Showing 90001 words to 93000 words out of 382072 words
SALAMA NA FADA NA KUDINE NA FITAR DA HAKKIN HAKAN RASHIN SANIN HAKAN ALLA YA SA MU FI KARFIN ZUCIYAR MU AMIN, , , , ,
Sahiba nada matsala ki barta a inda kika ganta kawai ni kaina wani lokaci ina tsoron wasu halaiyar yar nan don abinda takeyi bana kai sake bane.
Shiyasa tunda tace dani bata ci idan ta hadiyeshi ya zauna a cikin ta akwai matsala ko dan uwanta ta hanashi ci nima kaina bata so ina danci din nan sai ta kama fadin idan naci duk abinda ya sameni ta fada min gaskiya.
Kallona gwaggo Addah ta kara yi don umma tace mu daina kiranta da hjy ko mommy da muke fadi da mukirata da gwaggo Addah.
Allah ya sauwaka tace tana mikewa tare da fadin yanzu taci wanan abincin da modibbo ya sayo mata ko ?.
Taci kadan tasha hura shine take wanan barcin haka ai ni kaina bazan so a farga da hakan ba ba kuma zan matsa mata akan sai taci girkin nan ba a gaskiya don nasan abinda take nufi.
Dole akwai wani abu a cikin wanan abincin da nasu baizo daya dashi ba don haka kinga cinshi gareta matsalane ke nan .
Jikina yayi sanyi da wanan zancen hjy ta fada tana fita daga falon ba tare da ta iya furta komai ba ashe zancen ya tsaya mata a rai sosai fura hjy karima ta kawo mata don tasan tana shan fura sosai ta fake a nan take kawo mata da sunan taga tana so nan ko surukulle ke cikin furan .
Hmmm kishi fa kishi ne don duk sunan su daya dana birni dana kauye tafiyan su daya ne a wurinyin shi ke dai kawai ki godewa Allah kuma ki rokeshi kada zuciyar ki tafi karfin ki har ki fada kishin kaucewa Allah ki fada shirka.
Allah ya tsare ya kare shine addu,an da mu mata ko yaushe ya dace mu dinga yi kada sanadin kishi mu shiga wuta a gobe kiyama.
Muyi hakkuri mu danne zuciyar mu mu fitar da idon mu akan kishiya akan mazajen mu kokarin mu shine muga muna da abin dogara da zamu iya tallafan kan mu dana yayan mu da iyayyen tare da yan uwa Allah ya bamu abin dogaro da kanmu amin.
Ya sassauta muna zafin kishi a cikin zukatan mu ya rabamu da kyashi da hassada akan komai damu da zurian mu baki daya Allahuma amin don kishi akwai zafi koga macen da bata taba aure ba balleke dake dakin auren ki.
Manya sunce yara basu taba wasa suce wanan ne kishiyana saidai suce ga mijina wanan ashe abin dashi ake haihuwar ko wace mace ke nan (KISHI)
Shine abinda ya taba hjy karima tazo gidan ta samu miji da matan shi da yan yayan su har sun girma tace kuma ala dole sai ta kaita ko ta fita a gidan mata Allah yasa mufi karfin zukatan mu amin.
Saman table hjy ta dora furan yana nason raba don sanyin daya dauka a fridge yau zan gwada yar nan hjy ta fadawa Nabila dake kusa da ita zaune tace Fa,iza jeki part din su yan uwa ki kira min Sahiba.
Kallonta Fa,iza tayi ta mike zuwa part din namu ta shigo da sallama take fadin mommy is calling you sis .
Na dago daga sharan da nakeyi falon you mean gwaggo tace yes ta juya ta tafi sauri nayi na karasa sharan na leka ciki ina fadawa umma tace inyi maza in tafi.
Sallama nayi na shiga daga ni sai dan riga iya gwiwa mai dan hannu rigan silk ne yana da dan kwalliya a jikin shi ta gaba.
Ina shiga nake gaida ita don duk suna falo suna kallo ita da yaranta mata tace min Sahiba i warn you wearing dis cloth with out putting hijjab.
Sorry ma na fada ina kaiwa kasa nace sis said you are calling me tace eh zaku tafi unguwa gidan yayan ku anjima da yan uwan ki don haka ki shirya.
Da sauri na dan kallota ta gane abinda nake nufi tace ba wani gida bane yayan ku na nan gidan zaku duba muna matar shi da bata da lafiya.
Yes ma na sake fada kafin nace na now, we go go, tace after four prayer nace yes ma na mike zan tafi take fadin nazo na dauki fura gashi in sha rabi in bata rabi tasha tunda ina son fura har yarta Nabila na fadin sufa, tace baida yawa, na dauka da murnana ina murmushi.
Budewa nayi bayan na dauko kofi na dawo da sauri na na dan bulbula a cikin kofin ina daga farin goran furan ina duban yawan shi.
Na aje ina fadin ga shi na gode nayi azaman kaiwa a bakina da sauri na dawo da kofin baya ina sake wani irin ihu a firgice ina kallon su.
Suma firgita sukayi da ihun dana sake din a razane da sauri gwaggo ke fadin dama gwada ki nayi ki natsu ki saurareni.
Ina na firgita Nabila ta mike tazo ta rike hannuna zuwa kujeran data tashi sama tana fadin ki natsu ki jimu Anty ce ta kawowa mummy shi data fita ta dade tana kawo wanan furan idan ta fita shine mommy take son gwadawa a kanki.
Ita hjy din cewa tayi maza a kira mata umma tazo yanzu da sauri Fa,iza ta nufi part din namu ta kira umma din sai gasu da sauri.
Ina ganin umma ta shigo nake fadin umma shabi dey wan kill me naw umma din ta tsawata min tana fadin gaskiyane yar nan nada abubuwa a kanta
Nan ta shiga bayani umma na fada min a cikin yarbaci ina dan gyada kai na fahinta har ta gama yi min bayani ohma binu na fada ina hada hannuna wuri daya.
Na masu in bar part din don kaina dake juya min lokacin wurin kwanciya kawai nake nema a lokacin.
Na koma dakin mu sai barci ban falka ba sai can dare sosai hjy tayi sintiri a dakin mu tana dubani sai barci nakeyi sosai a lokacin kafin na tashi ina neman abinci da zanci umma ta tashi ta dauko min.
Ta aje a gabana na dago kai na kalli abincin na mayar da ido kan mahaifiyana saina ya motsa fuskana ina bata rai na kawar da kaina gefe daya.
Gwaggon ki ta dafo maki wanan ta kawo mak ki dauka kici ki kiyi sallah sai ki koma ki kwanta sai dan kara bata rai ina fadin d food no get herbal inside.
Ki dandana mana ki gani ta fada tana mikewa tabar wurin na sake kallon abincin sai na jawo bowl din abincin zuwa gabana da kyau na kura mai ido.
Kafin na dan diba kadan ina kaiwa zuwa bakina hannuna bai rawa kuma banji komai ba na kai bakina kamar an tsure munafuka cin abincin haka nayi.
A hankali na hade abincin dana kai bakina ina sauraren yanayin da zanji din sai Allah da ikon sa banji komai ba na kara diba na kara kaiwa bakina sannu a hankali nayi kamar spoon biyar na aje na mike na shiga ciki zuwa bandaki na dauro alwala na fito.
Barci nayi sosai har na makara a ranan haka na kwanta nace banda lafiya ba zan iya shiga school ba don ko idanuwa sun nuna cewa banda lafiya a lokacin.
Lokacin da mommy ta shigo gaida umma a dakin ta sameni kwance a hakana cikin ciwon kaina na dunkule a wuri daya.
Har lokacin fararen idanuwana sun rikide mun sun koma ja dasu don wahala ta dan dade a part din kafin ta fito ta koma nata part din cikin mamakin hakan a zuciyar ta.
Tsab ta labarta wa yaranta da yanzu sune abokan shawaranta tana cewa duk yadda akayi akwai abinda karima take zubawa ga abincin nan.
Don haka kawai ai mutum ba zaiki cin abinci haka da gangan ba dole akwai wani abinda takeyi na boye wanda bai dace ba.
Koma meye Allah ya mayar mata da aniyar ta ko menene mudai bamu bita da sheri ba amma nasan dole akwai abinda haka ke nufi ai.
Sun dauki lokaci suna wanan hiran a tsakanin su kafin su kawar su dauko wani zance su kama duk dai zancen na tsaye a cikin ran
hjy har lokaci.
Ban samu kaina ba sai zuwa rana na iya dagawa nayi wanka na dawo normal dani duk da hakan kasala ne duk jikina nake jin hakan kwana kaman hudu tsakanin faruwa hakan muna zaune da yamma mukaji.
Sallama anyi a part din namu na karba yaran mommy ne suke shigo muna da kwalayen abinci irin su taliya da sauran su har gas din dafuwa da tukwane saida aka kawo part dinmu suka saka a dan karamin kitchen din dake part din don ko wani part a ginan shi akwai dan kitchen da store makale da ginan sai dai bai kai wanan babban dake can ta kofan baya ba.
Umma dai tana zaune tana kallkn su saida suka gama aje komai saiga mommy ta shigo daga karshe takai zaune tana fadin.
Mairo wanan kayan abincin kune Alh yasa a kawo muku zaku dinga girkin ku a nan yanzu ba sai kun hada da kowa a gidan ba yanzu akwai shimkafa taliya indomei da garin alabo da na semo da sauran kayan girki sai ku girka abinda kuke son ci a kullun.
Wanan kamar dawainiya muka kawo maku kuma umma da fada tace aiyiwa kaine don kamar kanmu muka taimakawa ga hakan Allah dai ya raya muna yaran nan rayuwa ya raka tace amin.
Tana tashi daga wirin da take zaune ta dan kalloni tana fadin zuwanki garemu sahiba yana shitin zama muna alheri ga baki daya a yanzu shiyasa akace kada ka wullakanta bako ko yaya yake.
Bayan fitan su na mike na nufi wirin kayan na dan tsaya ina karewa kayan kallo kafin na duka na dauki abin shara na sharo kitchen din tsab na fara jera kayan abincin.
Abu daya nafi jima dadi kamar wanan garin elebo da suka saka muna mai yawa a cikin kayan saidai wai Nama da kifi zamu dinga dauka a fridge din cikin gida idan mun tashi girki don fridge din dakin namu ba freeze bane.
Kaf har aka gama wanan wainar hjy karima da bata zama gida bata san wanan zance ba sai ranan ta gama girki Asabe na kallo ta diba kamar yadda ta saba a kullanta ta mika mata takai mata part dinta ta dawo tana fita ta dan labe ta ganta tana zuba abu ga sauran miyan ta motse don dama tunda taga anyi haka take zargin akwai wani abu kuma gashi hjy taja mata kunne kan ta saka ido sosai taga abinda hjy karima din take masu a girkin su sai gashi kuma ta gani.
Da farko bata so yarda da hakan ba saida mommy din tace kin san dai nice na daukoki gidan nan da kuma a guna kike in ba yanzu da kuka hade ba idan har cutan mu take yi to harke ake cuta don duk abinda akayi tare dake muka ci shi a gidan nan.
Wanan yasa jikin ta yai sanyi ta dawo hankalinta da ta kwadaitu da dan abin da hjy karima din kan mata ihisani dashi don kama bakin ta a kanta mata ku kula da yawan mutane badon son ransu suka juya ma baya ba.
Sai don kwadayin abin duniya da akan basu a jaye su dashi hankalinsu ya raja,a ga amarya har su bar wanda suke tare dashi su hade kai da bakuwa sabon zuwa don zuciya bata da kashi.
Saboda shi alheri bai bar komai don kyautatawa yana saka kaunan ka a zuciyan mutane har suji suna kaunan ka da zuciya daya komai munin halin ka kuwa.
Gabanta ke faduwa sosai koda ta dawo hjy din ke fadin ki karasa zuba abincin akawa kowa nasa har wa yan nan bakin ki zuba masu miya mai yawa akai masu.
Tace baki hjy jiya da mukai girki tace a daina saka masu abincin yanzu don nasu sukeyi a aurin su basai an saka masu ba su.
Wani irin juyowa tayi da mamaki tana fadin a daina saka masu suna girkin su daban akan wani dalili ta tsareta da idanu.
Tace nima ban sani ba gurkin nan daina hjy kaf ba,ayi dasu ba jin haka ta fita fuuuu zuwa part din mommy din ta fado masu ciki a fusace tana fadin.
Duk ta samesu a zaune falon su ta soma fadin bako sallama yanzu Asabe ke fada min wai an daina saka abinci da bakin nan .
Hjy tace eh saboda basa iyacin abincin mu kada abin ya zamo barna yasa aka sayo masu wanda zasu iyaci a wurin su.
Din sufi mutane ko me don ni ban gane wanan fitinan ba haka wasukafi a gidan nan da za ace wai abincin su daban ne da namu yanzu.
Ba haka bane kinsan bawai sun iya cin namu cimakar bane na nan yasa yaran basa iya cin abinci wanan ai masifane aka daukowa mutane.
Wasukafi ko wa suka kai ta juya ta fita tana fada tare da fadin idan ba munafunci ba don me ba za a fadawa mutum ba ko banda hakkin sanin hakane a gidan.
Ya fita suka hade da Asabe a hanya take gaida ita da dan girmamawa har lokacin jikin asabe ya rawa don abinda ta ganewa idon ta din game da ita a kitchen din.
Nan ta shigo ta aje abincin suna gaida ita da aiki take fadin ga abinci an gama hjy saidai yau din na ganewa idona gaskiyan abinda kika fada min don ta zuba ta motsa miyan bayan ta gargadani zuwa kai mata nata da batayi hadi a cikin sa ba.
Shine na dan tsaya na labe na kamata tana zubawa a cikin wanan din daya saura shi kuma tace na dibarwa bakin nan daku nan na kai maku.
Ke nan wanan din tayiwa hadi ke nan bada nata ba ta tambaya tace hakane hjy ki gafarceni kusukurena ne da ban tsaya a inda kika ajeni na kula da komai yadda ya dace inyi ba.
Koma me tayi muna Allah zai isar muna a kanta don da nufin cutan mu tayi wanan abin da takeyi har Allah yasa yarinyar nan ta gane hakan da badon haka ba haka zamuyi tacin mugun abu tana cutan mu a kullun.
Ban faye shiga ko ina ba na gidan don ma umma ce data matsa na dinga shiga part din mommy ina gaida ita a can ba sai tazo nan ba ta samemu bamu je mun gaidasu ba.
Yasa har nakan dan shiga kuma bana iya sake jiki dasu kona shiga din don kowama tsoron sa nake a nan arewa tunda akwai hassada a zukatan su.
Zamu dafa abinda ramu ke so muci mu sha mai kyau amma hakan bai hana umman shiga cikin tunane ba don ita ko yaushe zaki ga ta zauna tayi shiru abin duniya yana damunta.
Ba komai umma ke tunane ba sai yadda makomar mu zata kasance a karshe in lokacin haduwan mu da yan uwan mahaifin mu yayi.
Sam ban da zuwan baki gidan ba ina kwance ne umma tace najie wurin mommy in samo mata paracetamol tasha kanta na ciwo.
Na shiga falon da sallama sai naja na tsaya suma din dakatar da dariyan da sukeyi sukayi a lokacin suka zubo min idanu a kaina.
U are wellcome ma nace dasu ina dan rusun nawa tare da fadin good afternoon ma suka amsa min kamar yadda na gaidasu din.
Nace mommy do u have paracetamol tablet, my mother want to use it, har lokacin ido suka zubo min suna kallo na da mamaki.
Tace go and check dat rober nd see na nufi wurin data nuna min din don nasan inda take ajewa sai naji dayan su tace .
Ina kuma kuka samu wa yan nan haka kamar kabila sai mommy din tace dasu diyar aminn Alh ne suka zo .
Daga ina dayan ta kara tambaya mommy din tace daga lagos suke aukuwa dai ga kama nan a fili wata ta fada a cikin su.
Tubarkallah ma sha Allah wanan yar kamar ba diyar kabila ba idan ka ganta sai dai idan ka kalli shigan nata ko batayi magana ba zaka gane kabilace ita.
Suma fa a cikin su dama ana samun kyawawa haka sosai wallahi kamar su sukayi kansu wurin kyau saidai kuyi mata magana mana wanan shiga haka ga yarinya haka da dirin daukan hankali.
Dariya mommy din tayi na dauko maganin tare da dan rusunawa ina fadin thank u ma na juya na fita duk suka bini da kallo.
Dayan mai kama da hamshakiya ta maya da bayan ta saman kujera tana fadin yarinyar nada shawa,a ga kuma irin