Showing 195001 words to 198000 words out of 382072 words
ko yarda akwai wani abu a kaina sai wanan ranan tawa ta farko dana ziyarci company nan kai rayuwan nan ina zaki damune wai.
A yanzu yan Annabi a baki Fir,auna a zuciya sun fi yan son abi a zukatan su yawa don zaka ga mutum har mutum amma kada ka tona kaji aikin da yakeyi a bayan kasa.
Meyasa tsoron Allah yai karanci a wanan zamanin hakane har kafiran masu bautan wanin Allah suna sun sufi musulmi gaskiya.
Nace hakan ne don zamana a cikin su ina rayuwa sai kadan dinsu ne ke saka ransu ga abin wani idan kaji sunce dakai i swea to god iyakar gaskiyan ke nan suke fada lokacin.
Amma a yau sai dan musulmi ya rantse ma da Allah bisa kan karya koda kuwa yasan gaskiya yake karyatawa a kan karya saboda rudin duniyan nan ubangiji Allah kasa mufi karfin zuciyar mu Amin.
Don naga abinda basu zata ba a filin Allah saidai zan bisu a yadda suke son mu tafi din har mukai karshe dasu hakana.
Kaci nawani ka raya kanka da iyalan ka yaya kake zaton diyan ka da ka tayar a cikin haramun zasu kasance suma zakaga mutum yana kwalliya da haramun yana tunkaho a cikin ta kamar ba ranan haduwan mu da Allah.
A gajiye muka gama zaga ko ina muka dawo office din mu zaman mu ke nan saiga abin sha an kawo muna masu sanyi da cake.
Yemisi na zama take fadin duk ta gaji ta mika hannu zata dauki drinks din nace don't ta dago kai ta dan kalle ni kai na kara kada mata alaman a, a dai tayi saurin ajewa ta daga.
Sabbin abokan aikin nawa suka zuba muna ido don rashin fahintar abinda ke gudana a lokacin.
Harshe na juya da yarbanci ina fadin duk wanda zai sha ko yaci ya fita nisa da wanan wurin yasai duk abinda yake bukata don wanan din hanyar dauremune aka dauko haka.
God forbid ta fada tana fadin iam testing let me go and find something to drink .
We can go home now sai gobe don Allah kowa ya fito da wuri na fada na juya wurin wa yan nan mutum uku din ina fadin mun gode da lokacin su da suka bamu da fatan zasuyi hakkuri a cin ma manufar wanan aikin a tare dasu.
Tare muka fito zuwa haraban aje motocin company ina kallon yadda mutane sukayi gungu gungu suna gulman mu a lokacin kowa ya shiga motar shi muka nufi gidajen mu.
Da yake azahar tayi tun muna hanya muke jin kiran sallah a wurare don haka ina shiga gida gaisawa kawai mukayi da umma na shiga dakina nayi shirin sallah.
Na idar ban fito ba karatun alkur,ani na soma yi sosai cikin daga murya duk wanda ke gidan zai iya jina a lokacin.
Har lokacin la, asar yayi na mike nayi sallah na shafa na fito na samu umma zaune tare da maniya suna hira muka gaisa da ita take fadin ashe ba barci nakeyi ba don shi maigidan ta tun shigowan shi ya kwanta barci wai yau ya gaji da yawa yace.
Murmushi nayi ina fadin na dauka zai fitane zancen karatun yaran nan amma yanzu yamma tayi ni zan fita gobe kafin in shiga office mu nema masu inda ya dace dasu.
Abinci fa umma ta fada muniya tace bakici abinci ba tun lokacin da kuka dawo Sahiba ai ita wanan yemisi din nan gidan mu tazo ta karbi abinci taci.
Tausayi yemisin ta bani kamar ba ita ba yadda tayi laushi a yanzu tun zuwan mu nan arewan don itama taso tazo tare da mahaifiyar ta sai sukai shawara kan ta fara zuwa taga yanayin wurin ita.
Abincin na debo na dan fara ci a lokacin kuma muniya ta fita daga part din mu tsakuran abincin nayi na kai na aje a kitchen waje na fita don kallon yanayin sabon wurin namu.
A hankali nakai hannayena saman kirji na sauke ina lumshe ido tare da shakan iskan dake kadawa mai sanyi a lokacin.
Dan takawa nayi na jingina jikina kan dan adon da akaiwa kofan shiga gidan namu wanda kusan ko wani gida akwashi a wurin.
Bin gidajen wajen nayi da kallo sabon wurine da gani saboda ba mutane sosai a gidajen kusan ma mu din ne nake ganin farkon shi gidajen da aka gina su ko muzo na biyu don yaran dana hango dan nisa damu sun fito a cikin shirin islamiyan su lokacin sai kuma naga wani ya fito ya bude mota sun shiga .
A gabana sukazo suka wuce na dan bi yaran da kallo hakan yasa na nasa a raina cewa zan samu lokaci in masu magana game da karatun su Amar don yanzu yana secondry ne a matakin farko.
Na dade a wurin don har nakai ga kaiwa zaune ina nazarin wurin kafin magariba yayi in shiga ciki don sanyi ya kara saukowa sosai a lokacin.
Sallah nayi na samu wuri na kwanta kasa a falon ina tunanen mai gobe zai haifar garemu in Allah ya kaimu gaskiya karatu yana da dadi ga dan adam sai dai idan Allah bai nufi bawa da yinsa ba.
Da badon jajircewan da Allah ya nufeni da yinsa ba na dage har na cin ma wanan manufan da ko wace uwa take gurin ganin haka ga abinda ta haifa da muna can wullakace ina faman tallah da neman dakon abinda zumuci.
Rana na farko ke nan danaga aikin alherin da ya Abubakar yayi min a rayuwana don shi mutumin daya dorani a matakin farko tunda da har na dakatar da karatun nawa ne.
Koda ina da baiwan sani idan banda ilimi baiwan ba zai kaini ko ina ba a duniyan don komai da ilimi yake tafiya zamanin nan.
Na shirya a cikin buje da rigan aiki don in batar da sawu fula kawai na dunkule gashina na cusa a ciki ban saka dan hijjab dina ba da nake sawa iya wuya.
Zan shiga mota ke nan na hango wanan miji da mata din hausawan zasu fita ashe matar ma,aikaciyar asibiti ce ita mijin daine ban san a ina yake aiki ba shi.
Tattataki nayi zuwa inda suke suna ganin na doso wurin suka dan kuro min ido na karaso Ina masu sallama suka karba gaidasu nayi a cikin harshen turancin kafin na fara fadin.
Don Allah ina son su taimaka min ne da yaran mu ko inane keda makaranta maikyau da zamu iya saka yaran mu a ciki.
Nan dai nayi masu bayani sai matar ke fadin tana shiga mota ashe suna da yarama to ka taimaka masu mana idan zaka iya kai.
Yace ai kinji Allah ta hadamu dashi don me zaki taimaka masu tunda muna wuri daya zaune dasu bamu san inda zasu taimake ba ai.
Nan dai muka aje magana dashi zai dawo ya dauki yaran a kaisu ko za a dauke sun don yanzu second term ake ga karatu.
Yadda yai muna alkawari hakan ya cika don ya samu Abdulhamid sun kai yaran da takardan da muka karbo daga lagos nasu an saka su azuzuwan da suke can din ranan mun riga Abdulhamid zuwa wurin aiki kan wanan matsalan sai lokacin hankalina ya kwanta ganin Amar ba zaman banza zaiyi a kadunan ba shima.
Yau kan ma,aikatan ya cika da ma,aikatanta duk masu zaman banza a gida suna karban albashi a banza sai gasu sun fito aiki a ranan.
Tundaga get din nake kallon irin mutanen dake wajen har nakai motana inda zanyi parking na ajeta ban fito ba don wayan dana tsaya yi da Abdulhamid sai hakan ya dan bata min lokaci ga ido sun zubawa motan suga wanda zai fito a cikin taba.
Kafana fari sol daya sha takalma mai tsawon duduniya na fara sakowa kasa na tsaya ina dauko jakkar laptop dina dana aje a gefena.
Na fito ina gyara dan yalalon gyalen dana yafa a kaina iya wuyata a hankali na fara tako a cikin irin tafiyana maikama data tarwada .
Tafiya nakeyi ina gyaran gyalen dake zamomin saman kaina din ina dan gyarawa ga waya inayi a cikin harshen yarbanci a daidai wasu mata dake tsaye nayi sallama dashi.
Wai aikin banza wanan abarce tazo har aka rudamu haka ku fito ku fito wasu yan zafin kai diyan kwari aka turo yin bincike wanan kan Allah na tuba ai bata ishe mu komai ba wallahi.
Salamu Alaikum na fada a daidai lokacin dana dan wuce su ban tsaya ba kuma duk me suke fada kunne yake.
Au wai musulmace a hakan sai dayan tace yo aikin kin san haka suke su ba a gane musulmi a cikin su don duk shigarsu dayace ai.
Wurin da muka shirya zama nan nanufa na samesu a zaune suna duban tulin takardun dake gaban su.
Gaida kowa suka nuna min inda zan zauna nace su tashi daga wurin gaba daya ku dawo nan na nuna wurin da zamu zauna a barin dama saitin taga da yake haska wurin sosai.
Mun zauna mun fara aiki bamu jima ba kamar an turo da wani abu a cikin siling din wurin da muka tashi din wani ihu yemisi ta sake tana fadin jesus da karfi kowan mu ya mike tsaye a cikin tsoro suna bin wurin da kallo.
Allah ya ban ikon fadin innalillahi wa inna alaihim raji,un Allahuma ajirni fi masibati wa,akkalibli hairan min ha.
Auzu bikallamatilllah min sheri man halak may d evils of dis place back to his sender.
Ina fadin hakan na koma na zauna cikin ko in kula naci gaba da aikina saida nayi da gaske na samu suka samu natsuwa har suka zauna a tsorace baki sai addu,oin tsari nake karatowa a cikin sa.
Ganin yadda na sake jiki ina aikina yasa suka dan sake nasu jikin saidai a tsorace suke aiki a wurin wai suna tsoron aikin malam.
Wasu files na rike a hannu na guda uku kafin na dago ina fadin ina son ku gane cewa rayuwa mu a nan yana cikin hatsari sosai kuma kun sani.
Saidai alkawari muka dauka kan cewa zamuyi wanan aikin komai rintsin shi da zuciya daya don haka nake ganin duk wani aiki da zamuyi a nan sai idan mun hada kan mu wuri daya kamar yadda muka saba.
Files din hannuna na daga masu nake fadin duk abinda muke nema ya farone daga cikin wanan files din na hannu na don daga kanshi ne abubuwa suka rikece a wurin nan.
Na kalli sabbin abokan aikin mu suma tsarguwa sukayi da yanayina sai dana dan juya idanuna nace na dawo gareku.
Na zabo ku cikin mu don ku taimaka muna da wasu abubuwan da suka shige muna a dahu daga abinda zamu aiwatar a nan din.
Na yarda da gaskiyan ku da nagani a fuskokin ku lokacin dana shiga wurin taron ku yasa na aminta muyi wanan aikin tare daku a yanzu.
Zamu fara da wanan file din dake hannuna na daga masu wani tsohon file daya sha jiki ya fara tsufa komai da muke nema yana cikin nan na dan bubuga file din dake hannuna.
Sun dauka shi suka boye suka dauki wanda bashi ba a matsayin wanan din na hannuna don haka kada wanda yai masu zancen wancan din da suka boye.
Suka kada min kai alaman haka yayi daga haka nace dasu mu tashi da dan murmushi makale a fuskana na bar wurin don gano wani abinda nayi .
Wani girma suke ban na musan man badon komai ba sai don abu biyu na farko suna ganin cewa kamar nafi kusa da oga gabadaya.
Sai na biyu don baiwan da suka fahinta Allah ya ban na sanin abubuwan dasu basu sani ba idan na fada yakan zama gaskiya wani lokacin.
Sam ban kula a yadda muka fito daga office din ba don hankalina yana ga wayana da nake duban sako a lokacin.
Sun sakoni a gaba suna bina a baya kamar dai wata oganyar su a gaba saida na juyo naga a yadda muken ne naja na tsaya ina makain hakan.
Dole sai mun hada da yin hakan zasu saka shakun mu a zukatan su Adnan ya fada min acikin yare na kada mai kai.
Wurin motanna na nufa na bude na saka kayan a ciki suka tako min saida na bude na shiga suka shiga nasu motan saidai na dan dade ban tayar da motar ba kamar yadda nayi dana shigo wurin.
Caaaa akai min da ido sun zobo min ido suna kallon kowa da abinda yake fada kan zancen mu masu fadin ai gara da akazo bincike wasu na fadin me zasu gane su oga balane fa.
Karshe izza keyan su zasuyi su sallamesu da kudi su tafi basu gane komai bai ai indai su oga balane sun saba da irin wanan bincike haka bai basu tsoro.
Waya na tsayi da oga jimo na tura mai duk bayan aikin da muka yi ranan kafin in tada motana in bar haraban ma,aikata zuwa masaukin mu.
A daidai lokacin ne suka kalli junan su daga inda suke tsaye suna fadin lalaima yarinyar nan zata gane kurenta na shigowa hancin mu da kudundune da take shirin yi yanzu su oga bala ke nan da suka tsargu da shigowan mu a cikin company da sunan bincike a wurin su.
Tun dare yake kiran layin umma baya shiga ya gwada nawa sam bai zuwa shima don wayan a kashe yake idan zamuyi aiki.
Allah ya taimaka yanzu yana fitowa daga inda ya gama bincike ya lalubo wayan ya kara gwada kiran umma sai kiran ya shiga lokaci guda ya lumshe idon shi ya nufi motar shi ya shiga yana kara wayan a kunnen shi.
Bayan sun gaisa ne yake fadin yayi ta trying wayan baya zuwa sai yanzu ya samu tace Allah sarki kwana biyun nan wayan yana kashene ai dazun Ammar ya saka min ita a caji.
Baiji abinda take fada ba yasa ya dan dago ya kalli wayan location din da network ya bashi ne nata ya bashi mamaki don ya nuna a kaduna yake waya da maishi kaduna kuma ya fada a zuciyan shi.
Zan sake kira anjima yanzu ina saman hanyane idan na isa gida zan kiraku da dare akwai tambayan da nake son yi makine akan uncle marigayi.
Allah ya kaimu ta fada sukayi sallama ya kashe wayan ya kara dubawa still dai kaduna ya bashi ya kira kaduna how comes zai nuna mashi tana kaduna matar dake lagos ya fada a fili shi kadai a cikin motan.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ANA DARA GA , , , , , , , ,
5️⃣8️⃣ BY, , , , , , , , , , , ,
ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , , , , , ,
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AL WASSE,E, , , , , , , , , ,
ONLINE PAID NOVEL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA BA TARE DA HAKKIN KOWA BA DON BIYA KI TURA DARI BIYAR 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK 08036959257
Har yakai gida yana mamakin hakan a cikin zuciyar shi bayan ya parker motar ne yaja tsuki yana fadin shirmen banza ya fito ya shiga gida.
Falo ya samu Nazifa yau ba laifi tayi dan kwaliya da alama dai ta fitane ko tayi wasu baki mm a musanman a gida ya nasa a zuciyar shi.
Gaidashi tayi yayi da yaran suka shiga murnan ganin shi daga nisa ya dan daga masu hannu ya shige dakin shi ya barsu a wurin uwarce ta bushi da kallon mamaki mutum haka da riko har ga diyan shi abinda ya faru ne ya fado mata a rai lokaci daya.
Izuwa yanzu daya horasu din idan tayi tunane akan abinda ya jawo masu matsalan takan tuna da hudubar uwarta datace mata.
Wai Nazifa kinsan darajan mahaifiya kuwa kinsan yadda wa yanda suka dauki iyayyen su da muhinmanci sukeji yayin daka taba masu ahali.
Mutum ko dan banza ne akayiwa nasa wullakanci ya sani balle wanan da shawarashi da komai nasa yana a iyayyen shi.
Kinyi kokarin nisanta diyanncikin shi da jinin shi shi kuma ya nuna maki ya barki da yaran ki kuje kuyi tayi dasu akwai abinda yafi wanan zafi a wurin mace ace yau uban yaya ya yafe maka yayanka aiko da wasa ya furta maki hakan idan kina da wayau dole ki damu.
Tunda nayi sallah ina dakina ina nazarin wanan files din haka ya hanani fitowa don aikin da nakeyi a falo din sai sallah kawai yake tayar dani lokacin.
Ummace ta leko dakin tana fadin yau wani irin aiki kikeyi hakane ya dauke maki hankali kai na dago bayan na zana arrow kamar yadda nake saka sheda a wuri idan naga tambaya.
Ina murmushi nace umma da alama aikin mu yazo da sauki don wa yan nan