Showing 330001 words to 333000 words out of 382072 words
gareshi sai mata dai da yara kan.
Ohni sahiba naga ta kaina a duniyan nan ni yaya zanyi da rayuwana ke nan da wanan kaddaran dayazo min a hakan ?
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ANA DARA GA , , , , , , , ,
1️⃣0️⃣0️⃣BY, , , , , , , , , , , ,
ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , , , , , ,
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM DHU_AL_ JALALI WA_AL_IKRAM , , , , , , , , , , ,
ONLINE PAID NOVEL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA BA TARE DA HAKKIN KOWA BA DON BIYA KI TURA DARI BIYAR 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK 08036959257
ALLAH SARKI AI RAINA BAYA BACI YANZU DON KIN FITAR DON NASAN AKWAI RANAN HADUWA SEE U👋
Kofan na tsurawa ido nabi shi da kallo har ya bace mun da gani kafin na sauke ajiyan zuciyan daya fito fili lokaci guda ina kawar da idanuwa ga kofan .
Aka sake turo kofan kusan lokaci guda azatona shine dai ya dawo kuma wanan lokacin sai muryan Fatima naji tana sallama da alaman kamar a dan firgice lokacin.
Yasa na juyo ina kallon su tare da fadin har kun dawo ke nan tace tun dazun muna waje an tare mu wai oga na ciki tare dake .
Juyowa nayi na dan kalleta take fadin wallahi anty Sahiba baki gansu bane fa a waje wasu irin murda murdan kataine dasu zabban tsoro na zatama wani abin mukayi lokacin da muka shigo na gamsu tsaye a kofan.
Banji tsoron komai ba tunda suka dakatar damu suna fadin wai oga yana tare da madam a ciki nasan shi suke nufi Faiza ta fada tana zama.
And so what da zasu tare ku a waje kamar wasu masu laifi shi baisan kuna dakin bane ya shigo muna dakin mu ?
Ai gara dai da suka tare mu ina zamu shigo ango da amarya suna ciki muzo muyi mugun gani a idon mu faiza ta fada tana kallo na tana dan dariyan shakiyanci.
Take na daure fuskana na hayayyako mata ina fadin Faiza ki dubeni da kyau nayi maki kama da wace zata wani shiririta da namiji can ?
Shi wanan din ai yanzu na daban ne ba dan i love you bane mijin kina don haka yana da right din da zai kebe da matar shi ai.
You are crazy faiza koda kuwa sonshi nake har cikin raina ba wanan daman a gareshi da zaizo min da irin wanan zancen a yanzu.
Ke kuwa kin san me aure yake nufi Sahiba mijin kine fa na sunna kike fadin haka aida zaran an daura aure a tsakanin ku shike nan komai ya wajjabata a tsakanin ku kuma.
You de craze har yaushe kika san irin wanan abubuwan da sai manya ya kamata su sani har kike wani kashe ido haka ?
Kinsan how old nake kuwa yanzu da ace nice na samu wanan babban daman da kika samu a yanzu kada kiyi mamakin ki nemeni baki ganni ba wallahi.
Wani kallon mamaki nabita dashi ina kallon ta tace kwarai kuwa sahiba dama da sa,a babba kika samu a rayuwan ki kuma naga kina son wasa dashi ke kamar baki san kin taki sa,a haka a rayuwan ki ba kekan ?
Ido na kurawa Faiza din tace Allah da gaske nakeyi sahiba gani nake sam abin kamar baki daukeshi da wani ma,ana ba a zuciyar ki.
Ban kara sanin ko waye mijinki ba sai jiya da sister ke kara bamu labarin shi matar shi daya da yaran su biyu yan mata tace bata son haihuwa da yawa tana planning.
A cewar ta matarshi ta girme maki nisa ba kusa ba da tare zasuzo nan sai tace bata shirya ba da tafiyan ya tashi don zata kai yaranta hutu Australia.
Ita din shi wai aurene na hadin iyayyensu mata da wani iri na kallo ta tace koya girmeta da kadan zai girme mata a shekaru don haka kinga ke nan dai ba yarinya bace dai ita din.
Saidai kinyi sa,a amma har idan kin daina wanan tsiwan naki na tsiyan na rashin nuna kulawa ga mutane don ita din ance.
Sam bata son yan uwan mijinta ko kadan don hakane ma yan uwa ke gudun su rabeshi a yanzu sabanin shi da yakeda son yan uwa birni da kauye nasa.
Yanada taimako tallaka sosai akace ga kula da iyali da duk wani wanda yake karkashin shi zaune yana jin dadin shi saidai idan har matan ta gane haka ba a daukan lokaci dole ka rabu dashi.
Matar shi shu,umace ta karshe yadda suke fadi din dukiyan shi da komai har ana zargin cewa suna hannun wanan matar don yadda take facaka da arziki ita kanta.
Auren shi dake sunce za a kirashi da mukkadarine don ba wanda ya taba kawo aure gareshi a rayuwan shi don yan mata da yawa suna son shi saidai babu dama garesu.
Akwai watama a cikin yan uwan su da kamar za, ayi aure tsakanin su ana sati daurin aure ayi komai yace ya fasa haka kawai har yau ance tana nan batayi aure ba tana jiran shi.
Yaran shi ko bai hadasu da komai ba a duniyan nan don yana ji dasu sosai akace duk abinda sukeso shi yake masu.
Kinga kota yaran kika nuna masu kauna nasan zaki kwasoshi a tafi yadda ake so keda shi don wanan mace dole sai an hada da siyasa lamarin ta.
Faiza do you know what you're saying me sahiba inbi ta yaran shi ko matarshi in sosu don kawai ya soni nerve ba Sahiban ummana nake ba ke nan ko kin manta da nice na girgiza kai tare da dan sauti da bakina ina fadin nerve.
Ki daibi sannu don irin wa yan nan matan dake kakace gida da wuya ake iya inmasu har kaima na baya ka samu ka kafa naka gwaunatin a zuciyan miji.
Who want the gorvenment ? i beg may you no west my time jooo all dis na rubish you de talk.
Sahiba wallahi kinsan fa yar maidugurice ita ni tsoron da nake ji ke nan wallahi koda yake kema din dai idon ki a bude yake amma duk da hakan dai ki kara natsuwa don Allah.
Juyawa nayi da niyar kyale zancen nata lokacin naji fatima na fadin ai ance wai tana da wasu hasabiban kannenta da take zaune tare dasu.
Wai yan iskane har shi basu raga masa itama din kamar dai tana tsorin sunema suke aiwatar da komai a gidan.
Yanzu ma haka tana can tana fitina dashi duk da yake yana nan don an samu wanda ya tsegunta mata zancen auren ki dashi.
Har hjy mahaifiyarshi takira ta zaga duk da itace mussababin hadin auren shi da ita amma ance yanzu duk ta manta da wanan ita kanta da yan uwanta kawai ta sani.
Yauwa kinga na mata faizan ta fada ko a nan saikiyi kokarin kafa gwaunatin kin tun yanzu a wurin hjyn tasa tunda muna tare a nan da ita yanzu.
Haka kawai fadin hakan da fatiman tayi sai naji ina son irin wanan drama din dasu haka yasa na juyo da kyau ina sauraren ta.
Har suka kare zancen su banjin zan dauki ko daya daga ciki don mutumin da yai min dole a kainshi ya bata min duk wani tsari da shirina a yanzu akan rayuwata.
Karfe uku kamar yadda muka saba fita nice na tayar dasu ranan da barci don ba abinda yafi min yanzu banda nakai kukana kan wanan sabon rayuwan da zan tsunci kaina a cikin sa daga sama a daidai lokacin da ban shirya hakan ba.
Farkon abinda ya dace dani ke nan a rayuwana na mika kukana a wurin ubangijina kan wanan matsalan a yanzu gani gaban maganin komai inji mafada.
Suna da gajiya a jikin su amma haka na matsa masu saida suka tashi muka tafi tare dasu ranan kan na mika kukana sosai a wurin Allah don babu kamar ubangijin mu gare mu.
Karfe goma muna masaukin mu na debo gajiya sosai a lokacin sai wurin kwanciya nake nema in kwanta har na kwanta din barci ya soma fisgana sako ya shigo min a wayata hakan yasa na bude idona.
Shine ya turo min sakon da Amaryata hope kin tashi lafiya ya karfin jikin naki ?
Naso sai na koma naje turai na kwaso maki kayan lefen ki don naga irin suturan su kike sakawa amma hjy ta damu da na fara saya maki tun a nan .
Don haka ki bani time da zamu zagaya zuwa cikin gari ki duba shine sakon daya turo min kawai naja guntun tsuki tare da wurga wayan bayana na kwanta sai barci.
Ban falkaba sai azahar na tashi ban kuma tsaya bin ta kan wayata ba wanka nayi tare da sallah kafin na hau abincin dana sama daci don yunwa nakeji sosai kwana biyun nan duk ban tsayawa naci abincin kirki saboda tunane.
Amma a yau kan jin kaina nake sakayau dani kamar an gafarta min dukkan zunubaina a ranan.
Bayan mun gamane kuma sai fira har muka gama mukai sallah la,asar na kara komawa gado na kwanta tare da jawo wayata.
Wani sakon shi na sama na bude tuni yake min kan sakon farko ga abinda na rubuta masa nima a lokacin.
Ayyah hjy nagode da kulawanta ga yar amananta saidai ka bata hakkuri ni din ba ma,abociyat tara sutura bace wanda ke gareni sun isheni rayuwa.
Bayan ya karanta murmushi ya sake bai kara min wanan maganan ba har sai ranan da muka hade dasu a wurin dawafin bankwana a nan ne muka hadu har da mahaifiyar shi.
Ba yadda na iya dole naje muka gaisa dasu din tana ganina ta fadada fara,anta tana miko hannu tare da fadin diyata na dauka har mu tafi ba zanganki ba ai zo nan ki zauna tana nuna min wuri a kusa da inda take zaune din.
Bayan na zauna taci gaba da fadin naso ace sun banike daga nan mu wuce can maiduguri dake yan uwa su ganki.
Amma iyayyen ki sun roka cewa muyi hakkuri har ku koma sati biyu da komawa su gama fadawa yan uwa sai ki tare ga baki daya.
Gabanane yayi wani mugun faduwa lokaci guda don jin abinda ta fada din lokacin da badon kaina a duke yake ba da zata iya hango irin razanan danayi a lokacin.
Sai magana takeyi bata kula da hakan ba taci gaba da fadin saidai yana da wuya ya barki ki dan zauna damu a maidugurin .
Don yace yanaga da wuya ki tsaya a nan don zaku wuce ga baki daya a can inda zaki zauna saboda wai ba a kasa daya zaku zauna da ita uwargidan naki ba yace.
Saboda yanzu harkokin shi ya koma singerpor ga baki daya da Dubai yace a cikin daya yake son ajeki a can .
Ba matsala duk inda kuke insha Allahu zan sameku a can din saidai ki riki wanan ibadan naki saosai diyata addua shine takobin mumuni Allah yasa albarka a cikin rayuwan ku ga baki daya.
A hankali na samu kaina da amsa mata da amin mama nagode ta kara da Allah yai maki albarka na amsa da amin again.
Komai yai farko yana da karshe akace yau gashi mun kare lafiya zamu tafi washegari kowa zuciyar shi cike da zumudin hakan.
Don tafiyan namu an kara kwanaki saboda yan kwanakin da yayi bai iso ba haka yai cuku cuku aka karawa tawagan nageria din kwanaki yakuma bi kowa da alheri mai tsoka a wurin.
Ban so sake haduwa dashi ba har mu bar kasan amma da gajiyan nan muna dawowa masauki sai ga uncle hamza ya kirani .
Wai mijinane yake son magana dani lokacin nayi mamakin jin hakan a bakin baffah din shi ba zai iya min magana ba ke nan komai da zai hadani da baffah a lokacin.
Wani wawan tsuki naja bayan mun gama wayan dashi lokacin na wurgar a gefena suka kalloni dafa inda suke zaune don wayan har yacin ma faiza lokacin.
Lafiya ta tambaya tana kallona idona daya cika da kwalla na sauke a kanta cikin takaici ina fadin jimun wanan mutumin fa wai uncle ya fadawa yana son ganina a yanzu zamuyi ban kwana dashi zai aiko a tafi dani masaukin shi.
Masauki ta fada tana kwalalo ido waje nace rainin hankaline nafishi iyawa yanzun nan zan gwada masa kuwa.
Da sauri na mike kanar ina shiryawa saida nagama tsab ne har faiza tana tayani tana fesa min turare .
Sai suuu na koma na kwanta saman gadon tare da dafe kaina ina fadin washh ina fadawa na fasa kara mai firgitarwa duk suka rude lokaci guda .
Yaren yarbanci na fara yi da sauri fatima ta nufi kofa sai dakin su umma take fada masu abinda ke faruwa.
Ai sai gasu tare hankali tashe sun shigo dakin namu tundaga kofa umma ta fara jin abinda nake fada tace dasu.
Ai mutanen kantane suka taka mata ashe har a kasa mai tsarki suna hawa kan mutum haka nan ta shiga shafana sai wani sauti nake sakewa kas kasa gaba daya duk wanda ke dakin zai iya jin hakan .
Hankali tashe mama ta kira su baffah tana fada masu yace yanzu fa muka gama waya da ita saidai dama naji muryanta ai wani iri can.
Sai gasu dakin suma a cikin tashin hankali sun shigo don baffah yazo da niyar ya fatatake ni ne sai ya samu abinda yafi karfin shi a dakin.
Sai gasu sun koma ban hakkuri jin har abinda bai taba fadawa wani yana da niyar yiba ana zakalo mashi da kaf labarin wurin aikin shi .
Da sauri ya shiga bada hakkuri yana fadin ba karya mun yarda daku mmdon munsan a kwaiku kamar yadda akai dan adam shima.
Nan ake fada mai ai yarsa na can kwance don shi ya tabo su ya batawa godiya rai ummace ke fassara masu duk abinda na fada a cikin harshen yarbancin wani kuma in yazo da turane suna jin abinda suke fada.
Text ya turawa mukhatar din yana fada mai abinda ke faruwa shima yaso daga hankalinshi amma baffah din ya kwantar mai da hankali.
Abinda basu sani ba shine turarena na shaka suka taso min don gaskiya na dade wanan matsalan bai taso min ba haka don gaba dayan su dakin ranan sun gaskanta hakan.
Sai dare sosai suka samu ya lafa min amma gaskiya koni nayi dana sanin yin hakan aiko da sassafe sai gasu har hjy tashi sun shigo gaidani ina kwance sharkaf dini don jikin da naji din.
Hajiyan tasu ke fadin kai tana da wanan matsalan ne haka dama umma tace ai yanzu ma yai mata sauki ke nan sosai sama ga da can baya.
Don tana kai sati daya tana fama da wanan laluran idan ya taso mata daga gefe baffah ke fadin ni ai na sheda yanzu.
No Wonder yarinyar nan take tsatsaye haka ashe manyan abubuwane haka saman kanta zancen yata data fada wallahi na kira suke fada min sati ke nan suna fama da ita sai jiyan nan suka baro asibiti.
Haka dai kowa ke fadan albarkacin bakin shi a wurin suna tsaye sun kura min ido kowa da abinda yake sakawa a cikin su.
Murya a sanyayye yake fadin uncle ko zamu daga tafiyan nan ne har taji sauki da sauri umma ke fadin yanzu data falka insha Allahu zata ji dama.
Zuwan daine na yanzu suka zo mata da karfi sai hjy nasu tace ai da kawai a dage idan sauran zasu tafi tunda sun shirya sai su tafi su.
Nagodewa umma data kafe da ai kawai a bari mu tafi zaifi koda an tsaya din ma duk abin dayane a can kuma za a samu a karbo min magani inda ake karba ai.
Da haka suka yarda da zancen umma har muka samu a ranan muka baro kasa mai tsarki zuwa gida nigeria.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ANA DARA GA , , , , , , , ,
1️⃣0️⃣1️⃣BY, , , , , , , , , , , ,
ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , , , , , ,
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AL, MUQSIT , , , , , , , , , , ,
ONLINE PAID NOVEL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA BA TARE DA HAKKIN KOWA BA DON BIYA KI TURA DARI BIYAR 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK 08036959257
ALLAH SARKI AI RAINA BAYA BACI YANZU DON KIN FITAR DON NASAN AKWAI RANAN HADUWA SEE U 👋
Kwance nake tun dawowan mu bawani karfi a jikina abubuwa da dama suka hadu suka sauke min rashin kuzari lokaci guda haka.
Saukin abin dai shine saukan dare mukayi washegari kuma da safe su baffah suka dauki hanyar kaduna basu kwana ba sai muka koma mu kadai a gidan kuma.
Idan badon tafiyan mu da Abdul bane ba wanda zaisan mun je har kuma mun dawo din