Showing 228001 words to 231000 words out of 382072 words

Chapter 77 - ANA DARA COMPLT BY MAKAWA

MAKAWA   

29 Jun 2024

28451

bazata lokacin.


ZAINAB IDRIS MAKAWA


ANA DARA GA , , , , , , , ,

6️⃣7️⃣ BY, , , , , , , , , , , ,

ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , , , , , ,

BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AL QAWAIE , , , , , , , , , ,

ONLINE PAID NOVEL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA BA TARE DA HAKKIN KOWA BA DON BIYA KI TURA DARI BIYAR 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK 08036959257

ALLAH SARKI AI RAINA BAYA BACI YANZU DON KIN FITAR DON NASAN AKWAI RANAN HADUWA SEE U👋👋👋👋

Ina tuki ina sharan hawaywn daya cika min idona da bakomai yasani yun shi ba a lokacin sai ganin yadda taron yan uwa basu san mu ba alhalin muna jinin su.
Wanan wani irin zaluncine haka dan uwa uba daya ku rabashi da duniya ku wofintar da iyalan daya bari a cikin duniya cikin rashin damuwa ku kuna zaune daz naku cikin jindadi da kulawa duniya ina zaki damune haka ?
Muniya datayi shiru a gefena take fadin kiyi hakkuri nasan abinda ya sakaki kuka ganin yan uwa haka a wuri daya dole kaji ranka ya sosu sosai .
To amma kuna da yan uwa haka ashe Sahiba meyasa baku ziyaran su alhalin naga suna son ku sosai ji yadda yarinyar nan data ganki ta rude gaba daya wallahi don jin dadin ganin ki.
Amma daga ke har umma har Ammar kamar baku damu dasu ba why kuke nuna kamar baku da gata hakane sai wanan dan uwan naku kadai naga yana zuwa wurin ku shima baku ke zuwa ba ?
Murmushin dole na kakaro a fuskana lokacin na kara kai hannuna ina share hawayen dake fuskana bandaiyi magana ba itama nisawa naji tayi kawai lokacin.
Haka muka isa gida umma dake zaune tare da yaran suna zaman jiran dawowan mu ta fito tana muna sannu da zuwa na amsa a cikin rai kawai na shige ciki zuwa dakina.
Gado na fada na sake wani kuka mai ban tausayi rashin Abban mune ya dawo min sabo a zuciya sai nake ganin gaba daya ahalin namu basu kaunan mu ne wanda ya mutu ya mutu ke nan dai.
Nakai wani lokaci kwance a wurin kafin naji muryan maryam tana fadin tare da dan bubuga min jiki in tashi in tashi kawai take fadi ganin ban tashiba ta hawo gadon ta kwanta a jikina.
Sai lokacin ne na sauke wani irun ajiyan zuciya naji kamar yarinyar ta lalasheni a lokacin ina jin wani natsuwa na sauka min a zuciyana lokaci guda.
Nakai wani lokaci a hakan ban motsa ba kuma ba barci nayi ba a lokacin jin nauyin yarinyae yai min yawa a jikina yasa na dan juyo naga halin da take ciki ashe barci yarinyar tayi lokacib a jikina na gyara mata kwanciya nima na juya rigingine ina kallon darking din dakin.
Sai can na tuna banga umma ta biyoni daki ba hakan ya sana mike da sauri nafito daga dakin na nufi dakin umma ganin bata falo a lokacin yasa na nufi dakin nata.
Zaune take a inda ta idar da sallah a cikin wani yanayi na ban tausayi jin na shigo dakin ne yasa ta dago idanunta daya sha kuka ta sauke a kaina lokacin.
Zaune nakai bakin gado kafin ince komai da ita ta dago tana tambaya maryam na wurin kine na gyada kai tare da fadin tayi barci.
Nan take tana damuna tun fitan ku shine na turata wuri ki ta fada a kasalance nasan zaki take son sha zakin nan kuwa ba zai basu lafiya ba idan ya tashi tambayan su.
Sun saba da shan sa ne tun gida tunda kikaga shi kadaine a bincin su tace bata ko koyawa diyan ta alheri ba ai duk uwar da tasan kanta zata nisanta danta da wanan kayan kwalaman na turawa saidai uwayen yanzu suna ganin kamar hakan wayewa ne amma da illan da yakewa yaro a jiki sosai kuwa.
Ai kinga yarbawa da sauran kabilu basu yarda sun yar da gargajiya ba kodama sugar zasu sha saidai mai kololo kuma bai wuce kwara biyu a wuni don sun san illan hakan ga jikin dan Adam abin ba manya kawai yake shafaba har da yara kanana a wanan zamanin.
Shiru nayi ina nazarin abinda umma ke nufi kafin inji tana fadin ashe kun samu taro sosai a airin yan uwa da kukaje ?
Na nisa tare da dago kai na dan kalleta nace eh umma gaskiya sun nuna muna jin dadin su sosai da ganin mu a wurin saidai mun barsu da mamakin mu sosai a zukatan su.
Nan dai na fara bata labarin abinda ya faru a wirin damu har dawowan mu din tayi shiru tana tunane mai zurfi.
Zaune suke a falon su sun tasa kayan a gaban su suna kallo a cikin mamaki kowa yayi shiru sai hauwace tace nifa wanan kafiran motar da kuma irin shiganta shine ya tsaya min a rai wallahi.
Jiki don Allah da wani zancen banza ace maki mutum ya fito lagos don me zaki tsaya mamakin arzikin ta lokaci guda sai dai idan kinso.
Shi dan lagos meye bai iya aikatawa don kawai ya tara kudi nikan banyi mamakin hakan ba tunda dai kinsa Sahiba kyakyawace ta karshe dama .
Wai kina nufin ta kallo Nabila din bata karasa ba tace kwarai kuwa ke nifa ban wani mamaki ko maza sukaje neman kudi acan ai kinga yadda suke dawowa nan
Amma ai barikin ta dai baisa ta canza ba yanzu ko tunda tarbiyan nan nata naga yana nan ji yadda taje gaban su mommy ta gaidasu a cikin taron nan ni shine ya burgeni da ita a wurin wallahi ko duk ko yadda ido yake a kanta ba.
Sahiba ta koma ubanta sak a yanzu muryan mommy datayi tagumi ta fada cikin nisawa da nauyi kafin ta fadi hakan duk suka kallota.
Wallahi yau ganin yarinyar nan ya daga min hankali sosai bani ba son duk wanda ke wurin nasan abinda ke zuciyar shi ke nan idan ya tuna.
Muryan yayansune yayi sallama duk suka kalli kofan shigowa falon nasu lokacin guda ya shigo suna mashi sannu da zuwa.
Saida yagaida mommy a cikin mutunci ya samu wuri ya zauna ya fara amsa gaisuwan kannen nasa a lokacin.
Yana ce masu ya bukin ashe har an fara ke nan ko hauwa ta amsa mai da kai kafin tace tun jiya yaya muna ganin bukin yan gayu ai.
Faiza ta fito daga dakin cikin murna take mai sannu da zuwa ta zauna a kusa dashi ta fara fadin yaya mu Sahiba fa tazo garin nan wallahi.
Sahiba ya fada a cikin mamaki yace ina kika ganta tace cikin fara,a wallahi wai bukin ne ya kawo su tace amma bata sauka gidan nan ba kuma ta karasa fadi cikin bacin rai a fuskan ta.
Ita dawa tazo da mama da Amar kanin ta ya tambaya yana boye razanan shi a fuskan shi lokacin.
Kai ina kakai yara nan ka tayarwa mutane da hankali haka anya kana son ganin farin cikina kuwa yanzu modibbo ?
Yara mommy wasu yaran ke nan ta watsa mai harara kafin tace ai sainace yaran ka zaka gane ko ?
Ya dan shafo fuskan shi kadan zuwa kasa yace suna Abuja gidan abokin aikina na kaisu tunda ita bata damu dasu ba.
Baka da hankali ina gani yanzu modibbo da har ka tsaya biyewa matarka mara tarbiya ka aikata hakan bayan kasan hakan zai jefamu a wani hali na tashin hankali.
Kuyi hakkuri mommy nasan a lokacin idan na kawo maki sunan zakice ne a mayar dasu wurin ta a lokacin ni kuma ina son nuna mata ita ba kowa bace yasa na dauki matakin hakan.
Yanzu kai wani irin yardane tsakanin ka da wanda kakaiwa yaran har ka yarda zai rikama yaran tsakani da Allah ku dinga yin tunane kafin aiwatar da abu wallahi.
Abinda za aje a dawo ana da ansani a kansa bayan lokaci ya kure baida dadi duk da dai itama din Nazifan halinta sai Allah ne amma wanan matakin baiyi ba wallahi ta karasa cikin bacin rai sosai ta mike ta shige dakin ta.
Suka bita da kallo kafin hauwa tace dashi kayi hakkuri yaya har daddy saida suka samu matsala da mommy kan wanan zancen don shi daddy wai laifin mommy yake gani yanzu .
Amma dai ita mommy ai bata kula mashi ba tunda neman abinda zai tunzurata ta cikin taron nan yanzu yakeyi .
Wani kallo yayi wa yarinyar yai shiru bai kara cewa komai ba yashiga dogon tunane mai zurfi kafin ya furzo da iska daga bakin shi yana fadin.
Naso a ginawa mommy gida ta bar su nan amma kuma hakan ba abinda zai yuyu bane don shi kanshi daddy ba zai yarda da hakan ba sam.
Kaima yayan mu kasan ba zai yarda da hakan ba ai don yasan duniya zata zageshi kawai dai mommy tayi hakkuri da sabon sauyin data samu a wurin shi yanzu don anty da kuke gani ba karamar shu,uma bace.
Kai ku daina irin wanan zancen zargine da camfi irin na mutane sai mutum ya daukarwa kanshi zunubi a banza irin haka.
Yaya kai namiji ne baka ganewa wallahi amma muda muke zaune a cikin gida mun san abinda ke gudana ai Nabila ta fada cikin bacin rai da damu kan irin cusgunawan da mahaifiyar nasu ke gani yanzu a gidan.
Bai kara magana a kan zancen ba sai tambayan daya jefowa Faiza data zauna a gefen shi itama cikin damuwa don irin rayuwan cin fuskan da mahaifiyar tasu take gani a gidan yanzu abin yana damun kowan su a rai.
Yace Sahiba din tace zata kara dawowa nan ne ko sun tafi ke nan tace zata gobe da yardan Allah don bamu ko zauna da ita ba a gidan gwaggo hari inda akai event din muka hadu da ita tazo da Alheri sosai yaya taba kowa mamami bakaga irin kayan rabo da takawo a wurin bane yaya .
Na fada maki sahiba ta canza a yanzu don babba ma,aikaciyace Sha,aban comoany ga baki daya inda yake da reshe cikin kasan nan itace mai kula da shige da ficen komai a kasa.
Sahiba din kwarai kuwa ita din ba karamar mace bace a yanzu gaskiya duk abinda kukaga tayi kada kuyi mamakin hakan tanada oppotuniy din yin hakan gaskiya don ta wuce sanin ku a yanzu.
Kinji ina fada maki kina cewa wai maza takebi kila in bashi ba ina zata samu kudi irin haka take wanan abin yanzu kinji ke nan da kunnuwan ki hauwa ta fadawa Nabila din.
Kallon mamaki yayi mata kafin yace ke yanzu ashe ba mai tsayawa kiyi fada bane idan wani ya fadi haka akan yar uwarki ashe ?
Kai yaya wai idan an tashi zancen yarinyar nan kai da mommy sai ku dinga fadin cewa yar uwanmune su ta ina muka hada dangi da jikan yarbawa wata kila dai mahaifiyarta ce yar uwan su daddy ta can wurin dangin danga kawai ace wai muna da hadi da wanan mai zubin larabawan don dai yanzu na daina kiranta da jikan Oduduwa ai .
Jiya Allah yaya don baka ganta bace ta fito kamar yar wani kasa ba yar nan Nigeria ba shigan da tayi jiya din kasan mutane da gulma ina jin wasu na fadin ko yar abokon business din daddymu ce sukazo kara.
Nabila da bakinki kike fadan haka kan Sahiba koda yake ba laifin ki bane yanzu don baki san yaya alakan ku yake da ita ba shiyasa .
Amma ki daina don watarana zakiji kunyan hakan da kanki wallahi idan kin san su din ko suwaye gare mu da kuma abinda kike takama dashi a yanzu zakiji kunyan kanki a ranan yana fadin hakan ya mike ya fita kawai ya barsu suna binshi da kallon mamaki.
Tsuki nabila taja tana fadin shike nan don ta zama dan wani abu a yanzu sai ayi kokarin danganta alakan mu da ita kawai haka ranan naji Mommy ta fadi hakan har da muna fada a kanta nifa na tsani yarinyar ne kawai wallahi.
Don tafiki kyau yanzun kuma kinji ance ga cigaban data samu a rayuwa ko me hauwa ta fada daga gefenta me zata nuna min wurin kyau nima inada nawa dirin sai me kuma ?
Shi arziki yanzu yin shi ai baida wuya idan kana aon yi ga hanyoyi nan na samun arziki lokaci daya ga mutane bila,adadin ba sai kayi wani wahala ba can.
Suka hada baki suka kwashe da dariya lokaci guda suna kawar da kansu gefe daya lokaci guda don sanin halinta da sukayi wurin yaba kanta da nuna ita tafi kowa aji.
Daddy yana zaune a kasa saman kafet ya mike kafafuwan shi yana amsa waya lokacin ne anty amarya ta shigo falon ta zauna don ganin waya yakeyi a lokacin mai muhinmanci sosai.
Ya dago kai fuska ba yabo ba fallasa a cikin fuskan nasa ya juyo inda take yana sake dan murmushin dole da baikai cikiba yace .
To ya taron naku na yau dai an watse lafiya ko ta gyara zama tana lumshe idanu tare da fadin wallahi Alhamdullahi Alh jama,a sunyi kokari sosai wallahi.
Wai kasan har da Sahiba tazo daga lagos kuwa saboda bukin nan ai bansan yarinyar nan tana kaunan mu haka ba sai yau wallahi bakaga irin alherin data kawo muna ba ni ai takara jamin girma a garin nan sosai wallahi.
Tarin daya sarke mijin a lokacin shine ya hanata karasa maganan da take son fadi a lokacin shi kuma sosai yake son tarin ya tsaya mai lokacin ya tambaye ta wai wace Sahiba take magana a kaine ?
Ruwa ta mika mai ya amsa da sauri ya kurba kafin yadan ji sallama itako ta tsugune a gefen shi ta kura mai idanu cikin mamaki.
Sannu ta kara mai bayab taga ya samu saita numfashin sa a lokacin tana kokarin kawar da kayan abincin da yaci a gabashi.
Ta kara fadin wai sannu Alh irin wanan sarkewan haka wata kila yajin ne yayi ma abincin yawa don naji su hjy suna korafin hakan yace umm,umm.
Saida ya dauki yan mintina suna shiru a falon kafin ta mike tana fadin zan koma wurin baki dama nazone in fadama zancen sahiba din ne.
Wai wace Sahiba dai kike maganane tun dazun haka ta koma ta zauna tana mamaki tare da fadin a, a Alh akwai wata Sahiba da muka sani da wanan sunan bayan Sahiban maman Ammar na lagos da suka zauna gidan nan shekarun baya.
Ita nake nufi wallahi sai gata kwatsam a wurin taron Alh wai kaga Sahiba ko yanzu kuwa wallahi idan bata fadi ba kokai daka santa baka ganeta yanzu Allah ko.
Ni ai yau naga abin mamaki sosai kuwa Alh duk yaushe Sahiba tabar nan ne amma gata da gani a cikin daula take rayuwa yanzu gaba daya komai nata ya canza wallahi saita fadama itace zaka tuno da fuskanta na baya can.
Sallaman modibbo ne ya katse maau hiran ya shigo falon don ya gaida mahaifin nasa anty Amarya ke fadin a, a ashe ka dawo ke nan masu tafiya babu sallama kabar hankalin mutane a tashe.
Ya danyi murmushi yana kaiwa tsugunne tare da fadin mun samemu lafiya ya taron jama, a Allah ya sanya alheri yasa wurin zamantane har abada suka amsa da Amin anty baki har kunne tana washe shi don dadi.
Sam sam a gidan basu kula da abinda aka rubuta ba a cikin jug din da kofunan sai ga kira a lokaci daya ya fara shigowa a wayan daddy kiran baffa Abdullahi ne kanin daddy ya dauka .
A zaton daddy zance zai mai akan daurin aure amma sai yaji Baffa din na fadin yaya kana gidane wai ?
Eh gani nan zaune a falo ya bashi amsa yace kajirani gamu tafe da salau yanzun nan muna hanya ya amsa da to ya kalli modibbo yace dashi .
Tsarin da kuka dauko dakai dame dakin ka baku dauki tsarin kwarai ba ace mutane kullun babu zaman lafiya an fada maku kowa ba hakkuri yake da iyalin shi ba yanzu ina amfanin biye matan da kayi ka kwashe yara ka tafi dasu ka kuma kashe wayan ka ba a samunka ka tayarwa mutane kawai da hankali haka ?
Kanshi na kasa yana sauraren mahaifin nasa ne yaji sallaman kanin mahaifin nasa a kofan falo har lokacin Anty Amarya tana wurin a zaune.
Kowa kallon kallo aka fara a tsakanin su ganin yadda suka shigo falon a lokacin kamar a firgice ina yar uwanki Baffa ya tambayi anty Amarya tana ciki ta bashi amsa yace kira min ita kizo da wanan abin bukin da kika ba matana dazun a gidan hari.
Ta dago tana mamaki kafin tace wani ciki yace wanan anbin me kamar flask ma da akace watace tazo dashi kika basu akan sai gobe zaki raba saura.
Oh nagane jug din da


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login