Showing 360001 words to 363000 words out of 382072 words
tayi turus a cikin mamaki tana kallona har zuwa idarwana data kasa hakkuri tace yaya akai hakane anty tana kallona.
Dan murmushin yake na sake a fuskana kafin nace mata nima dai hakan na gani yanzu nake mamaki don ba alaman wanan matsalan a tare dani kuma yanzu ya dauke kamar banyi ba.
Zaune takai a cikin mamaki tana kallona kafinta nisa tana fadin na kawo maki abinci a nan ne kici ?
Don uncle tunda ya fita dazun har yanzu bai shigo ba shima abincin dai is ready nasan zaku so don fried rice ne with Chick meat muka hada.
Ke dawa na dago na tambaye ta ina kallon fuskanta tace wanan matar ta jiyace ta dawo yau ma tare mukayi aikin da ita yauma.
Fuska na bata lokaci guda don jin hakan data fada don ni sam yanzu ban yarda da kowa ba a wanan garin kuma haka zuciyana ya fara nuna min.
Wani abune ga hakan anty ta tambayeni tana kallon fuskana cikin sonta san komeye ya bata min rai a lokacin.
Nace a dan kasalance no ba komai zan fito na bata amsa ta mike ta fita a take zuciyana ya fara kawo min wani tuhuma nayi saurin kawar da zancen a raina lokaci guda.
Na dan jima ban fito daga dakin ba saida nayi sallah la,asar nafito a falo fatimace zaune ita kadai tana kallo lokacin dana fito din.
Da sauri ta dan yunkura tare da dagowa daga kwancen tana fadin kin fito anty nace ehh fatika sannu da hutawa dan dariya tayi kafin tace ga abinci can a dinning table an gama zanci amma ba yanzu ba na fada.
Hira mukayi sosai lokacin da ita wanda hiran ya shafi hiran gidan sune da yadda suke zama dasu anty Nabila sai banji dadin yadda take ban labarin ba a lokacin.
A takaice dai na fahinci cewa akwai wanan akidar ta zama dan uba a tsakanin su wai me wanan halin yake nufi na yan uba ?
Shine fa ya jawowa Abban mu rasa rai har saida yan uba sukaga sun rabashi da duniya ga baki daya saboda wani dalilin shirme nasu can akan dan uwa.
Shin a ko wani kabila akwai wanan halin yan ubancin ne da ake samu a yawancin gidaje ko dai sai a fulanin mu kawai ?
Dole in bincika in gano idan wanan halin a ko wani kabila akwaishi har ko idan hakane kowani kabila har haka suke to lalai kuwa ina da aiki a gaba kan irin mutanen dana shigo cikin su yanzu.
Gabana ne ya fadi sosai lokaci guda don tunawa da nayi da wani abu, lokacin daya wanda ya shafi rayuwata dana yan uwana.
Mikewa nayi zubur zuwa kitchen yayin da fatima tani da kallo kitchen din naje na samu matar tana aikinta tukuru kamar yadda ko wace mai aiki takeyi a gidan aikinta.
Na dan dade tsaye a bayan ta ina nazarin ta alaman motsin mutum taji a bayanta yasa ta juyo da sauri lokaci guda.
Dan razana tayi kafin ta kakaro murmushi a fuskanta tana gaidani na amsa saboda kusan itama naji ba hausane sosai a bakinta ba lokacin.
Juyawa nayi na koma falon don ban samu abinda nake nema a wurinta ba lokacin fatima ta fara fadin lafiya dai anty ?
Lafiya na dai mike kafatane da yai min nauyi a yanzu sai naga tayi murmushi tana fadin aida kina iyawa sai mu fita waje zuwa garden don a kwai garden babba a wajen gidan nan.
Ba matsala muje mana na bata amsa ta mike tsaye muka fice tana min jagora ita data san kan gidan a lokacin.
Wurin yana da kyau sosai da tsari ga kujerun roba masu kyau gefe gefen na wajen a jiye muka dan fara zagawa muna hiran yanayin wurin dana gane da kuma yanayin weather din garin.
Shine muka hango a tsaye daga kofan baya ta inda muka fito din ya tsaya yana kallon mu a cikin mamaki kafin ya fara takowa a cikin mamakin ganin yanayina a lokacin.
Muma juyowa mukayi muka nufi inda yake sai muka hade dashi har lokacin ya na a cikin mamakin ganin yanayi na ban mamaki don fuskanshi yanuna hakan kafin ya fara fadin.
Sahiba kinji saukine har kin samu fitowa waje ina can ina tunanen irin halin yanayin dana barki a ciki kafin in fita.
Anty kan taji sauki ai uncle don har sallah tayi dazun don nima abin mamaki ya bani wallahi ni har tsoro ta bani wanan abin haka da ban mamaki yake kamar ba ita bace jiya gwanin ban tausayi muka kwana da ita ba.
Sallah ya fada a cikin mamaki tare da kallona yana fadin how about the blood ya daina zuwane kuma ko a yanzu ko me ya kara dan kura min ido a cikin mamaki.
Ya daina ne ai tunda har tayi sallah fatima na magana kamar wata babban mace da tasan ta kan duniya din nan kamar zaiyi magana sai kuma ya koma fadin.
Muna can munje wani waje amma hankalina yana nan tun dazun ashe Alhamdullahi sauki ya samu masha Allah.
Dan sunkuyawa nayi irin yadda yarbawan zamani keba na gaba dasu girma a yanzu cikin stly ina fadin you're welcome .
Thank you ya fada a sanyayye yana mai dan sake fuska da nuna wani yanayi har lokacin a fuskanshi dana kasa ganewa.
Uncle Bataci abinci ba tana jiran ka tun dazun nayi mata tayin abinci tace ba yanzu ba nasan kai take jira ka dawo kuci tare fatima ta fada a cikin zolaya ya kallo inda nakw da wani mamaki a fuskanshi ya kalloni a inda nake tsaye yana fadin.
Ba kici abinci ba kina jirana madam ya fada cikin mamaki tare da kara karasowa gab da inda ni nake tsaye cikin mutuwan jiki?
Har lokacin idon shi na kaina ya sake fadin keda kika kwana baki da lafiya haka don kawai naga kin samu barcine sosai da safe yasa bamu tafi asibiti dake ba a yau.
Yanzun ma na dawone naga yanayin ki idan zamu tafi mu samu wani likita a nan ya duba min ke da wanan niyar na dawo yanzu don naji tsoron yanayin dana ganki ciki jiya din.
Na samu lafiya na bashi amsa ina dukar da kaina kasa don haka basai mun tafi asibiti ba nagode daga haka na juya na nufi cikin gidan na barsu tsaye suna min kallon mamaki a wurin.
Nima naji tsoro kwarai amma kuma sai naga ita bata damu ba wata kila dai mutanen tane sukazo mata da wanan yanayin haka.
Don gashi kamar ba abinda ya faru da ita yanayinta ya nuna fatima ta fadi hakan tana kallon shi bai furta komai ba sai kai daya girgiza kawai yabi bayana itama ta shigo zuwa falon gidan.
Bai fita ba saida akai magariba ya tafi samujn jam,i a cikin jama,a muma sallah mukayi normal kuma nake har lokacin bayan ya dawone daga sallah muka zauna mukaci abincin dare tare.
A wanan lokacin ne mai aikin nan tace zata tafi gida alheri nayi mata tare da umartan ta tafi da sauran abinci abawa mubukata kada ya kwana ya lalace a nan din.
Tayi godiya ta tafi sai bayan fitan ta yake fadin a ina muka samo wanan matarne nace hjy ce ta turo muna ita ai.
Dan shiru yayi kamar me nazari kafin yace well tunda hjyce a barta amma ni nafi son a samu namiji da zaifi koda a bangarekune .
No banda ra,ayin me aiki sam a rayuwana don wanan din ma banga matsala a wurinta bane kuma tana da tsabata da kula yadda ya kamata.
Don bakin mu da baifi na mutum goma zan iya girka muna abinci ai a kullun na fada sai ya kalloni da sauri yace No ba zakiyi girki ba sam wanan din ma da kikayi a yanzu na barkine don in dandana hannun ki naji kalar girki a yanzu ai .
Meye amfanin dukiyana iyalina basu huta ba koda yaushe nafi son naga iyalina suna hutu suna jin dadi nima na zo garesu na sauke gajiyana a wurin su ya karasa yana min murmushi a fuskanshi.
Sam ban fahinci me maganan shi ke nufi ba don haka ban dauketa da wani muhinmanci ba shima din kuma ya gane hakan gareni sai ya share zancen bai fita mun dan taba hira.
Daya shafi mahaifina yadda suka hadu dashi har ya zama yaron shi saidai hiran bai kai ko ina ba don dan kukan dana fara a cikin kunan rai da jin daci a zuciya.
Haka yasa shima jikin shi yai sanyi bai iya karasa min labarin ba ya barni sai kuma ya dauki waya daga wata kasa yana amsawa shine ya tayar damu a wurin na mike zuwa dakina.
Lafiya kalau na kwana a ranan shima ganin banda lafiya yasa bai nemini ba ya share yadai leko dakin ina barci haka yasa ya gane ni kadai ke kwana a dakin ba tare da fatima ba.
Washe gari bayan mun karya yake fadin karfe hudu in shirya zamu tafi gidan hjyn shi tare da hjy falmata dukkan mu ukun zamu hadu a can.
Sam banji komai ba a raina sai cewa kawai nayi Allah ya kaimu ya fita don ana jiran shi a waje nagane dai koda yaushe shi busy yake da mutane da aiyukan shi dama na saba da ganin irin hakan tun wurin oga Shaaban .
Ranan kuma nayini yin baki suna shigowa ganin amarya don haka ban wani zauna a daki ba lokacin saidai masu zuwa idan sun fita zasu fara fadin ance bayerabiyace amaryan gashi bamuga zubin yarbawa gareta ba ai.
Akan lokaci nayi sallah na shirya har fatima don yayi min waya mu hadu a can din driver yana nan ko yaushe a gidan idan muna da bukatan hakan.
Hudu daidai ba saba lokaci muka dauki hanyar gidan hjy har me aikin nan nawa da yanzu mun dan fara sabawa da ita.
Gaba daya yaranta da yan uwanta suna gidan lokacin hakan yasa na gane abu mai muhinmancine ya kawomu gidan ke nan wanan zuwan.
Mun shiga an kuma taremu a cikin mutunci tare da jagoran sister muka isa falon hjy suna zaune su hudune a falon har kasa nakai na gaidasu suka amsa muna gaisuwan a cikin mutunci.
Kafin na samu wuri nan kasan na zauna da sauri suke fadin haba sahiba a kasa ga kujera dai kya zauna kasa kuma no nan din yayi Mah, na fada.
Baifi minti biyar da zaman mu ba muna nan zaune cikin ladabi sai gashi ya iso nan naga irin so da kaunan da yan uwa ke nuna mashi sisters din shine su hudu suka sakashi tsakiya sai shagwaba suke zuba mashi.
Haka harya zauna suma iyayyen kamar zasu lasheshi kowa dai mukhatar kaina na sade kasa shima idon shi a kaina yake duk hiran da suke da babban yarsu lokacin.
Dan dago kai nayi na gaidashi fatima ma hakan ya amsa a cikin sakin fuska da jin dadi tare da tambayan mu ba matsala ko kai na dan girgiza mai alaman ba komai a lokacin.
Sukaci gaba da magana da yan uwanshi wanda mu bamu san me suke fadi ba din ba yaren da muka iya sukeyi ba su can ya dan ja tsuki tare da fadi yana kai fuskan a kan
Duban agogo yayi yaja tsuki tare da fadi a cikin yare ita falmata me take jirane bata karaso ba kuma na fada mata yanzuma da zan taho.
Sai wajan kamar minti goma sha biyarne sai gata ta iso a cikin kasaita da isa da takama da izza suka shigo falon da yan uwanta dake mara mata baya.
Kowa dake falon ya bita da kallo waya takeyi a cikin isa da takama ta kai zaune ba tare da gaisawa da kowa na falon ba, suma yan uwan suka zauna saman sauran kujerun suna gaidasu hjyn a cikin isa.
Kaina nadan dago na kallesu kafin na sada kan nawa yadda nake zaune ta gama wayan ta dago tare da fadin gani yare ya fara yi wanda dagani har fatima bama jin me yake fadamata lokacin .
Amma kana gani kasan fada yake mata itama amsa ta bashi tare da kallonsu ta gaidasu a cikin yare zaka fahinci akan gaisuwa ne wanan maganan idan kana da hankali yadda abin ya faru lokacin.
Fatima ki fita ki jiramu a wurin sister na fada ta amsa da to da sauri ta mike zuwa waje din kowa ya gane me haka ke nufi a cikin turanci na fada.
Falon yayi shiru na dan lokaci kafin ya kalli yan uwan nata yace dasu su bamu wuri zamuyi magana fuskan shi a daure.
Kamar ba zasu tashi ba don sai wanan ta kalli wanan wacan ta wani ya mutsa fuska tana kawar da kai gefe daya sai karamar ta fara mikewa ta fita.
Idona ya tsaya akansu duk abinda sukeyi ina kallonsu lokacin kafin su mike don kallon da yar uwan nasu taimasu suka mike da sauri suka fita ko a nan ma na samu wani hit daga garesu ke nan .
Boyayyen ajiyan zuciya na dan sauke tare da dukarda kaina kasa a daidai lokacin muryan hjy mama ya ga hjyn su uncle take sallama ga kowa na falon.
Aka amsa mata taci gaba da fadin mun taru a nan ne don murna da samun karuwa yar uwa a cikin kuma abokiyar zama tare da yin nasiha ga juna son a zauna lafiya a taru a rufawa juna asiri tare dayin zama na amana da juna.
Excuse me ta fada tana mikewa da waya a hannunta da alama wai wayan zata karba da sauri ya dakatar da ita da fadin koma ki zauna.
Wani irin kallo ta watsa mashi kafin tace zan karbi wayane a ban yan mintuna indawo shima a hasale yake fadin a magana kike fadin zaki karbi waya yanzu?
Wanan ai abune da muka sani gabaki dayan mu ba tashigo cikin muba a yanzu zata iyane yasa ta shigo don haka meye na wani zaunar damu a nan kan wanan maganan da mama ta fada.
Kowa nan yasan me ake nufi da zaman aure ai don haka ita ai ba yarinya bace idan tazo da zaman lafiya matsalan tane udan kuma tazo da wani manufa duk a daidai muke so ni ina da abubuwa a gabana yanzu .
Wanan ba zai zaunar dani nan ba muna batawa juna lokaci tashigo gidan ka fine shike nan mu zuba kawai a kan ka nida ita .
OK haka kikace tace na fada saita juya wurin yan tsofin tana fadin mama kuyi hakkuri ni zan tafi wanan ba maganan da zaku zaunar damu nan bane yanzu.
Tunda baku iya zaunar dani ba kafin ayi auren ku fada min zai kara aure kuji ra,ayina ba yanzu da komai ya faruwa ba ace za a zaunar damu tare ai muna wani nasiha.
Zaiyi magana kanwar maman shi ta daga mashi hannu tare da fadin barta ta tafi Allah ya bada hakkurin zama ke sahiba ki zauna lafiya da mijin ki jeki Allah yayi maki albarka ya baku hakkurin zama sauran aka amsa da amin.
Kaina dago tare da fadin nagode mama na yunkura na mike tsaye tare da masu sallama na fito na barsu a falon.
A yadda na samu su sister a wajen rayukan su a bace da alama sun ji yadda ta fadawa iyayyen su maganganun banza a falon.
Gaidasu da zama nayi kafin nacewa fatima mu tafi mukai masu sallama muka fito zuwa gida wurin mota muka nufa kaina na a duke yake ina kallon hanya.
Sai naji a dan firgice fatima na fadin gasu fa a wurin motan mu anty ta fada a dan firgice na dago kai sune tsaye suna magana a hasale.
Saidai suna hangomu duk hankalinsu ya dawo garemu wani kallo suke muna tun daga nisa har muka karasa excuse me na fada don su jaye a wurin.
Sai duk suka juyo suka kalleni lokaci guda a cikin rashin damuwa na karasa wurin jikina saye nake a cikin wani dogon riga ja baja sosai ba rigan kamar feated yake don yana da dan sharp da dogon hannu sai v neck da akaiwa aikin zare na yafa dan kwalin rigan a wuyana.
Sai takalmana masu tsini sosai high hill mai tsawo da igiya kana ganina kasan nasan ta kan lagos da kyau ko daga shirina ya nuna hakan duk da gidan saruka danazo
Kai tsaye na nufo inda suke din fuska ba sauki zan bude motar saidai basu jaye a wurin ba har lokacin, , , , ,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ANA DARA GA , , , , , , , ,
1️⃣0️⃣8️⃣BY, , , , , , , , ,