Showing 207001 words to 210000 words out of 382072 words
din zanje yanzu in samu daddy din.
Yana gadin haka ya mike tsaye ya fita zuwa part din daddy din yayi sallama ya shiga don hango daddu din da yayi zaune kasa yana waya hjy karima zaune a gefeb shi..
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ANA DARA GA , , , , , , , ,
6️⃣1️⃣BY, , , , , , , , , , , ,
ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , , , , , ,
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AL MAJID, , , , , , , , , ,
ONLINE PAID NOVEL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA BA TARE DA HAKKIN KOWA BA DON BIYA KI TURA DARI BIYAR 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK 08036959257
ALLAH SARKI AI RAINA BAYA BACI YANZU DON KIN FITAR DON NASAN AKWAI RANAN HADUWA SEE U👋👋👋👋
Karfe goma na dare muka fito don nema inda zamu kwana ga yunwa dake cin mu lokacin don ma munyi dabaran odan abinci aka kawo muna har inda muke banci abincin ba don inada matsala a rayuwana.
Bana cin kifi ko wani iri kuma bana zama a indama ake cinsa sai gashi anyi rashin sa, a sun kawo masu ferfesun kifi a cikin hadin haka yasa na dan fita daga waje don warin shi da aka bude yake son sani amai.
A inda na zauna bayan ginan nake jin ana kuskus waya akeyi da wani kan cewa ya tabbatar ya shigo cikin dare yayi yadda aka umurce shi dayi.
Fotowan da nayine ya ban dama samun lokacin don jin abinda suke shirin yi anyi yan wasu abubuwa a wurin.
Aikin ne damuka dan dakata ya kaimu dare gashi shawarma da dan ruwan lemu naci shine a cikina har daren.
Bello ne ya nema muna wurin kwana don gaskiya yana da kirki sosai ga kwazon aiki don ya iya computer sosai irin talent din nan ne shi.
Wanka nayi tare da alwala nayi sallah na dade zaune ina addua kafin nashafa na mika hannu na dauko wayana dana makala a canji na kira umma nayi masu bayanin ba zamu samu daman dawowa ba a ranan.
Addua tayi na Allah ya tsare ya kare na amsa da amin daga man na shiga duban sakon da aka turo min.
Sakon farko daga oga jimo ne yana min fatan nasara da godiya kan aikin da mukeyi ya samu labarin yadda aikin ke gudana.
Sai sako na biyu daga Faiza idan da sabo na saba da ganin sakon nita tana min fatan sake ganina a rayuwa a karshe tace kada nayi mamaki ganin ta lagos wurina wata rana.
Sai na uku sakone daga oga Sha,aban shima din fatan alheri ya turo min da godiya sai tambayan umma .
Dan murmushi na sake a fuskana don jin dadin wanan sakon kamarni mutum irin sha,aban zai tsaya ya turowa godiya irin haka ?
Nagaji daga inda nake ni kadai ina faman tunane don haka na mike zuwa bandaki na fito nayi adduan kwanciya nakai saman gadon.
Wasa wasa aikin da muke ganin na kwana biyu muka shigo yi sai gaya yakaimu har karshen mako a nan kano din sanam muka koma kaduna.
Yayi sallama ya shiga fallon ya samu wuri ya zauna yana sauren wayan da daddy din keyi akan rashin lafiyane har yana fadin a kaishi waje idan nan din ba su gane komai ba.
Daddy din ya gama waya ya juyo yana fadin kai duniyan nan wai Alh Bubane wanan aminin Alh Nuhu ya samu matsalan tashin lafiya da rana tsaka hannu ya rike mai.
Allah ya sauka ya bada lafiya ya fada kafin ya zamo yana gaida daddy din sunyi kafin yace nazone kan zancen Summay baby don a tuntubi gidan mijin aji in sun gama hada inda zasu sakata a kai kayanta can don kayan sun iso ko a yanzu.
Nan hjy karima ta fito daga uwar dakin Alh din datake ciki tana gyara sai taji abinda modibbo din kr fadi kafin daddy yace dashi kamar wasu irin kaya fa yana tambayan dan nasa.
Ya dan gyara yace kayan dakine nayo mata odan su kuma sun iso dama nayi hakane don kada kayan su jima suzo daidai bukin ya kusa.
Shine banda masaniyar hakan Abubakar bayan wancan kudin da tace ka basu a baya har kayan daki kuma ka hada mata ?
Zaune hjy karima takai don ta rigada ta gama magana akan wanda zata sayawa yarinyar har hakan ya hadasu fada da mijin nasu sai da ban baki aka shawo kanshi ya fara bada rabin kudin kayan.
Wayan shi yake duba don haka hankalin shi baikai ga kowa ba a cikin su balle yaga irin kallon junan da sukayiwa juna na zargin kin gani ko ko kuma don me zai mata haka a bangaren hjy karima din.
Wayan shi ya mikawa hjy karima dake zaune a gefen mijin ta yana fafdin ga kayan sunce kalla biyune milk da purple suka shigo dasu shine na zaba mata purple din kamar zaifi.
Wayan ta tsurawa ido tana kallon kayan da suka saka zuciyar ta kusan bugawa a lokacin yau yar tane da wanan kaya haka masu uban tsada.
Ta mikawa Alh wayan shima ya dade yana kallon kayan ya mikowa dan wayan shi ta fara din modibbo wanan irin dawainiya haka mai yawa ?
Ni zan koma dama abinda ya kawo ni ke nan ga takardun kayan sai idan an shirya aje da wanan idan za a kwaso yayi masu sai anjima ya fita ya barsu da mamakin shi.
Mommy aka kira koda tazo dan nata ya fita falon lokacin sai mijin da hjy ta sama zaune zugun zugun ta zauna a cikin tsarguwa tana fadin gani Alh.
Yace modibbo ne yazo da wani zance yanzu koya fada maki ta dago tana fadin zancen me Alh don ni bamuyi maganan komai dashi ba ya fita.
Takardun photunan gadon ya mika mata ta dago ta karba ta fara dubawa kafin ta dago kai ta kallo shi.
Modibbone ya sayawa kanwarshi kayan daki murmushin dadi mommy ta sake a daidai lokacin da ta dago don taga yanayin da fuskan mommy zai nuna a lokacin.
Mommy ke fadin amma ya kyauta haka akeso babba ya zama babba a wuri ya fara daukan girman shi ke nan a yanzu.
Nan suka dan taba zance irin haka kafin ta mike zuwa part din ta ta barsu a falon hjy karima tabita da kallo.
Yau na tashi ina son sawo abin bukatan mune na gida don haka na shirya tsab cikin doguwar riga mai tsaga har gwiwa sosai sai dan gyalen dana yafa a kaina dayasha gyara.
Nida Amar muka fita nake jan mu a motana dayasha wanki yana walkiya muka dauki hanyar cikin gari da zan iya cewa wanan ne karo na farko dana taba shiga gari da sunan wani bukatana.
Tafe muke mun sake kida dake tashi na yarbawa aikin Amarne wanan yawo kawai mukeyi don haka kawai muke dan shakatawa kuma na fitone don Amar din lokacin.
A daidai traffic muka tsaya magana nake a wayana hankalina yana saman traffic din dukda wayan dake kunnena a lokacin.
Hannu aka bamu na ja motan da sauri kamar ance in dago kaina in dan kalli gefe Almustaphana ya kura min idanu na kawar da sauri ina kallon hanyana.
Shi dine tabbas na gani don jikinane ya ban ana kallona na dan kallo wurin na ganshi a cikin wata mota fara.
Mamakine ya kama shi don zuciyar shi bai gaskanta mai abinda idon shi ya gane masa ba harko in kamane wanan kaman yayi yawa sosai wallahi.
Har motan ta wuce yana binta da kallon mamaki ta cikon glass yana fadin anya wanan ba sahiba bace kuwa ?
Inhar itane tun yaushe take garin nan ke nan har yakai gida cike da wanan tunanen a zuciyar shi dabara ya fado mai yaron shi ya kira ya bincika mashi har in itace ko tana lagos din tunda yasan gidan yasan kuma motana.
Wani shago muka shiga Amar ne zai zabi kaya a cikin sa shida kansa ya zabo abinda yake so muka juyo zuwa gida lokacin shidda na marance tayi ko.
A wajen gidan mu muka samu umma zaune tare da muniya suna hira a nan na tsaya sai Amar ne wanda ya shiga da kaya cikin gida lokaci.
Umma ke fada min yayan mu yazo bai samemu ba da sauri na juyo ina tambayan wani yayan namu a ciki tace Modibbo mana.
Na sauke ajiyan zuciya don a zatona shima mustapha din yasan gidan nan ke nan don ko sun sani ba zan je gidan kowa ba a cikin su na raya a raina.
Saida akai kiran sallah muka bar wurin zuwa ciki kowa ya shiga dakin shi don gabatar da sallah a lokacin.
Ban fito tunda na idar din ina daki ina aiki har dare yayi sosai kafin na fara jin haushin karnuka daga wajen mu can nisa kadan damu don ina jin haushin da dan nisa da mu.
A can kuma na dinga jin dan hayani kafin a fara kwankwasa muna kofan gida na taso da sauri na zura hijjab dina a jikona.
Falo muka hade da umma tace waye a cikin daren nan haka karfe ukun dare yake kwakwasa kofa a yanzu ?
Ba lafiya dai duk yadda akayi ta kara fada kofan na nufa da sauri umma ta tareni tana fadin waye daga ciki.
Bude mama ya fada da hankali nine Abdulhamid jin hakan yasa na bude kofan da sauri ina budewa suka fado cikin gidan mu shida iyalin shi baki daya lokaci guda.
Umma ta mayeastar da kofan da karfi ta rufe lokaci guda take tambayan shi meke faruwa ne wai ?
Yace ki saurara kiji tun dazun ake wanan ihun hakan daga bayan layin mu nace ina sauran yace baisan halin da suke ciki ba a gidajen su.
Mikewa nayi na nufi hanyar fita daga gidan da sauri suka tareni nace dole na dubasu ina fadin haka na fito shima ya biyoni a baya yana fadin su rufe gidan.
Wurin yemisi na nufa ita da take mace bugu daya ta kara zabura nace nine sahiba saita bude tayi kuka har ta godewa Allah.
Fitowa tayi ta rufe gidan jin cewa da nayi nice sahiba yasa su Adnan da felix dake tsaye a bayan mu bude kofan suma da sauri suka fito daga gidajen su nan sauran makwabta suka dinga fitowa daya bayan daya jin karan bude kofunan sauran gidaje da sukeji a lokacin.
An hadu wuri daya ana shawaran zuwa duba abin ko a kira yan sanda suzo nace me zai hana muje mu duba kada ku manta bamuji motsin masu gadi ba kuma ya kamata a duba halin da suke ciki su ma.
Kowa ya fara kallon dan uwa an rasa wanda zaiyi kundun balan zuwa ga karan abin kamar dabba yana ci gaba da kugi a cikin wahala sosai lokacin.
Kallon Abdul nayi ina fadin yakai yemisi gidan mu wurin su umma ya dawo da sauri suka wuce don duk a tsorace take lokacin.
Tafiya na fara yi ba tare da sun farga da hakan ba sai wajen kofan masu gadin get dakeda dan tazara da inda gidajen namu suke.
Kofan na bude saidai basu cikin daki ga takalman su nan a kofan da alama sun gudu ko an daukesune muka fara zargi .
Tambayan sunan su na fara yi aka ce Lukas da Barau suke ba wani tsoro a zuciyana ko fuskana sabanin sauran jama,an wurin da suke a firgice lokacin.
Hasken wayan dayan mutumin na karba na fara bin inda abin ke kuka na fara karanta addua a bakina ina tafiya zuwa wurin da kukan abin ke fitowa.
Innalillahi wa, inna alaihim raji,un wani mugun halittane a wajen kamar an masa tarko shi bai shigo compound din wurin ba kuma bai tafi tankar kafeshi akayi.
Dabba zan kira abin da suna ko dodo gaskiya idan na tsaya fada zan bata lokaci haka yake kamar kosassan karya amma yafi karya girma da abu najen kasa kamar nono a jere har kasa.
Bindin shi kawai yakai kaurin wani katon kare fuskan shi kamar hallitan alade amma a sabule zakace tsokane kawai baida fata ya wani irin walkiya na tashin hankali.
Mutum biyun da sukai karfin halin biyoni a baya sukai saurin juyawa da sauri acikin tashin hankali sukuma sauran na ganin su suka arta cikin compound din a guje har wasu na ihu.
Kowa yace a zamanin nan ba dodo ya tubawa Allah don har gobe akwai sauran halittan boye da Aljannu masu rikida su koma irin don tsafi.
Daga inda nake na fara fadin kayi ko kiyi gagawan komawa gun wanda ya turo ka daga yau kada ka kara dawowa aike a cikin garin nan har abada.
Kamar mai jiran a bashi umurni ya fara tafiya yana wani irin kugi da numfashi ya nausa yayi yamma ya bace a cikin duhun dare.
Saida suka kai basu ganni bane wasun su suka juyo dan dubani din a hanya muka gamu dasu ashe sauran makwabtan unguwar tamu duk suna tsatsaye cikin tashin hankali.
Washe gari kan ace kwabo labari ya karade ko ina a cikin gari ga wanda Allah ya nufa ya ji wanan labarin .
Kowa da fassaran abinda yake fada wasu suce ai dodo aka gani wasu kuma suce masu maita ko tsafine da suke rikida suka zama hakan suka fito yawon dare.
Rana ta baci masa ua kafe a wurin nikan tunda ba a fita office weekend ne barci nayi sosai ranan abina.
Sai daya na mike nayi wanka tare da alwala nayi sallah umma ne ta lekoni ina addua take fadin in fito naci abinci saidana shafa na saka kaya na fito daga dakin.
Na zauna na zuba abinci na fara ci ke nan mukaji anyi nocking din kofan gidan Amar ne ya amsa yake fadin waye yana bude kofan.
Ganin mai nocking din yasashi dan sake murmushi yana fadin wellcome broda tare da dan rusunawa kadan ya shigo da sallama rike da hannun Amar din ciki yana gaida umma.
Ta amsa mai da dan fara, a tare da tambayan shi iyalinshi ya amsa cikin jin dadin hakan kafin na dago ina gaidashi ya amsa min.
Ya su mommy da yara shima din ya amsa da lafiya kalau yana juyawa wurin Amar tare da tambayan shi ya yake yana zuwa makaranta ko ?
Ya amsa da eh mun fara zuwa a nan har an fara muna test kuma naci dukka, gaban shine ya fadi don kama da Amar a yanzu yayi da mahaifin mu sosai don duk zuwan da yakeyi wurin mu bai taba ganin wanan kamar namu da mahaifin mu ba irin yau.
Don gaskiya duk wanda yasan Abbah mu yasan duk muna kama da Abbah mu sosai saidai shida yake namijine yafi kama da Abbah din sosai.
Umma yanzu nake karantawa cewa wai jiya an samu dan matsala a wanan unguwar wani abin firgita ya ziyarci shiyan nan da fatan wanan matsalan bai shafeku ba dai.
Bai shafemu ba kuma bana zaton akwai wanda ya shafa a cikin wurin nan Allah ya kare kowa dake cikin nan wurin dama wasu makwabtan unguwar nan.
Saidai hakan ba karamin daga muna hankali yayi ba don gaba daya jinyan ba wanda yai barci da dadi saboda tashin hankali.
Idan wurin nan babu security daya dace gaskiya ya kamata a canza maku wuri kada sani abu yazo ya sameku a nan din.
Daga inda nake zaunen na sake kallo shi naji yaci gaba da fadin ina tsaron kada wani abu ya sameku ne umma don garin nan baida kyau yanzu kaduna ba kamar da can bane.
Ba abinda zai faru da yardan Allah don akwai hadin kai sosai a cikin wurin nan kada ka damu da hakan.
Kafin tace dashi wai da gaske ne zancen auren yar uwarka ko shirmen Faizace kawai irin da sukeyi ?
Kwarai mama zasu aurar da ita ga dan gidan uncle gyade yayan mommy, yaya gyade dai gyade dana sani zasu ba yarinya karama kamar wanan din.
Allah ya kyauta amma shi Alh ina nufin yaya mahaifin ku yasan wa yan nan mutanen kuma ya yarda ayi wanan hadin ?.
Eh yace min uwar ce ta nuna ita dai tunda yarta naso abashi ita har hakan yaso saka rikici a tsakanin su da farko.
Fuskana da hannayena ne kawai a wayan da nake tabawa din lokacin amma hankalina yana wurin zancen da sukeyi
Waye wanda zata aura ke nan don ba gama sanin yan uwan namu dama nayi ba tunda a boye muke a cikin su lokacin kamar