Showing 162001 words to 165000 words out of 382072 words
ba Alh shinema dalilin zuwana yanzu ai kan zancen.
Don Nazifa tace tunda ya fadi hakan ba zaizo gidan nan ba kan maganan nan nasu tunda ba fada sukayi dashi ba tazo nan don haka kayi hakk, , , ,
Ke salma ki kama kanki da wanan maganan da kike kokarin fada min a yanzu idan baizo ba shike nan a kashe auren mana bashi ke nan ba.
Alh har da bakin ka kake fadin auren yarka ya mutu bayan kasan akwai haihuwa a tsakanin su yaran ina za a kaisu idan ka kashe mata aure ?
Yayi wani irin juyowa yana fadin yara yarafa kika ce salma yaran dasu taje gidan sa dama ta mayar mashi da tsiyar sa mana kowa ya rike nasa.
Gaskiya hakan ba zai faru ba insha Allahu kadaiyi hakkuri kai mai diya mace ta koma dakin ta tunda dama duka daya ake matsalan ka da mahaifin shi ba zai shafi auren yarka ba.
Wani tsawa ya jefa mata kafin yace kin ko san abinda kike fadi idan kin mata dako ni waye ya kamata kishiga hankalin ki kinatsu keda yar taki zaifi maku.
Mikewa tayi rai bace ta fice falon nasa tana magana ciki ciki ya bita da kallon tsana har ta bace mashi da gani yaja tsuki yana kallon ruwan dake gaban shi.
Dakin ta ta koma a cikin bacin rai ta rasa meke mata dadi a lokacin zama tayi tana kallon yar nata dake kwance dunkule a cikin damuwa.
Mikewa tayi tafita daga dakin tare da wayan ta falon ta ta koma ta fara neman layin da take son kira har ta samu ta danna kira ba, a jima ba aka dauka.
Sun dan dade suna magana da wace ta kira din a wayan kafin ta mike tsaye tana kashe waya tare da sauke ajiyan zuciya.
Dakin metting din namu yayi tsit ana jiran aji me zaice damu a wurin game da kiran da yai muna na gagawa kan shirin da yake son ayi din.
Shi ya fara gabatar da tsarin shi kafin sauran su kawo nasu shawara duk su dora akan nasa din sai da naji sunyi shiru na dago kai na dan saci kallin su lokaci guda kafin na mayar da kaina kasa ina rubutu.
Sam ban yarda nayi wani magana a aurin ba don abinda nake son fadi bai yuyuwa a lokacin don a gauraye muke ga addini sannan kuma su ko musulmai sun dauki wanan da muhinmanci sosai.
Har aka gama na tura mashi sakon a nasa sytem din ina jiran su mike nima na tashi Ausa girl you no say anything now ?.
Felix ya fada yana mikewa na danyi murmushi ina tashi tsaye tare da kallon su ina fadin Allah ya sadamu da alherin sa na saba jakata na fita daga office din.
Tun a mota na fara fada a zuciyana ina faman jin zafin irin dukiyan da suka ware na wanan shagalin kai ina na fadin shirmen banza shirmen wofi mutane ku dinga hauka haka wai al,ada tir da wanan bakin al,adan nasu gaskiya naja tsuki ina kada kai tare da fadin kai ina sam hakama bazai yuyu ba haka kawai ku karawa mamaci nauyi don jahilci.
Shiyasa bahaushe ko yauahe yake rena addinin yare don duk yadda kayi dashi sai ya surka hakan da al,adanshi.
Bayan na isa gida nayi wanka nafiti banci abinci ba kwantawa nayi don in huta saidai barci ya gagareni a lokacin.
Gashisai juyi nake ina tsuki can nayi wani tunane take na mike zaune na jawo wayana don aikata abinda zuciyana ya bani a lokacin.
Wayana dauka na zauna na tsara komai yadda nake so na tura sakon kai tsaye zuwa gareshi nayi saurin kashe wayan nawa don kada ma a kira a sameni a lokacin kan wanan karanbanin dayi a lokacin .
Sai lokacin naji dan sanyi a zuciyana duk da nasan al,adan sune hakan shawarana ko magana ba shi zaisa su fasa abinda sukayi niyar yi na barnan dukiya ba ga wanda ya mutu din.
Na fadakar dashi yin hakan da zasuyi katin wani nauyi ne gun mamacin su kamata yayi su bada sadaka gun mabukata da gidan marayu a cikin unguwa.
Ko asai shimfida akai masallataiya da butoci da laspeakee gadai abubuwa nan da dama na rubuta mai na fadarwa garesu da wanan tunanen na koma na kwanta barci.
Washe gari da safe ina barci ummace ke tayar dani na dauka zancen zuwa wurin aiki zatayi min har na fara fadin umma yau ba company zani ba.
Sai naji tace kina da bako a waje yana jiran ki wai umma waye da safen nan kuma na tambaye ta banga maishi ba dan wajen Abdulhamid ne ya shigo yake fadi.
Lokaci na duba a wayana tara saura na safe ashe lokaci har ya ja haka ina kwance na dan shiga bayi na fito na dauki rigan da nayi amfani dashi jiya na mayar a jikina sai hula akaina.
Na sauko na hangoshi tsaye ya bada baya yana kallon titi har na karasa saukowa kan steps din ina mamaki a raina waye wanan mai sallaman dani wanan lokacin har na iso nayi sallama ya juyo yana amsawa .
Gabana ya fadi tare da ambata sunan shi lokaci guda nake fadin yaya Abubakar kaine dama kana nan wai ashe dama akwai ranan da zaka tuna damu har kazo garemu ?
ZAINAB IDRIS MAKAWA,
ANA DARA GA, , , , , , , , , ,
4️⃣8️⃣ BY, , , , , , , , , , ,
ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , , , , , ,
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM ASH SHAKUR, , , , , , , , , ,
ONLINE PAID NOVEL YAR UWA KUKAN KURCIYA A KULLUN JAWABINE SAI MAI HAKKALI KE GANEWA, , , , , , ,
Yana tsaye ya zuba min idanun shi ba kiftawa jikin shi saye da farar shedata maza mai dinki iya cinyar shi da guntun hannu.
Ga shaddan sai maiko takeyi alaman tsada da sabon taka a jikin shi agogon hannun shi silver sai kyali da yakeyi da takalma baki rufafu a kafan shi.
Shiru yayi baiyi magana ba sai kallon mamaki da yake min naci gaba da fadin yaya na dauko ko duk dangi sun kimu kaida yan gidan ku ba zaku taba mantawa da muba ai yadda kuka nuna muna kauna.
Sai gashi har kun din kun manta damu kun watsar damu a cikin kabila kun fita batun mu kun barmu a nan muna rayuwan kadaici.
Haka baisa mun zargeka ba sam don kaima hawan abin kayi daga sama yaya dalili yana iyasa ka fita zancen mu idan kaga abin zai shafi wani naka don haka zaka iya mantawa damu, , ,
Sahiba ya fada da karfi a lokacin ne wani kuka mai karfi dayafi wanda nakeyi yazo min na dago ina fadin haka ya tabbatar muna da kissan Abban mu ya shafi duk ahalin mu ga baki daya ke nan, , , , , ,
Sake kiran sunana yayi a cikin tsawa a daidai lokacin da gaba daya yan gidan namu ke fitowa zuwa wurin ga baki dayan su umma har tana hadawa da dan gudu tana saukowa.
Kilode sahiba na dago kai na kalleta a cikin hawaye ina fadin ko,sin kankan, ina nuna mata shi da mamaki a fuskan ta yadda manya kan rude wani lokaci idan sunga tashin hankali.
Juyowa yayi don jin muryan umma din da magana ya makale mata lokaci daya duk abinda take da niyar fada nakinta yayi nauyi ta kasa fadi lokaci guda.
Sai nuna Abubakar din da yatsa da takeyi can ta samu bakinta ya bude tana fadin modibbo kaine yau ?
Ya dan murmusa cikin takaici yana fadin nice umma mun sameku lafiya yaya gida ya bayan rabuwa zoka shiga ciki umma ta fada ba tare data amsa mashi gaisuwan shi ba har lkacin kuka nake darza a wurin sosai .
Amar na isowa yana sheda fuskanshi ya fada a jikin shi lokaci daya yana kiran sunan shi yana sake kuka mai karfi shima.
Duk dauriyan ya Abubakar din ya kasa rike hawayen shi shima din dai kukan yakeyi sosai a lokacin hankali tashe.
Nan umma tasa hannu tana fincike Amar din da shima ya rike shi a lokacin tana fadin ku barshi ya shiga ciki kun tsaya a nan kuna kuka haka kowa na kallon ku.
Sai kuma ta juya wurin muniya tana fadin muniya broda din mune daya tafi shekara kusan biyar kenan rabon shi damu.
Shine wanda ya saya muna wanan gidan da muke cikin sa tana nuna gidan dagani itama umma din a rude take a lokacin don bata cikin natsuwan ta idan kaganta.
Inda nake tsaye na dafa mota dayazo a cikin ta ina rusa kuka ya nufa hannuna naji an riko wanda na gane ba hannun umma bane lokacin yasa na juyo da sauri.
Shine a tsaye bayana yana fadin zo mu shiga daga ciki ku daina kuka haka gani na dawo da karfin Allah gareku wanan karon insha Allahu kunyi hakkuri ku saurari uzurina don Allah.
Zomu shiga ciki ya fada yana mai kura min ido yana kallon cikin kwayan idona lokacin na mike nabi hanya ba tare da masa magana ba zuwa ciki.
Shima din jan hannun Ammar yayi suka nufi hanyan cikin gidan namu yana sharewa kanin nasa hawaye tare da danyi mai magana a cikin kunnen sa.
Ban tsaya falo ba daki na nufa na fada saman gado naci gaba da kukan da zance ga dalilin shi ba a lokacin dalili daya ya kawo shi shine zuwan yaya Abubakar wuein mu yau.
Ina jin muryan su a falo tare da umma bai fadi komai ba shi ummace ke magana duk daba wani abu take fadi ba sai tambayan shi da tayi mutanen gida da sauran su.
Barin zo umma ya fada ya mike tare da tambayan ina ciki ko aka bashi amsa da ina ciki ya shiga da sallaman shi dakin ya hangoni nayi rub da ciki kwance saman gado ina kuka.
A kofa ya dan tsaya ya kura min ido kafin ya karaso cikin dakin yana kiran sunana jin ya zauna a bakin gadon kadan kusa dani yasani motsawa lokacin.
Kara kiran sunana yayi yana fadin kukan ya isa haka don Allah nasan nayi laifi babba na tafi na barki da fama dasu umma da Ammar amma ki saurari uzurina kan haka.
Mikewa nayi na fito falo wurin umma ya bini da kallon tausayi don yasan irin zafin da mukeji a lokacin ya dan kada kai ya mike ya fito daga dakin.
Ummace ta kalleshi tana fadin sahiba badai rikici ba idan ta tashi yi yanzu murnan ganin shi kukewa kuka haka ko baku so ya dawo garemu bane yasa kuyin kukan nan.
Barsu, suyi umma don a zaton su na tafi na barkune da wani manufa Allah ne shedana tafiyane ya kamani tun ranan dana aje ku a gidan nan.
Gaba daya nida iyalina muka bar kasan nan sai kuma nayi kuskuren daukan layin ku a lokacin don azatona zan kara zuwa na dauki layin ku ko kuma lokacin ba bukata tunda zan dinga zuwa kai da kai ina ganin ku.
Saidai gaskiya nayi mamaki kwarai lokacin dana dawo kasan nan naji cewa tun lokacin ba wanda ya neme ku har zuwa yanzu din.
Bansan da haka ba a bakjn Amira yar hjy karima nasan basu tare daku ashe yadda na zata abinda ya ban mamaki kwarai ke nan a lokacin.
Dakuma nayi tunanen cewa nima kaina gaba daya wani tunane a kanku ya gushe a zuciyana yasa na fara zargin cewa dole akwai wani dalilin hakan an matar damu ku an cire muna ku a zukatan mu ga baki daya.
Saidai abjn mamaki ba a cire ku a zuciyae Amira da Faiza tare da fatima idan yai zan shiga cikin gida don mu gaisa zakaji Amira tace yaya ka kaini wurin sahiba.
A sauri don Allah ita kuma Fa,iza zata labe tana tambayana yaya ka samu layin sahiba din ka bani wanan ya kara min karfi a zuciyana jiya tana tambayana na koma gida na kwana da shirin zuwa duban ku yau din nan.
Karshema kuma kyautan da sahiba ta turawa yan uwan nata ya kara karfafa zancen ku a yanzu don yadda hjy karima ke fada min cewa saida takai ga dukan yaran kan tambayan da suke mata ko da acikin darene.
Kunji abinda ya faru wanda nasan wani kulline akan hakan don Allah kuyi hakkuri da abinda ya faru banayi bane don wani manufa a gareku.
Haba modibbo idan kana da wani munufa akan mu tun farko aiba zaka daukemu ka kaimu wurin dangi ba tsawon shekaru ba kuma zaka nema muna wurin zama a nan ks hanemu da yawon hayaba ai.
Kayi muna hanyar da zamu dagora da kanmu nabada haya a dayan bangaren kudi na shigo muna ta cikin sauki a yanzu duk da yake hayan ya zama kamar gidane don wanda ke ciki a yanzu kamar dan uwa muka koma dashi a nan.
Mutumin kirki muka samu don tun lokacin bamu sa wani a gidan nan ba yana rufene kawai sai lokacin da wanan mutumin ya shigo rayuwan mu a karshe kuma sai gashi ya samu matsala da gidan da yake haya shine muka bashi nan su zauna a cikin sauki don wurin aikin su daya da sahiba shine sabon mu dashi.
Ya dago yana fadin Sahiba din aiki takeyi yanzu wani irin aiki takeyi a yanzu din kafin umma ta bashi amsa wayana dake gefe yayi kara na dauka.
Felix ne da zolayan sbi ya fara mun hira yana ban labarin wai yau sun tashi oga na fada masu cewa sun danyi wasu sauye sauye taron da za,ayi don haka na shigo karfe hudu mu zauna kan sabon tsarin da akayi din.
Kinsan masu kudin nan da wahal da tallaka ya dauka mu bamu da abunyi ne a garin sai nasa tsarin koda yake fa muna samu oga badai kirki ba kan don nasan bamu tashi a taron nan banza.
Jin abinda yake fadi yasa na danyi murmushi daya baiyanar asirin kyawawan dumple dina a fili har suka dan lotsa kyawona ya baiyana a fili sosai.
Daga inda yake zaune yana satan kallona ya lumshe idon shi yana ambatan subbahanallahi haka yarinyar nan take dama ashe ?
Na sake dago kai lokacin da Felix din ke fadin kedai yarinya fito da katon jakarki gobe zamuji dumus a wurin ogan mu sosai na sani.
Fararen idanuwan nawa da suke farare tas gashin ido dogaye don wasu na dauka ina saka eyes lashes ne a idona haka gashin gira na suma a kwance bakikirin dasu kamar an jera min su.
Dariya nake sosai ina kara juyawa kamar da gaiyya nake juyasu a lokacin wanda ma ban san ina yin hakan bani sam.
Ido ya kura min yana kallona tare da tunanen yadda na sauya ga baki daya ko magana na yanzu abin kallone don a cikin wayewa da isa nani watace nake wayan yana kuma jin kalaman mu da Felix din.
Nan dai muka dauki lokaci a wayan ni da Felix din indan na dago kaina har fararen idanuwa suka sauka a nasa ganin zan kallo inda yake sai yayi saurin kawar da idon shi gefe da sauri.
Subbahanallahi yake iya ambata don ganin yadda nake sauke idon ganin yadda wayewa da natsuwa yake a tare dani ga wani irin kwanciyar hankali daya hango .
A take yaji wani irin faduwan gaba ya sauka masa tare da tsoro da fargaba yanayin nan da yake kallona a cikin shi zaune gaban shi lokacin.
Don dai komai nawa har nasu umma din da Ammar a yanzu ya sauya muna ba kamar yadda muke a cikin wahalan rayuwa ba a baya.
Saidai kuma yasan ba karamin kudine zaiyi wanan aikin ba a garemu haka dole dai da akwai babban madafan da muke dafawa a rayuwa daya sauyamu haka lokaci guda yanasa a zuciyar shi.
Daidai lokacin da yaji ina sallama da wanda nake wayan ya mike yana fadin shi zai tafi sai ya sake dawowa insha Allahu zai shigo ya kara ganin mu.
Wanda har lokacin ban kara masa magana ba ko kallon inda yake ya daga daga zaunen da yake umma ta kalloni tana min signal da ido nayi saurin fadin mungode ya Abubakar.
Yace No kada ku damu wanan duty nane in kula da ku don ku din yan uwane sosai a gareni don haka ba zan kara barin ku ba kuma insha Allahu ya fada yana taba kafadan Ammar
Hannu umma ta daga tana fadin amin wooo amin mun gode nikan hankalina na mayar kan wayana na nuna ban ma san yana falon ba a lokacin.
Wanda sam bashi ba ko umma hakan da nayi sam bai mata dadi ba don ita a nata taso muyi haba haba da shine mu nuna ina aka saka dashi