Showing 279001 words to 282000 words out of 382072 words
da yayi zafi a lokacin ya turani dakina in bata magani nima nasha maganin daga nan na tsaya na shimfide ta shine barci ya dan daukeni ganin shi yana ta faman rubutu a cikin littafin shi na siri yasa na zauna dakin kada mu dameshi don nasan inya gama zai nememu ai ko don yaji lafiyan yar shi.
Shine a cikin dan barcin daya daukeni na fara jin kamar kakarin shi na fito zuwa dakin shi da sauri a nan na samu sun gewayeshi su hudu Alh Nuhu ya dora mai yuka a wuya shi ya ganni sai dai su basu ganni ba da hannu yayi man nuni da in gudu.
A daidai lokacin da shi Nuhun ke fadin dama kai kadai ka rage bakin irin a cikin mu yanzu sauran basu dameni ba kawar dakai shine yafi a garemu ya fara yanka mashi yuka yana rokom shi idan kun kasheni ku kula da matana da yata da ciiii daga nan sai salatin shi naji da karfi alokacin na dauko yar muka fice ta kofan kitchen ta baya na nufi dakin maigadi don babu kowa a wajen .
Sai bayan na shiga ne na dinga ganin innuwan mutum a cikin duhu yana zirga zirga a wurin yana tsuki tare da fadin wai daga magana sun nemi wuri sun zauna.
Kuka ya hana umma karasawa shima lauyan komawa yayi ya zauna yana dan caka biron dake hannun shi saman takardan shi .
Alkali kuma sai faman rubuce rubuce yakeyi a nasa takardan lokacin kukana ya tsananta sosai yasa ban iya jin komai.
Hannun Ogan mune naji saman nawa yana fadin be strong ba a cin yaki da ragganci ki zama mai karfin zuciya ko yaushe da zafi amma ki daure.
Kai kawai na gyada a lokacin don ba zan iya fadan komai ba duk lokacin da ake bada wanan labarin nakaji wani iri a cikin kasan zuciyana nakan kwantanta irin zafi da radadin da mahaifin mu yaji a lokacin.
Muryan lauyan mune yake fadin ya alkali mai sharia zanso ganin buharin da ake zance a gaban kotu yanzu ya amsa min wasu tambayoyi kafin nan ga wanan mai sharia ya gani bayanin dashi marigayin yayine a cikin nan din.
Aka karba aka mikawa Alkalin ya gyara zaman glass din shi ya fara duba a hankali nan akai cigiyan buhari ya fito a gaban kanta ana neman shi.
Kowa ya bishi da kallo har ya karaso ya tsaya gaban su hayaniyane ya fara tashi lokaci guda a tsakanin su Alh nuhu da yan kallo da kyat alkalin ya samu ya saita mutane akai shiru lokaci guda.
Sai a lokacin na dago kai na kalli wanda ake kira da buharin nayi mai kallo na tsana da ki shima din yana da zubi hallita irin nasu saidai baikai su shekaru bane kawai shi.
Lauya ya fara magana Alh buhari ko ya amsa da eh yace sunan ka ya fito a sharian nan kusan sau biyu ke nan ko zaka fadawa kotu abinda ka sani game da abinda ake tuhuman yan uwan ka da aikatawa ga dayan dan uwan ku da Allah ya karbi rayuwan shi a baya.
Fuskan shi ya dan shafo kafin ya soma fadin eh to gaskiyan abinda na sani dai shine shi dan uwan namu ya dawo daga tafiye tafiyen da yakanyi a kasashen ketare .
Sai wanan kayon ya bukaci daya ganmu a nan bayan mu hadu a gidan mahaifin mu yake fada muna cewa wanan tafiya ya samu haske da yawa a cikin shi.
Nan ya bukaci da mukawo ya shawaran abinda zaiyi har muma mu karu da yaga ba wanda yai magana yake fada muna nasa kudirin a lokacin .
To sai abin baiyi tasiri a zukatan sauran yan uwan mu ba bayan mun bar wurin shine suka bukaci damu hadu muyi wani shawara a lokacin.
Lauya ya tareshi da fadin ku nawa ke nan fa yace iya mu yan dakin mune a lokacin amma kuma da mukazo taron sai naga Alh bello da Alh tanimu dinne ma suka tsara duk yadda za ayi a tunkar shi sambo din lokacin.
Kamar wani irin tunkara ke nan lauya ya tambayeshi yace eh to a gaskiya shawarane kan yaya shi da yake karami a cikin mu don mahaifin mu ya dauki nauyin karatun shi za ace yanzu shine zai juyamu.
Ma,ana ya fimi arziki inma arzikin ne aida kudin mahaifin mu yayishi tunda shanun da dukiyan mahaifin mu aka batar har ya samu ilimin nasa.
Don haka dole ya kawo dukiyan da yake ikirarin ya samu a kasa aba kowa nasa ko kuma muyi karan shi akwato muna hakkin mu.
Na basu shawara kan mu barshi da abinshi shi Allah ya zaba a cikin mu sun nuna min ba hakan ba nace to ba laifi nizan tafi.
Sai na manta da dan ledan dana shigo dashi wurin na dawo daukane na samu sun canza maganan shi Alh nuhu na fadin sai in halakashi in halaka banza ba zan sa ido ina kallon takaiciba hakana.
Nace kai haba dan uwankane fa ina laifi dai kuyi mai maganan da kukace zakuyi zaifi nabar wurin hankalina bai kwanta ba na samu yayan mu Ali dcp da zancen sai cewa yayi in barsu suyi mai magana ai sambo dukiyan nasane abin tambaya.
Nikan lokacin dana bar wuri Ali dcp ina mamaki saina nufi wurin sambo din na fada mai komai dake faruwa akan ya dauke iyalin shi yaje wani wajen.
Sai ya nuna min in yan uwan shi na haihuwa sunkishi ina zai tafi ke nan da yamma sai naga yazo wurin nuhu da yake lokacin duk gidan muna gado muke bandashi daya sai gidan kanshi bai zauna a ciki ba.
Nan suka dade da nuhu suna magana kafin ya fito ya tafi ranshi a bace daga inda Alh nuhu yake tsaye yace munafuki dama nadade ina zargin ka a raina.
Murmushi yayi yaci gaba da ba kotu labarin dashi ya sani Alkali yana rubutawa har aka sallamishi aka dawo kan wanan dan littafin da akai rubutu akai.
Inda mahaifinamu ya rubuta idab na mutu a tuhumi nuhu gyade da Ali dcp aminina donshi yasan sirina ya fadawa nuhu komai.
Ga inda ya tsara kaddarorin da yake dashi an karanta kowa yaji nan dai Alkali yace aje a rufe su Alh har haduwa na gaba kan zargin da ake masu din na kisan dan uwan su a shekarun daya gabata a baya.
Kotu ta tashi na dade zaune ban motsa ba a inda nake ina jin wani iri a zuciyana kafin can in dago kaina.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ANA DARA GA , , , , , , , ,
8️⃣3️⃣ BY, , , , , , , , , , , ,
ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , , , , , ,
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AL QADIR, , , , , , , , ,
ONLINE PAID NOVEL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA BA TARE DA HAKKIN KOWA BA DON BIYA KI TURA DARI BIYAR 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK 08036959257
ALLAH SARKI AI RAINA BAYA BACI YANZU DON KIN FITAR DON NASAN AKWAI RANAN HADUWA SEE U👋👋👋👋
Kowani bangare ka kalla fuskan su babu dadi ko kadan gashi ranan sun fito kwansu da kwarkwatan su anzo kotun .
Don Alh nuhu daya fada masu ranan ne za, akai karshen sharian sai mun kwashi kunyar mu a hannu mun gane kuren mu a wurin shi.
Sai gashi ranan reshe ya juye da mujiya shari,a ya hau kansu yanzu nayin kisa da salwantar da dukiyan marayu da sukayi a tsakanin su.
Saidai daddy da kotu ta nema ance bai kasan yana waje amma harshi baffa buhari an rufeshi ranan don shima za a tuhumeshi kamar yadda shari,a ya tanada.
Mutanene gun gun haraban kotu din kowa na mayar da zance akan sharian na yau kusan mune na karshen fitowa daga cikin kotun yayin da aka zubo muna idanuwan tausayi wasu kuma na tsana.
Kasancewan da oga Shaaban a wurin sai ma aikatan mu suka koma bayan mu suka sakomu a gaba hakan ya kara sa mutanen wajen mayar da hankulan su a kan mu.
Har lokacin kuka nakeyi sosai gwoggo hari da danta da mijintane suka haro inda muke din sukazo wajen mu gaisawa aka farayi dasu kafin tace Sahiba kibar wanan kukan in Allah yaso gaskiya ta fara halinta kowa ya sheda hakan a nan yanzu.
Yaya Abubakar ne ya karaso wurin kallo daya zakai mai ka gane baya cikin hankalin shi suna magana da mijin gwaggo hari din da mustapha.
Ogane dake gefe yana waya ya taka zuwa inda suke shida Ammar da zuwansu Ammar ya nuna ya Abubakar din yana fadin dis our big brother and his like a father to us now .
And dis our uncle too and his wife sai ya riko hannun ya mustapha yana fadin dis too is carryin with us too he means alot to us.
Kallon ya Abubakar din da uncle din yayi kafin ya kai kasa yana masu gaisuwan sarakuta tare da fadin yaji dadin daya gana dasu yana neman auren yarsu Sahiba a wajen su idan ba damuwa.
Duk wanda ke wajen kallo ya koma a kansu lokacin yasa da sauri ya Abubakar ya dago shi yana fadin wanan zancen banayi bane a wajen nan sai anje gida an zauna tare da sauran iyayyena zaizo.
Adnan ne yake nuna min ogan namu lokacin da yake tsugunne na juya da sauri tare da mamakin ganin hakan a garesu a yadda na sanshi babban mutum dai.
Dariya aka kwashe dashi lokaci guda naga Abban ya mustapha yana dan bubuga mai baya ban san abinda suke fada ba a lokacin.
Sai dai duka fuskan yan uwan nawa biyu a lokacin baida dadin kallo bayan dan zancen da sukayi a tsakani ya juyo zuwa wurin mu fuska a sake ya umurcesu da su kawo motoci mu wuce zuwa airport daga nan.
Takawa mukayi inda su ya Abubakar dasu baffa hamza suke tsaye suna hira wanda bai wuce akan oga mu ko sharian suke magaba ba lokacin.
Gaisawa mukayi dasu kafin muryan ita gwaggo hari tace ke yata ashe tafe kike muna da suriki yau yanzu yake gabatar da kanshi a garemu ai.
Da mamaki nake kallon ta don ban gane abinda take magana a kanshi ba lokacin wanan ai shirmen banzane mutane na cikin wanan tashin hankalin zai wani zo ya gabatar da kanshi wai a matsayinshi na wanda ke son ya auren Sahiba.
Mahaifin shi ne da baffa hamza suka idan ya gabatar da kanshi garemu yanzu laifine yaushe zamu kara ganin shi ne wai ?
Tunkan mahaifin nasa ya rufe baki ya juya ya bar wurin mahaifiyarsa ta bishi da kallo kafin ta juyo tana kallon mu dan dariyan yake tayi a fuskan ta kafin tace damu yau din zaku koma ke nan ?
Umma tace yanzun kuwa daga nan sai airport zamu tafi jirgi karfe biyar na yamma zai tashi wai mukai sallama zamu tafi umma ta kira ya Abubakar sun dan jima suna magana kafin ta juyo muka tafi.
A cikin motan da mukazo da ita muka koma don mun samu duk sun shiga motocin su saidai ba wanda ya iya maganan komai a cikin mu lokacin har muka kai airport din.
Nan ma ba bata lokaci muka kama hanyar lagos don dama lokacin tashi ya kusa har muka isa gida lafiya ina jin wani zazzabi ya rufeni tun a cikin jirgi da kyar na samu nakai kaina gida a lokacin ban tsaya komai ba sai kwanciya a yadda nake jin kai .
Duk yadda suke shiga tashin hankali a gidan wanan yafi daga masu hankali sosai don gaba daya gidan ya rikice da kukane lokaci guda.
Yadda makwabta suka saba shigo masu idan wani abu ya faru dasu sai yau din babu kowa daya shigo masu gidan a ranan.
Cikin manyan mazan diyan shine suka shigo a lokacin suma kallo daya zakai masu kaga bacin rai fuskokin su don rayukan su babu dadi ko kadan lokacin.
Sun zauna ana masu sannu sai daya daga cikin matan ke tambaya kun gane inda aka kaisu kuwa ko har yanzu ?
Mun gano da kyar mama saidai ba a bari a gansune don wuri mai tsanani aka kaisu don laifin da ake zargin su dashi din mai karfine sosai.
Kukane kuma ya dawo masu sabo kowa na fadin abinda yazo mashi a baki a lokacin dayan matasan ne ya yanka wani ashar sai Addah wuro take ce mashi.
Na fada maku ku daina zagi don mahaifin ku shine da laifin komai ninasan abinda ku baku sani ba akan wanan maganan.
Tunfa ba ai wata biyu ba Alh ya rabe kayan Sambo sambo mutum mai kirki mai zumuci kaf a cikin yan uwanshi amma suka dauki karan tsana suka samashi a dalilin mahaifan su kawai.
Ina laifin wanda ya samu yace kazo kuci da wani dan uwane ai bazai ko tuna dasu ya jawosu a jiki ba amma shi duk lokacin daya sauka kasan nan kowa sai ya sani dangi kaf kuwa don zaibisu daga daga yana sauke masu alheri a gida.
Kukun sani basai na fadi komai ba ta nuna kishiyoyin nata dake zaine sukace kwarai kuwa kayan sallah mu dana yara a lokavin duk shine ke muna tun baiyi aure ba kuwa.
Ko a lokacin da ace yabi ta Alh wallahi ba zai muna wanan din ba kuma bamu ba gaba dayan mu yan uwa hakan yake masu wanan alherin amma wai ace yau su Alh ne sanadin barin bawan Allah nan duniya duk wanan alherin da yake binsu dashi kan abin duniya kawai.
Addah wuro ki daina fada don Allah don aikin gama yariga daya faru wanan babban dan ya fada ni ba komai nake jiwa ba a yanzu sai kaddarorin Abba da kaf za a kwace a mayarwa masu dukiya da abinsu ne abin ji ai.
Kai kuma yaya ka fara zancen ka ke nan a kan me za a kwace dukiyan duka saidai a basu nasu a bar mashi nasa ai.
Mekega Alh din dama hjy salma ta fada tana kallon su tace ai zancen gaskiyane ya fada shiyasani idan zai tuna ko wancan gidan da muka fara zama a cikin sa na waye gadon shi sambo dinne ai da aka raba tunda su sun sayar da nasu a lokacin sun raba kudin da sunan zasu ja jari dashi ya karye.
Kowa yayi shiru yana tunane wayan Nazifane yayi kara a lokacin ta dauka tana jan suki da muryan ta daya dushe don kuka tana fadin muna gidane mana har yanzu.
Can kuma tace sai mun gama zan dawo mana bana fadama ina gida har yanzu ta kashe wayan tana jan tsuki kajiki da wani shirme ke kuma.
Wani dan uwanta ya fada daga cikin su mutumin da tun dazun muna tare dashi wurin neman inda aka kai su Abba a dalilun shine fa har muka gano inda suke.
Dayan yace balle idan akace yau bawan Allah nan baiyi kuka ba da wuya wallahi yadda hankalin shi yake a tashe din nan koda muka rabu yace zazzabi ma yake ji sosai.
Toki tashi kije gida kinji mijin ki ba lafiya uwarta ta fada idan kin zauna nan din me zakiyiwa mutane tunda ba wani abin kukeyi a nan ba gobema aisai ya barta tazo a cikin dadin rai amaryan gidan nasu ta fada karshe.
Badon taso ba tamike zuwa gida haka ta isa gidan ranta a bace ta samu babu kowa a falin part din ta ta nufa ta shiga ta yada jakar hannun ta saman kujera.
Kayan jikinta ta fara cirewa don tasha iska ta kafin kuma ta fara kwalawa mai aikinta dake dakinta da yaranta kira ta kawo mata abinci.
Bayan ta kawone ta aje mata ta koma ta dauko ruwa lokacin ta samu ta fito daga bandaki tayi mata sannu da zuwa.
Yauwa don Allah ki koma ki dauko min wani drink don ban faye son wanan din ba zata dauka sai kuma tace ki barshi mana ki dauko min wani.
Ba,a jima ba sai gata ta dawo mata dauke da wani da kuma wani leda a hannun ta tana fadin hjy wanan baban su maryam ya dawo dashi dazun da zaishigo ya bani.
Ok meye a ciki ta tambaya nuna mata tayi bata bude ba bayan ta bude ta dibi rabonta don tasan ba zata samu ba idan uwar dakin ta dawo ta amsa a hannun ta.
Sun dan taba hira a tsakanin su tana tambayan ta yaran idan basuyi fitina ba dan bata nan tace sun dan taba sai kallon uwar dakin nata takeyi yadda take hankada abinci a cikin ta kamar ba gidan su tafito ba har dare haka.
Nan dai suka zauna harta kare abincin tas ta mike ta kwashe kayan tare da mata saida safe ta tafi tana mamakin hali irin nata ko yaranta