Showing 267001 words to 270000 words out of 382072 words
Wurin yayi tsit lokaci guda sai muryana da akeji in hada da turanci in hada masu da yarbanci na zamo masu yar daba ta asalin da suke jin labarin su a Getto.
Unbagarborn kai idan kasan kuya har zaka iya budan baki da sunan fada yau ka kallemu bayan mahaifin ku shine yayiwa mahaifin mu yanka na rago a wuyan shi a gaban yan uwanshi bayan sun sakashi saka hannu a kan kaddarorin shi.
Carb naji an rike min hannu ta baya nayi wani irin juyowa a kausashe ina shirin illanta maishi baffa hamza ne da ya Abubakar suka rike ni sai dai a lokacin har na fita hayacina ko lokaci guda.
Don Ina sun makara ihun dana sake don bacin rai saida duk tsikan jikin wanda ke wurin kuma dan asalin jinin ahalinmu ya tashi kowa yace babu Aljani a duniya karyane.
Ai kafin suyi haka nayi cikin taron nan na cakumo wuyan wanan dake maganan fitsaran babu wanda zaice ga yadda akayi na kai garshi a lokacin na shakoshi nayi wani irin girgizashi idanuwan shi suka firfito waje lokaci guda.
Duk mazan dake wurin taron nan sunyi sunyi su bambareni daga jikin shi sun kasa da kyat umma da yaya Abubakar suka iso gareni a cikin tashin hankali.
Shiya karbi wanan guy din a hannuna da kyar don kalama daya kawai daya fada a lokacin na sakeshi yanzu dai kun gani idan dabanci ko wani iskanci kuke ji tsohon ya fada rai bace.
Wanan da kuke gani a gaban ku ko ubanku ya taba ta yanzu ina yake yana can cikin wahala kukuma gaku kuna son tayar muna da zaune tsaye.
Daddy dake zaune yayi mutuwan wacin gadi ne ya nisa tare da mikewa zuwa inda nake sai kyarma nake ina jijiga a cikin wani irn tsuma yazo gabana yace.
Sahiba ki kalleni nine daddy ki bar zancen nan har a natsu ayishi hankali kwance zaifi don mun san kinsan komai harda abinda mu bamu sani a yanzu.
Kallon daddy din nayi cikin wani irin yanayi kafin na girgiza kai tare da kutawa ke da kingani kin san abin bana kai sake bane a lokacin.
Ai kafin a samu yaya Abubakar su fitar dani wurin tuni wur ya rikece da surutu kowa na fadin albarkacin bakin shi kan abinda na fada a lokacin.
Kamar wata gwauna suka rakani zuwa gidan gwaggo hari da umma tace can za a kaini don umma bata yarda a san inda muke ba ma,ana dasu kawai ta yarda yanzu ke nan.
Ranan kan gwaggo ta sheda irin abin dake kaina sai dare sosai na samu kaina nayi barci sosai gashi koda wasa ba wanda ya sheda masu ai iskane sai suka dauka duk turjin yan iskane kawai da jigalanci irin na yam dabam lagos dana koyo.
Saidai zancen cewa uban su yayiwa namu uban yanka irin na rago shi abinda ya dagawa kowa hanlali don haka yaran nasa suka shiga motan da suka ciko da sunan iskanci da turji a wurin suka koma cike da kunya da fargaban abinda sukaji din.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ANA DARA GA , , , , , , , ,
7️⃣9️⃣ BY, , , , , , , , , , , ,
ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , , , , , ,
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AL MAJID , , , , , , , , ,
ONLINE PAID NOVEL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA BA TARE DA HAKKIN KOWA BA DON BIYA KI TURA DARI BIYAR 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK 08036959257
ALLAH SARKI AI RAINA BAYA BACI YANZU DON KIN FITAR DON NASAN AKWAI RANAN HADUWA SEE U👋👋👋👋
Gaba dayan su sun taru a falon kowa sai mayar dana zuciyar shi yakeyi a fili iyayyen su mata sunyi zaune zugun zugun abin duniya ya damesu.
Ku lokacin data sheke hadi meyasa baku tarar wa yar iskaba kun nakasata muga karyan dabbancin nata Nazifa ta fada rai bace.
Ke wallahi na raba ki don duk yadda kike tsamani ta wuce nan wallahi ki dubafa mijin ki dasu baffa hamza bayadda basuyi su bambamare ta a jikinta ba amma sun kasa.
Shi kuma muna fuki dama ai haka yakeso dam iska da sauri mama Ammo uwargidan Alh Nuhu din ta kallo yar tasu tana fadin akul na karajim kin zagi mijin haka a gabana saina saba maki.
Kowa shiru yayi a falon yana kallon su don fadan da Ammo din kewa Nazifa ido rufe ts juya ga sauran yaran da kaf din su suna gida a lokacin in ka debe mutum uku dake aure wani gari a cikin su.
Dama nasan komai daren dadewa wanan ranan yana zuwa garemu don shi alkawarin Allah bai tashi abin bakin ciki da kunya ne a yanzu yake shirin tunkaran mu gidan nan kuna hauka baku sani ba.
Gaba daya kan yanzu sun mayar da hankalin su kan Ammo suna kallon ta da sauraren mai take shirin fada masu haka mara kyau da rashin dadin jine ?
Baiyanan ahalin Sambo a duniyan nan yafi komai muni garemu da baci gami da tonon asiri ku kun sani ta kalli sauran kishiyoyin nata.
Dama abinda nakewa Alh gudu ke nan a baya yace ina nafito ni ban isa in fada mai gaskiya ba kuma ba wanda ya isa to yau ha otin sa nan ya fara faruwa.
Da Allah zai nuna muna sai ya dawo da yarinyar nan da karfi karfi kuma na iko da fin karfin duk wani yanzu dake cikin Alhalin mu a raye.
Yanzu sai ku shirya fuskanta kyama da tsana da gori daga kowa bawai yan zuri,an mu kadai ba duk garin nan sai an nuna ku a matsayin yayan Alh nan gaba.
Tana kaiwa nan ta fashe da wani irin kuka tana fadin In Boni Hande da mike tabar falon da sauri suma kishiyoyin nata sai kuka sukeyi na tashin hankali.
Wa zai basu amsa a yanzu babu amaryan su ce bata kuka ba itama ido ta zubawa sauran tana sauraren su don koda aka aurota wanan case din ya mutu ta shigo gidan.
Umma Salma ce ta dan kallesu tace tun ina goyon kane Sanusi abin ya faru ai ya kamata ku gane me Addah Ammo ke fadi a yanzu don masu girma a cikin ku yaci su gane ko wanan gidan kanshi da muke zaune cikin shi a yanzu na wanene ?
Kwarai kuwa ummu salma na tuna gidan marigayi ne dan uwan Abba daya rasu baida kowa Abba yayi gyara muka tare a cikin sa hakane ya kalleta a zabure don tunawa da hakan.
Tace to ka tuna ke nan yanzu kowan sun dawo shi Addah Ammo ke son ku gane kuyi nazari a kan shi ai .
Wai yay buba wai a nufin wanan gidan da muke ciki a yanzu dama na chikas din nan ne ko me ?
Karfe bakwai nayi sallah na mike ina kallon umma nace umma mu tafi gida akwai aikin da zanyi a ma,aikatan mu don kaya zasu iso yau din nan su Adnan sun taso yanzu daga lagos zasu zo nan na fada a sanyayye.
Ai ki bari gwaggon naki ta fito kada taga munyi mata butulci jiya fa kusan kwana raye tayi a kanki shigowan hjy hari din ta ga yanayin mu kamar muna wani zance.
Take tambaya umma ke mata bayani cewa zan tafi gun aikine wai juyowa tayi ta kalleni tana fadin haba aiki saida lafiya akeyin shi ai ?
Ki bari sai ta kara samun lafiya ki fita ni kaina wallahi saida nasha magani da asuba din nan na samu mikewa haka balle ita da tayi wanan abin haka.
Yarbanci nayiwa umma na hari gadon dakin na kwanta rub da ciki suka bini da kallo kafin hjy hari din tace wallahi mairo idan nace dake jiya nayi barci a gidan nan karyane.
Abin nan da kuka fada min ya tsaya min a zuciya na kasa barci wai meye gaskiyan zancen nan don Allah.
Murmushi irin na takaici umma ta sake kafin tace gaskiyan ne kikaji hari a bakin mu shine kuma muka fada yanzu din.
Kuka ta sake a hankali tana toshe bakin ta tare da fadin yanka fa mairo yankan rago kayiwa dan uwa ka don dukiyan shi haba haba tana kuka take wanan zancen.
A gabana wallahi Allah ya nuna min lokacin da yaya Nuhu ke yankashi yana fadin idan kun kasheni ku kula min da iyalina don Allah sai naji muryan wani na fadin iyalin ma naka ba batin su zamuyi ba ai balle su kawo muna matsala kinji abinda yasa na bar gida ke nan lokacin da shigan cikin yaron nan naje nisa daku.
Kuka sukeyi sosai harni dake lafe saman gadon kamar nayi barci a lokacin umma taci gaba da fadin hari nasha wahala sosai a rayuwana har na haifi yaron nan shi kuma yanzo ba lafiya haka nayi ta fama dashi ko yanzu kika kalleshi kinsan Ammar ba lafiyeyye bane a ido .
Sai fa da Allah ya turo muna rai biyu rai biyun nan sune suka fara fitar da rayuwan mu kangin wahala sune dan wajen yaya Ali da dan wajen ki .
Kafin sahiba yanzu ta hadu da wani bawan Allah wanda ya daga darajan mu da kimarmu a rayuwa haka tana aiki a karkashin su.
Wallahi komai akace yaya Nuhu sunyi zai iya batan ki ko shekara ba ayi ba ya fara gyaran gidan ku ya tare da iyalin shi suka rabe komai naku iyasu kowa na kallo ba wanda zai iya furta komai akan haka har yaya Ali kuwa da ake ganin zai iya dashi lokacin.
Ance sunce koda kin dawo baki da wani gado don ya mace ke gareku da marigayi don haka suna hakkin cin arzikin dan uwan su yadda wasu ke fadan sunce fa.
Murmushin takaici umma ta sake lokaci guda tana fadin ai Allah yafi su yansan komai kuma yanzu da Allah ya dawo damu din sai muji me zasuce.
Gwaggo hari tace baki ga shi ya buhari jiya saida aka daga shi ba a wurin shiko yayya gyade fadi yake karyan bamza da wofi kawai a cikin kunya yana muzurai.
Nidai har barcin gaskiya ya daukeni suna zancen don maganan su kara tunzurani yakeyi a lokacin ina jin zan iya kashe kowan su dake da hannu a cikin kissan mahaifin mu din.
Barci na samu nayi sosai a lokacin a cikin barcin nake jin ana tayar dani wanda umma ke dan kiran sunana a hankali na samu na bude idanuwana da kyat lokaci guda.
Ki tashi gasu sun zo suna falon gidan wai mu zo alwai maganan da suke son yi damune kaina girgiza ina fadin umma barsu ba zamu kara zancen komai dasu ba sai an hadu a kotu.
Tunda na fahinci basu son sulhu ko girma da arziki akan zancen tashi zakiyi muje muji abinda suka zo muna dashi tunda su din sune magaba tan mu.
Dole na mike badon naso ba na fada ban dakin dake cikin daki fuskana na daurayo na fito kayan da umma ta tura Ammar ya dauko min a gida na saka.
Wani rigane dogo mai Short hannuwa sai filawan kwakwwa dake jikin rigan an masa ado daga cibiya kuma dan tattarane ya sauka kasa rigan yayi matukar karban jikina sosai.
Gwaggo Hari ce a gaba umma na bayan ta sai nida Amar dake biye a bayan su muka shigo falon wanan karo su kaman gomane suka zo ba a irin taron nan mai yawa sukazo ba.
Yadda naga su umma da gwaggo sun zauna sun zube a kasa yasa nima zubewa a kasan lokaci daya aka fara gaisawa a tsakani.
Kafin wanan tsohon na jiya ya fara magana mai kama da ban hakkuri ko nasiha kan a taushi zuciya kada abar abin kunya cikin duniya duk daya ake ayi duba kan lamarin banda bata suna.
Sam maganganun da yakeyi a lokacin basu shigeni ba yasa na mike kawai da niyar barin wurin lokaci guda umma tace dani ina zani na dan bata fuska ina fadin zan shigane ciki tunda mun gaisa dasu.
Kallona sukeyi ina tsaye kerere ba wani gyale ko hijjabi don ban saba da sakawa ba sai dan half sunna da nakan saka shima din yanzu ba ko yaushe ba.
Muryan daddy naji yana fadin na zauna a gama abinda ya kawo su suna son mu janye kara a sulhunta komai a gida .
Wanan ba zai yuyu ba na fada ido bushe gida zaku saka su yanke kawunan su kamar yadda suka yanka min mahaifina lokacin da yake rokon su.
Kada ki kawo muna zancen banza munan iyayyen kine a matsayin yan uwan uban ki mukazo wurin ku.
Wai wai wai kamar ya daba min mashe a zuciyana lokacin din abinda wanan ya fada tabe nayi da hannuwana ina kallon shi ido da ido nace.
Oh realy kai dan uwan mahaifinane ashe ai ban sani ba sai yanzu da kake fada amma lokacin da muke cikin wahala ban ganka kazo da zumar kwatar min hakkina ba a lokacin.
Masu girgiza kai suna girgiza masu budan baki sun bude don mamaki na kalli tsohon ina fadin look baba ka daina wanan sulhun da kake son yi a yanzu don hakan ba zai yuyu ba.
Gaba dayab su suna da hannu a cikin kissan mahaifina dakai baka sani ba amma zakaji a nan gaba don hakane suke kara nisanta mu dasu basu son mu rabe su basu son a nuna mu a matsayin diyan mahaifin mu balle duniya tasan muna raye.
Daddy dukar da kanshi yayi kasa yana dan murza hannayen shi don ya gane abinda nake nufi bayan baffa hamza ya gama fassarawa tsohon abinda na fada.
Kai naga ya kada ya nisa tare da fadin Allah ya kyauta sai kuma yace yanzun dai kuna da hujja akan hakan ke nan ko .?
Na gyada kai yace zancen baffah ki Nuhu da ake fadin kokuwan kine yasa yake kwance muna rokon a sassauta mashi idan hakane .
Ni ni ai ban masa komai ba a yanzu zagin mahaifina yayi muka dakatar dashi don yasan ba abinda zai iya babu babu .
Amma baffah kun ban mamaki da kuka zauna kuna kallon yadda yarinyar nan ke kokarin zuba muna rashin mutunci kuna zaune kuna kallon ta wai iska ko iskancin .
Kaita kanka tukunna kafan ka idan bakai hankali ba har abada ba zaka tashi ba shine ajalin ka shi zai kaika kamar yadda kuke kai mutane lahira.
Ka tuna shi kukaje kashewa a ranan kaida yaron ku dake kwance a yanzu an rasa meke damun shi akan fadan baki kukaso kasheshi a ranan.
Kaf na basu labarin shirin su a lokacin Ya Abubakar ya shigo falon shida su baffa Abdullahi kaf nabasu labarin komai dake aike daga bangarena.
Har kisan Abban mu da sukayi da rabon komai da sukayi iyasu da abinda suka tsorata daddy dashi a lokacin har ya karbi abinda suka bashi daga ciki.
Aradu yarinyar nan manyace baffa gyade ya fada lokaci guda kai kai ka daina fadin hakan a fuskanci abinda ke gaban mu yanzu tsohon ya fada.
Kai ina wanan yarinyar ta gama damu ta shuci rayuwan mu ke har kin isa ki muna wanan tonon silar idan da a bayane shan.
Kun dai yarda kun aikata ke nan baffa hamza ya tambaye shi a fusace yace in Nuhu yashe ya yarda ba idan bai sheba muma ba zamu sheba don ya fita sheri kun sani.
Daga bayan su baffah Buhari yace nikan na yarda na kumayi nadama kai Ali dcp ka sani ba yauba na fada maka komai ko a lokacin barazana da rayuwana sukai min kuma da kurciya a lokacin na fadama komai ai ?
Kallon daddy modibbo yayi yana fadin why daddy why ka aikata haka akan dan uwan ka sai yayi shiru don hawayen da yazo mashi a lokacin.
Kafin yace nasan komai daddy na sani tun lokacin dana dawo na samu kafita wanan zancen nake kwankwanto a kanka har yakai naje na bincika file din case din wanda mutanen kan sahibane suka fada min inda zan sameshi.
Ikom Allah dayan tsohon ya fada yana kara kallona yace wallahi tsoho su suka fada min inda zan dauko file din don wanan yarinyar da kuke gani ta wuce yadda kuke kallo ayanzu kan komai.
Wanan case ne daya shafi hukuma don haka dole abar yarinyar na akan karan da tayi baffa hamza ya fada idan munce a rufe wanan magana a gida haka dole dai zancen nan fita zaiyi waje ku sani.
Haka su masu bin hakkin su ai kunga bamu kyauta ba idan an kyalesu a haka ana kallonsu su kansu zasuga rashin adalcin mu a nan don haka wanan zancen bana gida bace bafa a yanzu.