Showing 87001 words to 90000 words out of 382072 words
Hannu ta daga tana fadin hjy ya isa haka ni dai na fadi a daina hada min diya da kalan dagi idan kuma ta kara dukan min ya sai nayi mata bugun a kawo ruwa a gidan in rama mata.
Na nuna kai na tare da daga hannu na nayi round dashi na kada ina fadin god forbid wallahi omale,
every day she de call us with cin arziki walahi talayi if she repeat dat neme for us again i go break dat her tieni leg before we come back.
Sam ban kula da kowa na gidan yana waje a lokacin sun fito ba gaba dayan su sai umman mu data sha magani take barcine bata san da hakan ba.
Sahiba naji muryan ya Abubakar ya fada a tsawace yasa na dan dago na kalli inda yake tsaye shida daddy din suna sauraren mu nace .
Nace broda na dis woman come push me for notin, nd she is abusue me, bcos her daughter de call us wit cin arzki, nayim i beat her, she come dey cry, her mama come dey block de road for, i come de inter nayin de woman push me back,
Karima ba yarinyar nan hanya ta wuce daddy ya fada yana kallon ta ido da ido tace au kama mara mata baya ke nan tayi iskancin data koyo acen ke nan ?
Bata hanya ta wuce nace dake ko kuwa ta wani irin jan hannun yar ta suka shige tana fadin wallahi da sake don ba zan yarda da wanan iskancin ba.
Juyawa nayi wurin daddy na dan rusuna nace tank u uncle ya daga hannu yana fadin dont faith next time nace yes sir nashige ciki Amar ma yabi bayana.
Kai ya Abubakar ya girgiza yana fadin wanan baku san ko waye ita ba a wurin dabamci da kowa ya kama kanshi da ita a gidan nan .
Yarinyar da gaba daya lagos kaf tasan shi sai ta zagaye shi da kafa fada a wurin ta kamar shan ruwa ne ita.
Daddy daya juya yake fadin dole tayi tarbiya sai namiji duk kokarin uwar ba zata iya bata tarbiyan da namiji zai iya bata ba ai.
Da sannu da lalami zata koya a nan insha Allahu wata rana hakan zai zama tarihi a gareta sai ka fara shirin koyar da ita hakan a yanzu.
Hjy Addah kan mutuwan tsaye tayi a wurin tana kallon ikon Allah ga yar dan uwanta dake tujara haka a gaban kowa duk dani ina ganin ai nayi masu mutunci tunda na tsaya nayi warning din ta ban makale mata a jiki ba.
Mun shiga mun samu umma a kwance falo muka tsaya na debe uniform din dake jikina wando da riga sai dan hijab din da ya zama mun alkakai don debeshi nakeyi idan mun fita tunda ban saba saka hijjab in dade haka ba sai idan zanyi sallah nake sakawa .
Abinci na zubawa Amar ya zauna yana ci sai ga Amira ta shigo dakin namu da takardan ta a hannu tana assigment din da aka basu.
Kwanciya yarinyar tayi a kasa ties ta kifa ciki ba wanda yai mata magana a cikin mu har lokacin nima dai a karshe hankalina sai ya dauku ga tunanen kalman da hjy karima ta fada game da mu da zata shiga gida.
A fuskana yarinyar ta manna min littafin nata tana inyi mata in koya mata mana sai yarinyat ta ban tausayi na shiga koya mata tana ganewa.
Nemanta akeyi a cikin gida ta ko ina duk uwar ta tayarwa mutane da hankali daddy da ya Abubakar dake alwala a waje har baya sukaje wurin tankin ruwa aka duba ciki babu yarinyar uwar ta kara tayar da hankalinta sosai.
Daga karshe sai ga yarta ta bude kofan mu ta gamu zaune tare muna cin abinci gs littafi a gefen mu muna assignment din a ciki.
Juyawa tayi ta koma da gudu ta na fadin mami ga Amira can daki ita da yan cin arziki suna cin abinci ana mata assignment din ta a cikin zabura uwar tace ina ?
Daddy yaja wani irin tsoki yana fadin shirmen banza shirmen wofi kinbi kin tayarwa mutane da hankali haka kince kin duba cikin gida ko ina.
Har ya juya zai bar wurin ya juyo tare da kiran sunan yarinyar da humaira idan naji kin sake kiran yaran nan da yancin arziki a gidan nan sai na bata maki rai.
Arzikin da uwarki ke fadin anzo ci a wurin ubanwa na same shi kije ki tambaya wanda duk ya fada maki da kikirasu da hakan ni ubanki nace arzikin su nake ci har ku a gidan nan yanzu.
Wurin gaba daya yayi tsit kowa na kallon daddy din da mamaki jin abinda ya fada tundai ita hjy karima din daddy yaci gaba da fadin.
Da arzkin uban su na samu aikin da nayi a baya da nasa kuma har na fara business din da nakeyi yanzu don haka ke dasu fada min waye dan cin arziki a cikin ku yanzu ?
Don haka wa yan nan yaran sun wuce a raina su a gidan nan musan maku da mahaifin ku ya daukeku kamar diyan cikin shi da ya haifa son yai min duk wani abu da dan uwa zaiwa dan uwan sa a rayuwa ke Addah kin sani idan su basu sani ba ai.
Don haka ku girmamin yaya don ko shi ke raye na barku haka zai muka baku maraici da rashina a duniyan nan nasani.
Daga haka suka bar wurin zuwa sallah ya Abubakar ya bin shi a baya zuwa masalaci unguwar da suke sallah.
Jikin kowa yayi sanyi haka suka kwasa suka koma cikin gida kowa da zancen daya tsaya mai a zuciya shi suka shige part din su.
A part din hjy Addah Nabila ce ke fadin yau wanan yarinyar ta mun daidai jifa yadda tayiwa anty a gidan nan.
Sauran ma suka dauka da hakan muma ai tayi bala,in ban mamaki ke bakiji abinda yaya ya fada ba cewa yar geto ce ita ta iya dabanci kamar tsiya.
Hjy ce daga kofa take fadin meye abin burgewa ga yiwa babba rashin kunya irin wanan amma mommy ai ita akan gaskiya ta fadi magana ba tsoro dole anty ta koma baya tayi shiru.
Ina zata iya da wanan yar tsatsaye take fa dagani saura kiris ta iya sheke koma waye ya taba ta .
Wai mami mai daddy ke nufi da cewan da yayi yaran nan suke da arziki hjy ta juya tana fadin kya iya zuwa kin tambayeshi a waje .
Tafice ta barsu suna magana a kai kona fadin abinda ya fahinta kan zancen mahaifin nasu har suka gaji suka watse zuwa sallah.
A dakin mu bayan mun gama umma tace muyi sallah la,asar yayi na idar na fito na samu Amira din tayi barci daykata nayi na dora saman kujera saboda sanyin ties na kwanta a kasa din ni sai barci.
Anty ta shigo dakin da kanta ta duba don jin yarinyar shiru da tayi ta samu munyi barci sallaman ta da umma taji yasa ta ta fito falon daga ciki uwar daka tana amsa mata.
Wanan nazo duba ta nuna yar nata a cikin murmushi umma ke fadin tayi barci sun gama karatu da yar uwan barci kuma ya dauke su zata dauketa umma tace aiki barta idan ta falka sai a kawo ta.
Anty din bata so hakan ba son bala,in haushin mu da take ji a lokacin ta juya ta tafi bata ce komai ba umma ta tsaya tana kallon ta cikin mamaki.
Kafin ta juya zuwa cikin dakin sai gab da magariba ne muka falka wanka nayi wa yarinyar nima nayi na shafa mata mai sai na riko hannun ta zuwa part din su duk ban taba shiga part din kowa a gidan ba.
Don mun kasa sake jiki da kowa damama ni shi Amar ko banza haka yake baida sakewa ko kadan da mutane kullun yana daki ne.
Nayi sallama tare da fadin gata nan barci tayi a aurin taje yin assignment a lokacin ina fadan haka na juya na bar part din na dawo namu.
A ranan daddy sunyi fada sosai da anty a kan mu tace wai ya kunyatata a gaban iyalin shi yace a kan yaran nan idan kince zaki matsa masu a gidan nan zan iya maki abinda yafi wanan din ma nan sukai ta musayan yawu dashi har ya gaji ya kyaleta.
Washe garine umma taji abinda ya faru a wurin hjy data shigo su gaisa umma tace a bata hakkuri sahiba fada ke gareta itama wanan halin yana damunta dani ai.
Na fito na samu hjy da umma a falin a cikin shirin makaranta na suka har kasa na gaida hjy din kamar yadda umma tace mu rika gaidasu.
Bayan ta karba ne ta fara min fada kan abinda nayi a jiya din tana fadi ita sin ai matar mahaifin mune udan ina haka shima ba zaiji dadin hakan ba ai.
Shiru nayi banyi magana ba saidata gama na mike tare da fadin thank you ma na kalli umma ina fadin zan tafi umma ta juye baki a cikin yarbanci tana min fada akan kada na kara fada haka da kowa koso nake plain din mu ya rushe ne idan ina hakan oda nace na wuce abinna .
Duk da naga yaran sun manta da hakan ban yarda na shiga zancen su mun dawo gida lafiya bayan mun taso zuwa gida suke nuna min assignment din da nayi taci su tana murna dayan tace nima na koya mata na ta yau nayi banza da ita.
Haka yaran suka zo suka tare muna a dakin mu dole umma tayi min tsawa na zauna na koyawa yaran suka fice can kuma suka sake dawowa sai ga uwar na kiran su sun daje still suka dawo kuma sai dare sosai suka bar part din nice na rakasu zuwa part din mu.
Haka dai zaman namu a gidan daddy yake tafiya kadaram kada ham wani abu da nayi notis a ranan girkin anty shine duk naci abincin ta haka zan zauna na amaye abincin tas a cikina sannan zan ji dama a karshe kuma kaina ne zai ta min ciwo sosai sai can ya lafa min.
Ranan gashi ina ji yunwa sosai tundare har safe banci komai har sha biyun rana mikewa nayi zuwa kitchen din su na samu mai aiki da ita suna girki.
Una weldone nace dasu tare dan raba ido ga kayan abincin dake kitchen din baga ko mai ba nace i wan cook indomie.
Juyawa tayi ta kalli hannu na tana fadin whare is d indomie nace i tink say you have it here ta juya kawai ta kyaleni a wurin taci gaba da aikin ta a wurin suka fita batuna.
Na juya na fita a hasale ban tsaya ba sai part din mu na dauko kudi na dauki dan gyalena na dora a kafada na dagani sai dan riga karami ya dan wuce gwiwana na fice daga gidan.
Wani shago danake hangowa idan zamu tafi school a unguwan na taka na tafi na sayo duk wani abinda nake so na juyo zuwa gida da kaya a blue leda.
Ban kallon kowa sai tafiyana nake a cikin dan rigana sabar sabar dani motar data wuceni ne ta dan dawo baya ta tsaya a daidai inda nake na zo na wuce ta ko kallon gefen ta banyi ba.
Najji anyi horn hakan ma baisa na juyo na kalleshi mai shi ba sahiba naji an ambata na juyo da sauri cikin mamakin jin an anbaci suna a nan din.
Mukai ido biyu da ya Abubakar a cikin motan yana zaune fuska a murde yake fadin from where are you ?
Nace i go by indomie that shop what ya fada har yana dan kallon gefe idan babu wanda yaji abinda na fada a lokaci.
Oya inter ya fada yana bude motan gaban shi na dan daga kai na kalli get din gidan da baida nisa damu lokacin.
Nace No i can trake, no far from here, yace a cikin tsawa common inter d car jare jin hakan na fada motan daya bude da sauri.
Ina shiga ya fara fada yana fadin babu abincine a gidan nace akwai saidai duk ranan da anty din nan tayi girki naci sai nayi ta mai kaina ya dinga min ciwo sosai tun jiya banci abinci ba yunwa nake ji .
Kuma nayiwa anty magana a kitchen idan akwai indomie ta ban na dafa ta kyale ni shine na dauki kudi na sayo.
Yayi shiru kafin yace na fadawa hjy nace ban fada ba don ban son na dame su na fada ina kawar da kaina gefe shima shiru yayi har muka shiga get din gidan.
Yana bude motar yace dani wait for me there naja na tsaya wuri daya har ya fito daga motan bayan ya rufe ya nufi hanyar shiga gidan yana fadin follow me nabi bayan shi da sauri.
Part din mahaifiyar shi ya nufa suna falon ta ita da yaranta da yanzu a nan suke zama muka shigo tare dashi yayi sallama suka karba mai.
Ya juyo yana fadin na aje kayan dana sayo a gaban hjy na dan yi darrr don yunwan da nakeji a lokaci.
Haka dai na aje din a gaban ta ta kalli kayan da mamaki ya nuna da hannu yana fadi a cikin hausa ga kayan nan yazu na hadu da ita wai ta sayo a waje zataci yunwa take ji.
Amma wanan yarinyar da tonon asiri kike wallahi hjy ta fada tana harara na ya tare da fadin a, a mommy nasan halin yarinyar nan tace taje kitchen ta fada suka kyaleta .
Yaci gaba da fadin ta fada min wani zance da ya kamata a zauna ai nazarin sa don idan taci abincin anty wai amai takeyi kamar zata mutu wanan maganan a duba mata ne.
Aduba meye ta fada rai bace yarinyar nan bata son a zauna lafiya a gidan nan nake gani zan zauna da uwarta muyi magana tunkan ta hada wani fitina kan hakan.
A a mommy wallahi nima kusan kullun naci saina amayar dashi saina daina ci dole Fa,iza ta fada daga gefen su.
A dai duba din tunda haka ne kada azo rashin kulla da hakan ya haifar da wani matsala nan gaba.
Jeka modibbo nace zan duba wanan zance naga ya da za,ayi ya juya wurin Nabila yace bata wani abu a nan idan akwai taci banda bread da butter ba wani abu a nan yanzu ok kawai ya fada ya fita daga dakin.
Sai kuma ya dawo yana fadin Fa,iza dauko gyale kizo da ita ku sameni a mota yasa kai ya fita ba abinda uwar zata ce sai kallon juna da sukayi da diyan ta kawai nikan na duka zan kwashi kayana in tafi.
Fa,izan tace dani in biyo ta mu tafi sai hjy din tace dani hakan nan zan fita ta nunani da hannu tana bata rai na danyi kasa da idanuna fa,iza din ta fito daga daki tana fadin mu tafi nabi bayan ta tsomai tsomai dani muka bar part din ban fita ba saida nakai kayan dakin mu na aje da sauri na biyo bayan su.
Wani gidan abinci ya kaimu akai muna take away har leda biyar sai kayan drinks daya saya muna muka juyo zuwa gida.
Muna sauka ya mika min ledan abinci biyu na drinks din daya na duka ina godiya na shige part din mu da sauri sai dai kash yuwa yacini a lokacin ban iya cin abinci ba Allah ya taimakeni akwai fura mai sanyi nasha sai barci.
Bayan sallah magariba muna zaune su umma suna cin abincin da na shigo masu dashi don ban boyewa umma komai ba don ban iya karya ba a rayuwana.
Sai ga mommy tayi sallama dakin ta shigo a falo ta samemu zaune muka shiga gaida ita ta zauna tare da kallon wurin da aka aje muna abinci bamu taba shi ba tace.
Dazun yar nan ta tafi sayo abu suka hade da yayan ta take fada min wani magana daya ban mamaki wai idan taci girkin hjy Karima sai tayi ta haraswa .
Wallahi hjy nima hakan yana ban mamaki don ranan har marinta nayi a dakin nan na tursasa ta sai da taci loma biyu saida ta kwata ciwo tun wanan ranan na kyaleta ai da abincin ko kamahin shi taji yanzu matsalane hakan .
Ikon Allah wanan wani irin matsalane haka ya samu yarinyar nan kuma ta dan kura min ido na dan lokaci
ZAINAB IDRIS MAKAWA
A NA DARA GA, , , , , , , ,
2️⃣7️⃣
BY ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , , ,
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AL GAFFAR, , , , , , , ,
ONLINE PAID NOVEL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN