Showing 351001 words to 354000 words out of 382072 words
hakkin zama da kowa nasa tunda Allahbya hore min abinda zan ciyar dasu din .
Ban kara magana ba illa matsua da ya tashi ya bar min dakin dana matsu yayi lokacin saidai kuma naga baida niyar yin hakan shi asalima kamar dadin zama yaji a dakin shi.
Saima naji yana fadin da safe zasu tafi an riga da anyi masu bucking din jirgi karfe takwas na safe shine nazo na sallamesu saidai zanso a bar Faiza da wata babba a nan tare dake idan hakan zai samu .
Faiza tana aiki a kaduna na fada don haka dole ta koma aiki saidai Fatima da zamu zauna tare da ita zasu bari ina gani dan shiru yayi kafin yace anyway zanyi magana da uncle hamza idan na fita yanzu asan abinda za a yi akai.
Sai kuma yakai hannun shi saman goshina yana fadin don't be a lazy tun yanzu kin fara rakin barin gida umma will be with you soon nasan shine damuwan ki dai yanzu.
Dan lumshe idona yayi banyi aune sai naji yakai min kiss a gefen fuskana yana fadin take care zan tafi saida safe ya mike tsaye ya fita da sauri daga dakin.
Nan ya barni cike da mamakin wai meyasa maza basu da kunya ne wai mutumin da yake a matsayin yaya a gareni ko mahaifi amma shi sam ba kunya ko wani nauyi a idon shi sam a kaina.
Har barci ya daukeni bangama tunanen zantukan mu dashi ba ga kum yan uwana sun shiya barina da farko ban dauka zanji komai ga tafiyan su ba amma yanzu dana tabbatar haka dinne sai nashiga damuwa.
Haka su sister suka kawo masu alheri har dakina suke suna min ba,a haka baisa nayi magana ba lokacin suka tafi.
Barci barawone shine ya daukeni har na rage jin irin yanayin da nake ci washe gari kuma aka tashi da wuri kowa yayi haraman tafiya duk da sammakon mu amma saida aka kawo abun karyawan su daga gidan mahaifiyar mukhatar din.
Bayan sun karyane mota tazo ta kwashesu hardani a rakiyan su don mukhatar din da nake kira da Uncle a yanzu don na rasa sunan da zan kirashi dashi wanan lokacin.
Ga manyana nata karfafa min cewa nayi biyayya na girmama duk wanda ya dace nabashi girman shi haka in zama mai tausayi da taushin zuciya ga kowa koda maigadin gidane.
Wanan huduban abokan arzikin mune na lagos da sukayo min rakiya su hudu har maiduguri daga cikin su tare da muniyat da makwabciyan mu Aminat suke yawan fada min hakan damun kebe dasu.
Dagani saishi a motan muna baya driver yana jan mu a gaba sai motar dake bi muna su faiza ne kadai a cikin ta ko wani mota biyar biyar aka dauko su a cikin lafiyayyun motaci masu kyau da tsada.
A gaskiya ko don wanan karamawan danaga gun mutanena ya isa zuciyana ya sassauta abinda nakeji anty muniyat ce ke wanan maganan lokacin da muka fito zamu shiga motar dan bamu san shima zaizo mu tafi tare dashi ba.
Gaskiya kan an karamamu sosai anty Amarya ta fada na dan yi dariyan yake wanda shine dabi,ata kawai ba yawan magana.
A daidai lokacin Motanshi ta shigo gida ta tsaya daga dan nisa kadan damu ya fito da sauri da alaman yaso makara yake gani.
Inda su gwaggo suke ya fara isa da sauri yakai kasa gwiwa bibiyu a wurin yana gaidasu suka amsa mashi suma a cikin mutunci da girmamawa zaku tafi ke nan ya fada a cikin gurbatatcen hausan shi don ba hausan yake ji sosai ba yare ya amshe harshen shi sai turanci.
Eh mukhatar sannu da dawainiya mun gode kwarai Allah yayiwa aure albarka ya baku zuria masu albarka ya amsa da amin nagode kafin ya mike.
Wurin su faiza ya nufa suna ba,a tunkan ya karaso yake fadin kedai badake za a tafi ba sai kin kwana muna biyu a nan zaki koma .
Bayan ya gama dasune ya nufo inda nake tsaye tare dasu muniyat din ya gaidasu nan manya suka sake addua daga inda su gwaggo suke tsaye gwaggo kudidi tace ashe mutanen nan haka suke da yawan ibada ?
Suna da ibadan kan saidai shirme yafi yawa a cikin sa don dai suna hadawa da al,ada sosai idan ba yanzu suke gyarawa ba.
Shine yasa ai nasan ba wani aikin banza su mairo suka aikata ba can da diyanta don dan zaman umuran da mukayi da ita na fahinci tana da rikon ibada da kamun kai sosai wallahi gwaggo Amina ta fada.
Aiki a zahirance ai bashi bane zuciyar mutum wayasan abinda suke aikatawa a boye tunda ba mijine dasu ba can rayuwan lagos fa idan ka shigeta sai a hankali gwaggo hari ta fada tana yamutse fuska.
Kai haba hjy hari koma meye ai tunda sun samu sheda haka ya wadatar don Allah ki iya bakin ki akan mutanen nan yanzu tunda Allah ya wanke muna su yar uwanta hjy Asiya ta fada.
Shiru tayi bata tanka ba don ta fahinci me yar uwan nata ke nufi da zancen ta akan ta daina maganan haka kada zancen ya dawo kunnem mu ba abu mai wuya bane yanzu inji.
Yana isowa inda muke tsaye ya dago ya kalleni tare da daga min gira yana fadin yaya jikin ya kika kwana ?
Not bad na bashi amsa ina gyara rufin lafayan dake saye jikina lokacin don shi anty amarya ta ban shawaran na dinga yafawa tunda an zuba min su da yawa a kayana.
Lafaya din yayi min kyau sosai a jikina sai kamshin turare da nakeyi wanda yanzu kan ya fara zama min jikina duk da rashin son kamshi da ban so ada.
Kana yin abinda baka so don ka kyautata rayuwan na tare dakai don kawai farin cikin maishi haka anty amarya ta fada min a karshe da take bin jikina da kamshi.
Zo naji lafiyan jikin naki kunnena yaji lokacin da banzata yana fitowa dags bakin uncle mukhatar din lokaci guda.
Yi nayi kamar banji me yake fada sai na basar da fadin antashi lafiya ya mutanen gidan suka kwana lafiya ya fada yana cusa hannayen shi a cikin aljihun shi ya kara kallona yana fadin mu karasa airport din kada su makara.
A nan kowa ya shiga motar kamar yadda sister ta tsara komai don tana wajen shine muka rakasu airport din ko a motan ma da zamu hannun shi yana sagale a cikin nawa yana dan matsa min su a hankali har muka kai airport din yana dan jana da fira ta hanyar tambayoyi su masu tafiyan ina masa bayanin wanda na sani.
Saida muka tabbatar tafiya ya kankama don muna zuwa aka kirasu muka fara sallama lokacin ne naji wani irin yanayi kamar kuka zaizo min saga muniyat ta fara abinda yasa nawa saukowa ke nan.
Rugumoni naji yayi a jikin shi tare da kama hannun fatima dake tsaye a gefen mu don mu kadai muka rage sai sauran yan uwanshi da suka rakosu suma da sauran mutanen shi a wajen.
Bai bari munga tashin su ba muka dauki hanyan wurin da motan take aje ya shigar damu muka koma gids har lokacin kuka bai tsaya min ba.
Muna shiga dakina nayi kokarin shiga kai tsaye sai naji ya rikeni ta baya haka yasa dole naja na tsaya na fada a jikin shi naci gaba da kukan da nakeyi fatima ma ganin ina kuka yasa ta fada saman kujera ta makure tana nata kukan.
Bayana ya dan fara bubugawa yana dan murmushi kafin yace why are you crying ko zama nan ne bakyaso na mayar dake kaduna yau din nan, idan zama can ne yafi maki nan din ?.
Kaina girgiza ba tare dana furta komai ba nayi kokarin zare jikina daga nasa amma sai naji ya kara rikeni tam a jikin nasa ya kwatar min da kai saman fadadan kirji shi.
Na dan lokaci ina lafe sai sheshekN kuka nakeyi a hankali ki duba fatima ma kin sakata tana kuka kamar ke don tags kema kinayin abu kamar karamar yarinya.
Sai kuma naji yayi murmushi anyway kina da right na kuka a yanzu nasan irin pain din da kike ji a zuciyar ki game da hakan don bakya so na ko Sahiba ba zaki iya zama da tsoho kamana ba.
Hakan baisa na dakatar da kukan da nake danyi ba a lokacin sai ma kara dan sautin shi danayi a lokacin haka ya rike hannu zuwa part din dake gefen nawa din.
Key ya dauko daga wani wuri da bazaka san akwai ma,adana a wajen ba ya bude kofan sai lokacin ya dan sassauta rikonnda yayi min din yana fadin key din part din ki na wanan waje but is a secret kada ki bar wani ya sanda hakan don tsaro .
Yana budewa wani dan karamin falone ya baiyana a gaban mu shima dai kusan komai da akwai a nawa a kwashi nan din saida kala daya banbanta don nan din komai na cikinsa farine kal sabanin na part dina da yake milk colour.
Zaunar dani yayi ya nufi wurin abin sanyin dake dakin sai gashi dauke da goran ruwa da cup a hannun shi yazo ya zauna a kusa dani ruwa ya tsiyaya ya miko min kaina girgiza masa alaman a, a.
Open your mouth ya fada yana kai cup din a bakina zaki samu relief idan kin kurba ruwan kisha ko kadan ne ya fada yana kallon fuskana.
Kai hannu nayi zan karba daga hannnun shi kai ya girgiza min yana fadin a, a karbi kisha kawai ba musu na dan kai bakina na kurba dan ruwan kadan tare da lumshe idanu.
Good girl ina son mutum mai saukin kai kamarki yanzu fada min komai ya wuce ko mu shirya zuwa kadunan ne muna a yau din nan ?
Kai na dan dago na kalleshi yace yes saina kaiki a yau din nan na fada masu kukan banza kike min don sun wuce sun bar minke a nan don baki yarda dani ba.
Irin kallon da nake masa yasa yace yes koba haka babe baki yardani ba baki kuma daukeni a matsayin mijin ki kuma dan uwan ki ba har yanzu why zaki dinga kuka haka sahiba ?
Kina son kijawa kan ki wani matsalane kuma yanzu ki tashi ki dan kwanta nasan akwai gajiya har yanzu a tare dake idan kin samu barci a yanzu komai zai wuce a zuciyar ki duk a cikin harshen turanci yake min magana don dole sai dashi zamu fahinci me muke nufi.
Ta fito dan yau itama bakin ta zasu tafi duk da tasan yayi sallama dasu a daren jiya din kuma ya bada mota da za a kaisu airport.
Amma zata so su kara sallama saidai tana nufar part din shi ta hango wurin a rufe a zatonta yana ciki har lokacin bai tashi ba.
Saidai tana nufa kofar a cikin kasaita sai gaida ita masu aiki ke faman yi taji dayan na fadin hjy oga ya fita tun dazun da safe ai .
Cak ta tsaya tana sauraron me maganan tace mene tare da kallon shi tana son karin bayani daga bakin shi yace eh oga ya fita dazun nan .
Ina ya tafi da safen nan ta tambayi kanta tana juyawa don barin wurin haka ta koma part din ta har bakin suka tafi bata daina tunanen inda mijin nata ya tafi ba tare daya sallameta ba.
Duban lokaci tayi idan ba karya idon ta ke mata ba yanzu shabiyu da wani abu na rana ji tayi ranta ya kara baci fiye da farko sai lokacin ta mike zuwa falo har lokacin abinci na ajiye haka ya karasa ranta baci karo na barkatai.
Zama tayi don taci abinci idan ya dawo sai yaci nasa da sauri dayan matan yar aiki ta karaso ta fara zuba mata hannu ta daga alaman ya isa hakana.
A hankali ta fara ci bayanta jawo abincin zuwa gabanta saidai da kyat ta iya hade spoon din farko data saka a bakinta tana taunashi kamat maicin magani.
Ina mukhatar ya tafi haka koda gidan hjy ne zai tafi atlist zai fada mata cewa zai tafi gaida hjy balle wani wajen .
Waya ta dauko dake gefen ta ta danna masa kira ya shiga saidai bai dauka ba har kiran ya katse yana kallo kuma bai dauki kiran nata ba a lokacin.
Tsuki taja tare da kai hannu zata dauki spoon din da take cin abincin dake gabanta sai zuciyar ta ya hasko mata ke kodai yana tare da amaryashi ce .
What ta fada karda ace mukhatar ya samu kebewa da wanan yarinyar ke nan a yanzu wait ta fada tana kada yatsun hannun ta suka bada sauti.
Impossible ta fada tana mikewa tare da daukan wayan nata ta shige part dinta a hasale a nan tabar abincin bata damu da rashin karyawanta ba na ranan.
Kira ta sake danna mai wanan katon ma ba,a dauka ba har kira uku bai daga ba abinda ya bata mata rai ke nan zuciyar ta kuma ya kara tabbatar mata da lalai ya samu kebewa da amaryan sa ke nan duk da a gidan ta ya kwana ranan kuma tasani .
Me hakan da mukhatar yai mata yake nufi yanzu yana nufin har ya fara juya mata bayane kan yarinyar nan ko me hakan da yai mata yake nufi yanzu ?
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ANA DARA GA , , , , , , , ,
1️⃣0️⃣5️⃣BY, , , , , , , , , , , ,
ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , , , , , ,
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AL, MANI ,E , , , , , , , , , ,
ONLINE PAID NOVEL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA BA TARE DA HAKKIN KOWA BA DON BIYA KI TURA DARI BIYAR 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK 08036959257
ALLAH SARKI AI RAINA BAYA BACI YANZU DON KIN FITAR DON NASAN AKWAI RANAN HADUWA SEE U 👋
Zubur na mike zaune don tunawa da inda nake kwance a lokacin jin motsin mutum a bayana yasa na juya da sauri shine azaune saman gadon nasa da nake kwance a dakin.
Yana zaune ya tasa laptop a gaban shi yana aiki a cikinsa kokarin tashi nayi zaune naji yace lokacin sallah bai karasa ba da saura a nan.
Don haka kwanta ki huta kinada sauran lokaci har yanzu na hutu is just past twelve now duk maganan da yakeyi hankalinshi nakan aikin da yakeyi a lokacin bai daina ba.
No i want to easy myself na fada a dan kunyace naji yace you can go ga bandaki nan a nan kaina girgiza masa tare da fadin zan tafi wurina in kewaya daga nan na duba fatima.
She is OK here so kada ki damu da ita but you can go don naga you are not safe here yadda kika tashi a firgice din nan .
Kunyan kaina naji don nagane ya kula da yadda na lalubi jikina bayan na waiga na ganshi zaune yana aikin da sauri nakai hannuna saman jikina najini nade a cikin lafayana dana kwanta har lokacin dashi.
Kunyan kaina naji ga fahintar abinda nayi din saidai na basar haka na mike ina gyara jikina kafin na waigo ina fadin nagode na fita zuwa waje.
Gidan shiru babu kowa a main falo din da zai sadaka da sauran part din gidan sai karan nauran dake aiki a lokacin gashi kuma an gyara ko ina sai kamshi ke tashi duk illahirin gidan baki daya.
Fitana yayi daidai da sake danna mashi kira da hjy falmata tayi a lokacin wanan karon ya dauka kafin ya katse babu sallama sai cewa tayi mukhatar ina ka shigane tun dazun na kira kuma baka dauki wayan ba ?
Kai tsaye ya bata amsa da fadin ina gidan amaryane ba tare da jin wani nauyi ko kauce kauce ba ya fada.
Ashar ta lalaiyo ta kundumawa gaba dayan mu lokaci guda duk da mamakin hakan ya kamashi amma haka bai hanashi sake dan murmushi ba tare da fadin mun gode ya kashe wayar.
Nan kuma wani haushi ya sake kamata lokaci guda ranta taji ya baci ga baki daya idon taya rufe wani bala,in kishi ya danne mata zuciya.
Mikewa tayi da tare da figan dan gyalen kayan jikinta da zumar ficewa gidan zuwa gidan da akai mata kwatancen nan ne gidan da nake.
Kannenta na ganin yadda ta fito suka tsare ta da tambayan ko lafiya muka ganki haka hankali a tashe zaki fita ba tare da kowan mu ba ?
Zanje gidan wanan yar iskan naci masu mutunci don naga tun yanzu suna son raina min hankali ganin irin kallon bamu gane wa kike zance a kaiba da suke mata yasa tace a hasale gidan Amaryan wanan munafukin mukhatar man.
Ehyyah anty please kada ki badamu mana tun yanzu mutune su samu abin fadi a kanki jiyan nan fa ta