Showing 84001 words to 87000 words out of 382072 words
To waye mai sanyi muryan data fada ya danyi nazari can ya girgiza kai yana fadin haka ba zai yuyu ba ace wai harda baffa Audu cikin case din nan.
Ya fara girgiza kai yana fadin No No no no dukan su ke nan sun hudun duk baffanin mune sukai wanan aika aikan ko me Allah dai yasa bada daddy a cikin su ba ya fada da karfi gaban shi nata faduwa don yasan kusan kansu dayane ga komai da sukeyi
Fadawa yayi saman gadon ya dafe goshin shi da hannun shi daya yana fadin daddy ya damu da zancen yaran nan sosai me hakan ke nufi ke nan a yanzu.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
A NA DARA GA, , , , , , , , ,
2️⃣5️⃣
BY ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , ,
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AL BARI, , , , , ,
ONLINE PAID NOVEL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA NA FADA NA FITAR DA HAKKI RASHIN SANI A GARE KI ALLAH YASA MUFI KARFIN ZUCIYAR MU AMIN, , , , , ,
Dakin namu yayi tsit a lokacin don ba me iya cewa komai a lokacin saboda kukan da kowan mu yasha ranan don tausayin abinda ya faru damu din da umma taba da labari.
Asabe ce ga shigo da abinci rana dakin niki niki ta kawo muna har kuryan dakin ina kwance na kifa ciki a saman gadon daga ni sai dan guntun shortniker wando a jiki da yar rigan shi a lokacin ina kallon yadda dattijuwan ke satan kallo na saidai ban dauki hakan wani abu ba lokacin.
Gaida ita umma tayi muma muka gaida ita a cikin turanci ta amsa muna da kada kai umma ke fadin mu tashi muci abincin mana nace na koshi.
Kin koshi me kikaci nace bana jin yunwa umma ta kyaleni ba tare da tace dani komai ba taci gaba da abinda takeyi.
Hjy Addah bata kara shigowa dakin na mu saida dare data shigo muna zaune dukkan mu kusan rabin jikin mu yana ga na ummane.
Gaida ita mukayi ta amsa muna a dan cikin sakin fuska take fadin zancen karatun yaran nan mukayi da Alh dazun yace a wani mataki suke yanzu ne ?
Umma tace da ita taoardun mu suna hannun ya Abubakar don ya karbo muna trasfer da zamu dawo nan din tace ya kyauta da hakan da yayi.
Ta mike take fadin mairo sai kin saki jikin ki komai zai zo da sauki don yaran nan suma su saki jiki damu ki godewa Allah ba mai zuwa gidan nan a yanzu sai can ba,a rasa ba kinga har Alh zai kare shirun sa ba tare da wani ya sani ba.
Umma tace har da wanan abokiyar zaman naki kuna ganin ba zata fadawa kowa cewa muna nan ba yanzu ?
Bata san komai a kanku ba kema ki hori diyan ki da kama bakin su akan fadawa wani kafin lokacin sanin hakan yayi a garemu.
Umma tayi mata godiya ta dan dafa kan Amar ta fice dakin nan umma ke muna bayanin komai sai a lokacin na samu bakin magana nake fadin.
Umma kina ganin suma ba zasu cuta muna ba kuwa ni yanzu kowa daya shafi mahaifin mu tsoron shi nake ji don ban yarda da imanin su ba kuma.
Ban amince inzo nan ba saida naji inda za a kawo mu mu zauna don shi din wanan maigidan shine kamar amini kuma yaya ga mahaifin ku don a wurun shi kawai yake jin sanyi yana fada min wanan ko wani lokaci.
Umma akan me sukaki mahaifin mu haka a cikin su tace ba akan komai bane tun farko a kwai wani camfi da fulanin mu syke dashi shine dalili.
Wani dalili ke nan umma na tambaye tace akwai wani al,ada da sukeyi kan yayan su idan kana da diya mace har ya kasance yar taka tana da halittan hakoran gaba masu yawa a bakin ta har suna fita fili.
Zakaga maza suna rubibin ta kowa na son ya aureta don sun camfa da cewa mata masu irin wanan halittan suna da yawan arziki a jikin su.
Idan ka aure ta arzikin ka zai kara hayayafa ninkin banin ki fiya da dacan baya shanun ka zasu karu suyi yawaka dara kowa a rugan ku ko a gidan ku.
Wanan dalilin yasa mahaifin mahaifin ku ya shiga gasan neman auren kakarku mace kuma Allah ya bashi ita har ya auro ta.
A dalilin hakan kishi da bakin cikin hakan yasa sauran matan shi suka dauki karan tsana suka saka mata a lokacin.
Ganin haka yasa kowa ya daina mu,amula da ita a lokacin suka maida ita ware a cikin su bata gane komai a tsakanin su.
Wanan yasa shi kuma mijin ya mayar da hankalin shi gareta sai suka dauka wai yafi son tane a tsakanin su ga kuma wana camfin da sukai mata ya fara tabbata gaskiya.
Dukiyan kakan ku ya dinga habbaka sosai a cikin dan kankanin lokaci shanayen shi sai yawa haihuwa suke karawa a lokaci sa,an da yake na fatauci kuma yana kawo mashi kudi.
Allah da ilon sa kuma tun da aka kawo kakan ku gidan batayi wanki ba ashe tun zuwanta ta samu ciki cikin na fita sai suka kara tsanar ta fiye da farko da suke mata.
Har yakai sun cusawa yayan su mugun akida a kanta suma yaran basu kallonta a matar ubansu a idon su don sun tsane ta kamar yadda aka koyar dasu hakan har Allah ya nufa ta haifi mahaifin ku a wata bakwai duk da mahaifin ku karamine sosai kamar yadda ake haihuwan yan wata bakwai.
Wanan bai hana suyi sheri da kazafin cewa wai da cikin shi ta shigo gidan don haka ta haifa masu shege a cikin gida zai rufe tauraron yayan su ke nan na suna.
Lokacin haihuwan maigidan yana wurin fatauci don haka suka korata ta gida wai ta bar masu gidan su ko wanka basu yarda anyiwa dan a cikin gidan balle ita wai kada jinin shi ya diga masu a gida.
Duk da maigari ya kirasu akan su bari har mahaifin yaron ya dawo aji me zaice amma suka badawa idon su tankwa sukace sam basu yarda da hakan ba garesu.
Dole maigarin ya kualesu ganin fitinan zaiyi yawa a lokacin aka bar kakan ku a gidan su har zuwa lokacin da ya dawo ko yan uwansa basu yarda sunyi wa dan suna ba yadda al,ada yake da sati a radawa da suna a yanka dabba a ci yan uwa da abokan arziki.
Har lokacin da kakan ku ya dawo ya samu wanan labarin daya tayar mashi da hankali don yadda aka wullakanta masa mata da danshi.
Korar sauran matansa uku yayi suje gidajen su sani Allah sani ma,aikin Allah har zauren hardon su da yake duk gidane aka bashi hakkuri ya mayar dasu.
Amma ya barta a gida ta samu wankan kwarai ta gasu ita da danshi ga kuma alherin da yake aika masu lokaci lokaci saima zaman ta a gida ya fi mata kwanciyan hankali don ita ta kasance mace ce mai hakkuri sosai a lokacin.
Ya bukaci matarshi ta dawo anan iyayyen ta suka nuna basu yarda da hakan ba haka ya juya ya koma wurin fataucin shi da bacin ran hakan.
Kaduna ya yada zangon shi bayan ya gama sayar da shanayen shi a gidan dan uwanshi wanda yake shi anan suke zaune da iyayyen shi.
Watau mahaifin su Alh mai wanan gidan shiyabawa kakan ku shawaran mai zai hana ya dauko kakan zuwa nan tunda yana yawan shigowa garin sai su dawo nan dayani tunda iyayyen su suna nan dama cikin gari da yawan su.
Shawaran da yabi ke nan shine mafarin kara lalacewan duk wani abu daya faru a lokacin don dai ya je ya dauko matarshi suka dawo nan kaduna aka basu masauki suka zauna.
Kafin yasai masu wani babban gida mai kyau a nan unguwan rimi dun da iyayyen su suke zaune aka gyara suka tare a ciki nakatse umma tace sai da aka dauki lokaci mai tsawo suka samu labarin ai sunkoma kaduna da zama.
Nan kishi ya tashi sosai har saida iyayye suka shiga aka dawo dasu duka kadunan a lokacin har shi mahaifin ku ya fara karatu suna zuwa tare da sauran yan uwansu na nan .
Koda suka zo garin akai zancen karatun yayan sai uwayen su basu yarda ba wai su yaran su zasu lalace tarbiyan su ya baci don haka manyan yayan gidan kakan ku namadi a lokacin basuyi kararu zamani ba sai yawon bin motoci akarshe da sukeyi duk da arzikin dake akwai ga mahaifinsu kuwa sai suka taso kamar marasa ji a lokacin.
Shiko mahaifin ku ance shida Alh gidan nan sun hade kamar uwarsu daya don yadda suka shaku duk da ya girmeshi .
Kana mahaifiyar su Alh na gidan nan a karshe ta dauke shi ta mayar a gaban ta daya gama primary sai aka turasu karatu can FGC maiduguri ya gama ya fito da takarda mai kyau.
Shine dalilin zuwan shi karatu kasan waje har ya zama babban dan kasuwa koda ya dawo ya samu labarin mahaifiyar shi ta rasu da hawanjini.
Yayi kuka sosai aka fara zancen auren shi sai duk inda sukaji yana nema a cikin dangi dama gari zasubi su soke sai wata yar mahaifin sune ta hadashi da jikan ta nike nan.
Ta nuna muna kanta nace ke nan kuma yan uwane dasu ke nan tace a wani wurin zaman kanwa nake a garesu ai.
Taci gaba da fadin a takaice dai mahaifin ku wanan fitan dayayi waje karatune ya dawo da abun arzikin shi da suke gudu ashe boyon kurwa ya dinga yi a cikin yan uwa.
Abin duniya baya boyuwa don saida suka gano yawan arzikin da ya tara dama kuma sun camfa hakan kuma ya zamo gaskiya a yanzu don ya zarta su ga komai.
Sai kuma suka koma fadin ai arzikin mahaifin su dayai sanyi a yanzu sune yatatara ya mikawa mahaifin ku yake juyawa har yai wanan kudin su aka barsu.
Wani fili Alh gidan da akasa sayarwa a lokacin ya bashi shawara ya saya tunda yace yana son bude asibitin kanshi a lokacin.
Wanan sayen filin shine dalilin komai daya faru a lokacin don mahaufin su yana rasuwa da shekara daya suka tayar da kayan baya kan cewa lalai sai ya kawo dukiyan shi tunda na mahaifin su ne dukiyan shi duk.
Bakin su daya a lokacin mazan su da matan su don mahaifi su da mahaifin su ya bari a duniya a yadda sukace.
Duk wani abu daya faru gaba daya ya farune ta wanan dalilin don saida yakai sunga bayan mahaifin ku a lokacin ya tafi ya barni dake da cikin dan uwanki a jikina lokacin.
Kuka nake sosai tare da fadin umma kuma mahaifin su daya kikace kamar yadda nake gani a gidan nan da mukazo tace kwarai mahaifin su daya kuwa saidai sun sheganta mahaifin ku a cikkn yayan mahaifin su din .
Don ko wurin rabon gadon shi daya rasu din dan abinda za a raba yaya Nuhu tsaye yayi yace ba za a raba da mahaifin ku ba don shi din ba dan mahaifin ku bane da cikin shi uwarshi tazo aure gidan mahaifin su ai.
Da malamai sukace ba a haka ai sai suke cewa ai duk rabin dukiyan mahaifi su ya kare ne a wurin shi don haka ba za, a raba dashi ba abin har yakai alkali ya tashi daure shi don tijaran da yayi a kotu din.
Don shi wanan yaya Nuhu din haka yake da tijara dan duk a tasha yayi rayuwan shi gun shigowan su kaduna da zama.
Shiya kowa a cikkn yannuwan su yake kafa kafa dashi don sun taba wani rikici da maigidan nan soka mai yuka har aka kulleshi akace suna yara a lokacin.
Umma me i hate d man ma self before i see am wallahi na fada cikin kunan rai da takaicin jin wanan labarin nasa da nake ji yanzu.
Umma tace kada in soma in nuna hakan koda wasa a gaban kowa idan nayi hakkuri wata rana zan kamashi a hannu ne don Allah zai daukan muna fansa a gareshi.
Kwance makai ina hadiyan zuciya kowa yasan yadda bafulace yake wurin zuciya ina faman saka yadda shima zan halakashi da hannuna.
Umma ta fahinci me nake tunane sai naji tace min ranan da duk naji kin nuna masa wani hali a yanzu ranan zan bar maki garin nan in barku a cikin su ga baki daya daga ke har kaninki.
Jin hakan yasa nayi wani irin ajiyan zuciya mai karfi wasu hawayen suka kara zubo min ina tunanen ni yaya zanyi in ramawa mahaifina zaluntar shi da akayi.
A sannu yan gidab suke dan jan mu a jiki muna sabawa dasu duk da ba hausa a bakin mu sai dan turancin lagos da mukeyi da yarbanci.
Har kwana uku wanda ya kawo mu bai shigo gidan ba ko ya shigo ne dai bamu ganshi bane oho ?
Gashi wani lokaci sai naji na tsani wanan matar da akace ai mahaifin su daya da mahaifina idan na tuna da abinda sukai mashi a jikin shi.
Itama umma na kula ta dan sake jikinta a duk da ko yaushe tana daki bata dogon motsi a gidan baka ma gane cewa muna gidan da zama din daga can ciki muke zaune idan ba mun fito bane har wani ya ganmu.
Zancen karatun mu ya taso muka koma makaranta duk da yanayin karatun ba daya ba saidai munyi sa, a don karatun can yafi na nan da muka sama don haka mun samu an sakamu ajin da daddy yace a saka mu din.
Mun ake kaiwa da safe makaranta don muna riga manyan yaran gidan fita zuwa school don haka tare dasu Amira diyan hjy karima muke tafiya school din.
Da farko ba wani abinda ke hadamu da yaran sai yaran suka fara kawo muna rainin wayau suna kiran mu da wani suna da bamu fahinta ba.
Ranan na dawo na tambayi umma meye ma,anam kalman tace a ina naji nace da ita a bakin diyan hjy karima suke kiran mu da yan cin arziki.
Salati naga umma ta fara tace dole mu bar gidan nan don zaman mu a wanan gidan ba zai yuyu ba kan wanan matar da yayanta.
Nace umma ta barmu dasu don ko mun bar gidan nan cikin wahala zamu kara komawa kuma bamu san inda zamu dosa ba ai idan mun bar nan din.
Bayan kwana biyu da yin tambaya gun umma din sai ga yaran sun kara kiran mu da wanan sunan nace na your mama be dat .
Na kaiwa yar yarinyar duka tare rankwashe har muka dawo gida sai darzan kuka takeyi mota na tsayawa ta fita da gudu zuwa gidan ta rafka ihu uwar dake kwance tana barci ta fito a gigice ta na tambayan abinda ya sameta tace nice na doke ta ai kuwa nan fa tayo kaina ina shigowa ta tsare hanya a cikin sababi tana nunani da yatsa a cikin sababi.
Na kyaleta ina kokarin shigewa ciki ta hankadone baya nayi tangal tangal kamar zan fadi na ja na tsaya take na fulanin suka kawo min nace a hasale dont beat me again if not i will show u my true clour now , , , , ,
Ayi hakkuri nagaji sosai
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ANA DARA GA, , , , , , , , , , ,
2️⃣6️⃣
BY ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , ,
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AL MISAWWIR, , , , , , , , , ,
ONLINE PAID NOVEL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA NA FADA NA KUDINE NA FITAR DA HAKKIN RASHIN SANI ALLAH YA BAMU CIKAWA DA IMANI AMIN, , , , , ,
Baya nayi tangal tangal zan fadi Allah ya kareni na cire jakar dake goye a bayana na kalleta ina huci nace why u de push me like dat ?
I push you , why the you beat her ? you want to kill her or what ?
Me i no go kill any body, na ur daughter de abuse me, na yin i beat her , whu u no ask her wetin she do for me.
Wanan yar iskan mai suffan kafirai sai nayi maganin ki gidan nan zaki shiga taitayin ki dani wallahi.
Na ce me i no hear u ask ur daughter first wetin she for me daga bayana naji ana fadin hey daughter why do you beat her she is your sistee now.
Hjy karima tace can dai gasu gada Allah ya tsari diyana da hada jini da wa yan nan matsiyatan da aka kwaso muna a gida.
Haba dai hjy karima zaki raba tsakanin su ne suma din ai yan uwan sune na jini daya.