Showing 261001 words to 264000 words out of 382072 words

Chapter 88 - ANA DARA COMPLT BY MAKAWA

MAKAWA   

29 Jun 2024

28409

na safe nace ya kaini airport.
Already Felix yayi min bucking din jirgi tun karfe bakwai na yammacin jiyan na godewa Allah don yan mintuka kadan suka rage jirgi ya tashi na iso.
Karfe sha biyu na shigarda kara da taimakon Bello ma,aikacin mu da yazo ya daukeni a airport mukai duk wani abinda zanyi ya juya dani ya kaini airport jirgin karfe biyu muka shiga lagos karfe hudu da rabi ina cikin gidan mu a zaune ba zakace na tafi kaduna a ranan na dawo ba.
Gaida umma nayi da gida don a shago na sameta na hausama zuwa part din mu wanka nayi na fito na tayar da sallah ban tsaya neman abinci ba nabi lafiyan gado na kwanta sai barci.
Baifi awa daya ba na falka don wayana dake gefena daketa ringing na mika hannu na dauka a jagule a cikin muryan barcin dake idona a lokacin.
Harshen yarbanci ya zaunu a bakina na dauka ina tambayan wake magana a cikin yarbanci saida gabana ya fadi lokacinn da naji muryan Daddy a kunne na.
Hausa yake min na nuna mai banji me yake fadi ba na kashe layina kai tsaye har wayan a lokaci guda ina jifa da wayan gefe daya.
Ido na mayar na lumshe da niyar barci sai kuma barcin ya gagareni don tunane ya rinjayi zuciyana a lokacin don babu abinda yazo min sai mamakin kiran da daddy yake min a wanan lokacin.
Shigowan umma dakin ne ya hanani ci gaba tana fadin Ngwa Sahiba yau ki tafi kadunane ko me ta miko min wayan tana mamaki tare da fadin yayan mune ke magana dani.
Na karbi wayan a hannun ta na kara a kunnena ina jin dan hayaniya a wurin koda yake min sallama don haka na gane cewa bashi kadai bane a wurin lokacin.
Mikewa nayi zaune da kyau ina karba mai sallaman sai gaisuwa daya biyo baya a lokacin kafin yace wani abin mamakine yaji don gasu nan the all family sun hadu ana neman iyayyen su a kotu ranan Monday .
Wai nice nake kalubalantar su akan dukiyan mahaifin mu shine daddy ya kira layina ban ganeshi ba an nema daga baya wayana akashe.
Sai Umma suka samu yanzu wai ya wanan zancen yake ne ko ina da masaniya nace idan munje kotu zamu hadu a can suji komai amsan dana bashi ke nan kawai a lokacin.
Kace ubanta dake kwance a cikin kasa koshi ya taso yayi kadan yace zai wullakantani naji muryan baffah Nuhu na fadin hakana sai dan hayaniya daya biyo baya a lokacin.
Recording din wayan na dana tun karbana haka yasa na sauke wani irin murmushi tare da fadin if he insult my father again i know how to handle him i swear will turne dat his folish mouth to his toes.
Alh wallahi ka daina don yarinyar nan da ji bata data ido kaji abinda take fada yanzu a cikin waya naji wani murya na fadin hakan ashe baffah hamza ne lokacin rike da wayan daya karba a hannun ya Abubakar din.
Ko uwarki mairo tazo nan bata isa ta tunkaremu haka ba hujja ba, , , , , subbahanallahi na fara ji a cikin wayan sama sama iya abinda zan iya karasawa ke nan a lokacin.
Ku kamashi mana kada yakai kasa subbahanallahi innalillahi kagani ba kunga abinda nake fadi wallahi yarinyar nan bata tun karo mu ba saida data shirya muna .
Duk sun manta wayan yana kunne ake ta wanan hayaniyar wasu na fadin ku kamashi a kaishi asibiti zaifi kada a barshi gida haka don Allah.
Dif umma dake sauraren su taji wayan ya mutu lokaci guda gidan baffa Amadu kanin mahaifin iyayyen mu kuma sai ya dauki salati da tashin hankali.
Hanklin kowa a tashe yake a lokacin dole asibiti aka nufa da Alh din fitowa magariba labarin komai ya isa kunnen yan uwa don a gaban kowa lamarin ya faru.
Bakin shi bude ya shiga common nan iyalin shi sukaji meke faru aka fara fada masu abinda ya faru baffa gyade yana fadi a cikin hasala
Saida baffa buhari yace kai gyade ka kama bakin ka wurin nan kada naka ya sameka yanzu kana fama da kafafun ka.
Shiru yaran sukayi suna sauraron abinda iyayywn nasu maza suke fadin wai wace yarinya wanan wanda ya kawo min hari ya juya masu a kaduna ya sake tambaya.
Baffa gyade yayi mai bayani yace kut wanan yarinyar shu,umace ta gaske yoooo ai shegiyace ta gaske don a shirye take da kowan ku nan ya nuna su da yatsa har yan uwanshi naji haushin shi.
Yace ni tsoho ya tura aiki kwanaki wurin ta yasin nayi wata daya ina ganin suranta a mafalkina duk na kwanta barci itace fa wanan, , ,
Kai ya isa haka don Allah bari muji da abinda ya damemu a yanzu yace alkur,an idan itace tsoho ya kara tabowa yanzu kuma sai kun lalubeta na rantse maku.
Idan kuma kun dauka wasane toh ku gwada ku gani aishi tsoho yasan ko ita waye don ya gwada duk sa,anshi a kanta karshe saida ta laishi makargama.
Aiko take wurin hayani ya fara tashi wasu na masa kallon mashayi wasu kuma kallon tababe ake mashi baffa hamzane ya ratso tsakiyan dakin yana fadin.
Yanzu kun daiji abinda yaron nan kalla,mu ya fada saboda haka a gwada don kallamu yafi mu sanin Alh da komai nasa kun sani.
Aiko a gwada din zaifi ya kara fada daga kofa shi kallamu din yana fadin wanan shegiyat kila a indiya take zuwa tsafin ta tunda bata tsoron kuna.
Mata gungun su daban mazan ma haka ga matasan diyan su a gefe daya suma suna nasu a daidai wanan lokacin da ake wanan maganan daddy da mommy suka shigo cikin dakin dake shake da yayan fulanin asali na kurnan kaya a can cikin jahar yola wanda suke surkukin daji daba kowa yasan dasu ba sai yan asali.
Daddy sun sama baffah hamza na fadin tsiyan abin yanzu ko an kira wayan bata dagawa idan ba wayan modibbo bane.
Meke faruwa daddy dake kallon yanayin Alh nuhu din dake kwance shirim saman gado baki bude ya juye ya koma gefe daya sai ya baka tausayi a lokacin don bai san wanda duk ke wurin ba sai numfashi da yakeyi sama sama a lokacin.
Yace kun dauka wanan ne dalilin ne yasa hakan faduwane kawai don damuwa da yai mashi yawa amma ai ita yarintane kawai ke cin ta harta furta hakan.
Wanan zancen da daddy yayi yasa suka dan lafa amma zagi kan ranan na shashi a wurin wa yanda suke dauka kazafi nayiwa iyayyen nasu a lokacin.
Duk yadda daddy ya kira layina kona umma a ranan muki dagawa har na dan nasu Abubakar din ba a daga ko daya kwatsam sai ga kiran dan hjy halira a wayan umma lokaci guda.
Nice na daga wayan a lokacin kwana biyu da faruwan hakan tsakanina da Alh nuhu da har lokacin yana kwance a yadda yake.
Ina sheda muryan shi na mikawa umma wayan tare da fada mata mai kiran ta din ta dauka suka gaisa da umma lafiya yake tambayana tace gani kusa.
Yacewa umma din mahaifiyar shice take magana da umma tace a cikin mamaki hjy hari yace ita gata zasuyi magana.
Muryan hjy hari din ne da sallama suka gaisa da umma akayi yaushe rabo don inaga har kuka saida tayi a lokacin kafin ta fara magana akan karan dana saka yan uwan ubana kan gadon mu.
Dan murmushi umma ta sake kafin tace wanan zancen sune da yarsu kinsan ita ta gado komai na kakanin ta itakeda karfin halin iya tunkaran su kan wanan a yanzu.
Hjy hari tace bazance kada ta nemi dukiyan su ba a yanzu amma komai nason sulhun gida kafin a kai ga hakan.
Naso nazo lagos din wurin ku kodan in ganku in saka ahalin yaya marigayi a idona wallahi Allah da ace nasan kuna raye da ba haka ba wallahi.
Don haka ku shirya ku zo nan kaduna duk ayita ta kare a zauna a sulhunta wanan zancen don magana ya gama karade garin nan kowa da irin abinda yake fadi akan zancen.
Zamu zo ai a cikin satin nan da za,a shiga kotu insha Allahu muna kaduna zanso idan kunzo na ganku kafin kowa don da abinda nake son mu tatauna daku.
In son samune zaku iya sauka a gidana idan babu takura kada ku zauna hotel ko wani wuri a,a ki barshi yarki nada gida a nan kaduna da muke zama a cikin sa bamu da matsalan wanan ko kadan.
Sunyi sallama an barta da mamaki ashe wai har kaduna din muna zama da sunan aiki amma duk basu da labarin hakan ?
A cikin satin sau daya nafita aiki ido yayi min yawa na canzawan da nayi sai kuma ga tafiyan kaduna ya riske mu haka muka shirya tafiyan yamma mukayi muka isa goma na dare don juye mun da akayi a abuja sai muka kara bin wani jirgi zuwa kadunan Belli ne yazo ya dauke mu zuwa gida a lokacin.
Ya Abubakar ne ya gano duk kwana biyun nan ina cikin kaduna don haka ya tunkaro gidan namu daya sani kai tsaye tundaga nisa ya hango wuta gidan a kunne alaman akwai mutum.a gidan lokacin .
Bai shiga ba ya juya zuwa yayi ya fadawa su baffah hamza da uncle Abdullahi sai gasu tare sunyi sallama muna zaune mun idar da sallah suka shigo.
Sau daya na daga kai na kallesu ban sake kallin inda suke suna gaisawa da umma ba sai kokarin shiga daki danayi a lokacin.
Ummace ta hanani take min yarbanci idanuwan su tar a kaina suna min kallon mamaki ina saye da dan t-shirt fari mai rubutun da manyan haruffa i wander why na kamfanin Nike sai dan bakin wandon jeans daya tsaya min iya idon kafa ya matseni kaina daure kawai da ribon da hulla mai raga .
Nima cikin harshen yarbanci nake fadin zan shiga cikine kawai aiba wurina sukazo ba don kiris ya rage a lokacin na sako hawaye a idona lokaci .
Kai haba hjy mairo baki koyawa diyan mu yareb mu ba sai yaren wasu kabilu can na daban baffa hamza ya fada yana kallona har lokacin a cikin mamaki.
Umma dai batace komai ba son fuskanta a daure yake lokacin sai naji baffh Abdullahi na fadin suna jin fulacin kila wanan yaren daine yafi karfi a harshen su don zama cikin su da sukeyi.
Ya Abubakar kuwa duk yana jin su baice komai don gaba daya na kula dashi baya cikin hayacin shi a lokacin sam.
Dan shirune ya biyo falon bayan na dawo na zauna din baffa Abdullahine ya fara magana yana fadin Mairo da farko zanso na kara maki gaisuwan rashin dan uwan mu kuma shakikin mu wanda bamu samu natsuwan maki ba tun a wancan lokacin mai tsawo daya wuce zuwa yanzu.
A hankali na dago kai na dan kalleshi kafin in mayar da kallona a wurin umma a lokacin da take fadin hakkurin namune ai duka Allah yayi mai rahama suka amsa da Amin.
Ya Sambo ya tafi ya huta saidai ya bar baya da kura akan dukiya munga abubuwa da dama mairo wanda har muka fara tuhumar ko hakan na daga cikin abinda yasaki barin gida dake da yarki a lokacin ?
Kafin umma tai wani magana Ammar ne ya fito daga dakin shi yana saye da wando three quarter na maza fari sai riga mai photon zaki a jikin shi light blue clour daya dauki jikin shi suka bishi da kallon a cikin mamaki.
Falin yayi shiru shima din dan kaduwa yayi da ganin su sai daya dan nuna razana a fili kafin ya gaidasu yana fadin good evening sir yayo inda nake zaune ya zauna a gefena rabin jikin shi na a jikina.
Ammar kuna garin nan baka kirani ba ashe sai lokacin ya kula da ya Abubakar din ya dan mike a cikin mamaki yana fadin broda welcome i no see u shaaa.
Suko mamakin kamar yaron da mahaifin mu ya hanasu ko motsi a lokacin sai can baffa Abdullahi ya nisa yana fadin ikon Allah kunga wani ikon ubangiji a nan wurin kuma ke nan ?
Bari kaidai ina ganin kamar gun wanan macen sai kuma shi wanan din yace ai ga inda kaman yake dashi sak.
Watau dai lamarin nan kawai saidai a barwa Allah ikon sa don zance ya kare a nan yanzu illa kawai yanzu mu tunkari baffa Amadu da wanan zancen.
Ammar din ya mike zuwa wurin ya Abubakar yana tambayan shi yaran shi sai baffa hamza ya ce kai ku tashi mu tafi sai gashi yana share hawaye daga fuskan shi dake zubo mashi yana fadin wanan alhakin dame zamu amsa shi gaban ubangiji.
Da kuka suka fita daga gidan mu dai muna zaune a inda suka barmu sai ammar ne yabisu suna rike dashi da yaya Abubakar din can ya dawo yana kulle gida yake fadin sun tafi ai tare da tambayan masu kukan nan suwaye su wai ?
Su baffane zaune a gaban kannen mahaifin su suna kuka wi wi wi kamar mata tare da fadin anyi sakaci baffa sakaci ba karami ba wanda na tabbatar da sai Allah ya tambaye kan hakan.
Ace diyan dan uwan mu suna raye haka a cikin duniya sun koma kabila zaka rantse baffa na diyan mu bane idan kagansu.
Zama tsohon ya gyara yana fadin to kai banda abinka Hamza a cikin kabilu fa uwarsu ta tayar dasu koda a nan arewane yau akace mace ce zata ba yaro tarbiya ba tare da mahaifi ba ya kuke tsamanin tarbiyan nan.
Hakane baffa ya gyara zama yana fadi tare dayin fifita da hularshi daya rike a hannun shi kafin ya kara gyara zama yana fadin kai jiya munga ikon Allah Baffa kamar yaron sak dana ubanshi har tafiyan nan na marigayi din.
Yanzu dai karfe biyu idan an fito daga sallah sai a hadu a nan din a fadawa kowa kamar yadda aka sabayi harsu din sai a fada masu.
Saidai kan yana da wuya ace sun amsa wanan kiran naku nake gani don gaba daya suna nuna kamar basu yarda damu bane ga baki daya mu nake gani.
Dole a yanzu su nuna hakan amma idan an fahinci juna komai zai koma yadda yake don haka a kara hakkuri baffa Amadu ya fada sukai mashi sallama suka tafi tun a mota suka fara waya suna gaiyatan yan uwa har mata wurin wanan haduwan.
Kamar yadda umma tayiwa hjy hari alkawari nice na tuna mata ta kirata tare da mata kwatancen inda muke sai gata da safen sun shigo da dan nata.
Ina daki kwance sai kulawa da kwancewa nakeyi wanda har lokacin ban gama tsara yadda nake so ba naji sallaman su har fitowan umma daga dakin ta.
Tayi masu sannu da zuwa bayan sun shigo sun zauna akai yaushe rabo da juna naji muryan Ammar daya fito yana gaidasu .
Kuka naji gwaggo hari din tanayi tare da wasu maganganu hakan yasa na fito daga daki a lokacin daidai kujeran dake saiti da inda zan shigo falon daga dakina na tsaya tare da dafa kujera ina gaidasu.
Naji tace zo gareni yata ku gafarce wanan duk sherin su yaya Nuhu ne kedai kin san komai dama mairo sai yanzu na kara yarda da cewan da akeyi suna da hannu a cikin kashe muna dan uwa dayawa mutane sun fadi hakan lokacin da sukaga ba a dauki lokaci ba an wawashe abinda ya bari kuma ba a nuna damuwa da bacewan ku ba.
Ba wani nuna damuwa da akayi a lokacin haka ana kallo bayan kowa yasan irin makircin su yaya nuhu har suka rabe dukiyan ku iyasu ba wanda ya iya masu magana duk da asanshi da iya salwantar da rayuwa ba wani aiki bane a wurin shi shi yanzu.
Kitchen na nufa don ban iya jin wanan zancen nasu bansan abinda yasa ba ko sau daya ni ban taba jin wani darrr akan shi ba yadda naga mutane na nunawa koda sunan shi sukaji.
Wai a cewan su ko sunan shi ka kira ka zageshi yana ji ko a wani garine kuwa don haka mutane suke yawan tsoron shi sosai.
Daga kitchen din ina jin abinda suke fadi a lokacin naji muryan gwaggo hari tana fadawa umma a cikin damuwa cewa ayi hakkuri tunda Allah ya dawo damu cikin su lafiya a janye wanan karan da yarinyar nan tayi a sulhunta komai a gidan kada daga baya hakan yazo ya jawo muna matsala wani abu yazo ya samemu kuma don halin su baida kyau har gobe zasu iyayin komai don dukiyasu.
A fusace na fito daga kitchen din na tsaya a inda zata


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login