a tsakiyan dan filin taron
Innalilllahi manyan ke fadi masu jin turanci daga cikin su, a harzuke baffa Hamza yace kunga ku bari abi abin nan yadda aka tsara shi yanzu kunji abinda ke shirin faruwa a nan kuma duk ku kuka ja.
Tare guy din da yafisu zafin nama akeyi yana tun karoni nace ku barshi ya tabani daga yau ba zaiyi gigin kara taba wani ba da sunan zuciya.
Muddin ka iso nan ida nake zaka kare rayuwan ka a daure gidan maza wallahi kowa yai maka tsaye a kasan nan kuwa .


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login