Showing 366001 words to 369000 words out of 382072 words
ya rufe yanzu anzo aci banza dole ta dauka daidai take da kowa tanzu banza kawai masu bin arziki da gudu kinyi kuskure wallahi.
Har lokacin wani murmushi na sauke tare da fadin No warder naga kowa da kowa naku kun maida gidan mijin yarku gidan ubaku har uwarku da kowa naku kun dawo kun tare a gidan mutumi kun hanashi shakat a rayuwanshi.
Kun hana danginshi su morewa dan uwansu kun hana kowa nasa ya rabeshi yaji dadin a innuwarshi yanzun kuma kuna bakin ciki da hassada nazo nima naci arzikin nasa.
Koda yake talauci yana saka hauka ba mamaki ga irin rayuwan da kukeyi na dabbobi ko wani dabban ma yafiku tunane da sanin ya kamata don dabba baya abinda kukeyi harda yar taku jaka.
Ehh lalaima yarinya wanan kin tarowa kanki much yau, dama gargadi kawai mukazo muyi maki ashe kina takama da karamin barikinki a hakan kema.
Kinyi gaskiya wanan dama nasan karamar yar iskace ta lafene kawai don ta samu shiga dayar ta fada daga gefe tana wani tafa hannu kamar taga abin mamaki har lokacin duk basu farga da mun kule kofa ba fatima da suwaiba mai aikina suna tsaye daga kofa a cikin tsoron abinda zai faru.
Amma gaskiya kunsan in munyi wani abinda ba daidai ba a gidan nan ran ya mukhatar zai baci damu wallahi don Allah ku bari mu fita lafiya yadda muka shigo karamar daga cikinsu ta fada a dan tsorace ta kara da fadi a cikin yare Gila gila.
Ayyah sorry sister ki barsu suyi abinda suka zoyi zasu samu duk kala abinda suka zo dashi gidanan a yau na fada sai ta tsakiyan datafi fitsara tayi wani shewa tareda tafi tana kara matsowa inda nake tsaye.
Kamar ban san me take ba a lokacin ina kallon biyun dake gabana a lokacin tana zuwa kusa dani hannu na daga saijin saukan mari tayi kawai a kumatun ta saida ta sake wani kara da karfin Allah lokaci guda.
Kafin suyi wani abu nasa kafa na tadiyo babban nasu sai gata a kasa ta buga goshi da baki a saman ties ya fara fitar da jini lokaci guda.
Dayan tayo kaina kafin ai haka tayi kasa na bita na haye muka fara fadan mata biyun sukayo kaina duk da ina saman yar uwan ban kyalesu ba suma don ina kai masu nashi da shuri duk wace na samu sai dayan dake tsaye tana kurma ihu duk abinda muke wayana a kunne yake yana dauka tunda nayi saitin shi lokacin da suka shigo suka fara iskanci.
Danbe sosai nayi dasu duka hudun lokaci guda amma Allah bai basu galaba a kaina ba lokacin jin wani irin karfi nayi yazo min sai bugun mai uwa da wabi nake kai masu a lokacin.
Dukan kofa da akeyine yasa muka dan dakata saboda na sheda muryan sister ashe Fatima ce ra tura mata text massage suzo ba lafiya gasu sun kawo muna attack a gida.
Duk yadda akayi na kyalesu na kasa sai binsu nakeyi muka fara zagayen gida cikin tashin hankali an rasa wanda zai rabamu a lokacin .
Har yakai sun nufi wurin kofan nabisu haukace suka fara ihu a cikin tashin hankali suna neman taimako ranan kan basu ba duk wanda ke wajen yayi mamakin ya akayi na iya masu dukan wulakaci haka su duka uku.
Dabara Fatima tayi ta samu bude kofan har aka samu shigowa gidan da kyar da bani aka samu kwatansu a hannu na da kyar aka jani zuwa dakina aka samu fita dasu.
Sai kuma ga yar nasu hjy Falmata tazo wai a barta tashiga tayi maganina don me zanyiwa kannenta haka kuma ace wai mutum daya tayi masu wanan dukan haka kai ina gaskiya da sake.
Kafin ace hakan har labari ya fara karada gari an fara fadin abinda ya faru ana kari a kai ga kuma video da fatima ta turawa Sister suka sake a median ya fara yawo nan zancen ya karade ko ina ko lokaci guda.
Hankali a tashe ya shirya zuwa Nigeria sai hjyn su ta dakatar dashi akan kada yazo don in yazo ba za,ayi mai dadi ba wanan yasa ya fasa zuwa saidai munyi waya dashi ya bani hakkuri kan abinda ya faru.
Tare da jamin kunne kan kada in kara irin haka da kowa na bari idan sunzo sai na kirashi yasan abinda zaiyi shi ko yanzun ma ba zai kyalesu ba.
A haka dai har maganan yazo ya lafa bayan tayi barazanan ta da borin sai tayi karana kan wanan matsalan shi kuma da taji yace tana karana daga can ta tafi gidan su.
Naje gidan mu fa kace baban yusura yace kwarai ki tafi gidan ku daga kotun sukai dan sa,insa dashi a karshe yace idan bata dawo ba ta zauna kuma kada ta dawo mai tare dasu gidan shi gaba dayan su.
Tashin hankali da jidalin ya karu ta dauki haka da wasa suma sai hankalinsu ya tashi sosai da jin abinda ya fada nan dayan take fadin aina fada maku kada kuje gidan da fitina kukace aje a saka mata tsoron a zuciya.
Yanzun ga abinda ya biyo baya mu din ai bamu san haka take yar daba ba da bamuje ba sun rasa yadda zasuyi gashi itama yar uwan nasu ta fara juya masu baya a yanzu .
Don yarsu hafsat data zaunar da ita ta lurar da ita kuskuren da suka tafka daga ita har yan uwan nasu takuma bata shawara kan su yarda girman kai suje gidan da sunan sunzo ba hjy hakkuri kana su suce zuwa har gidana daga nan.
Da farko sunso suyi mussun hakan har ita hjy falmata din amma kowa yace hakan dai zasuyi ai aidukawa wada ba rage tsawo bane ga mutum a faki gaba dani dasu ai yanzu aka fara wasan.
Da wanan shawaran suka bi sai gasu har gidan da misalin karfe biyar na yamma a lokacin tare da ita hjy hafsat din data kawo su saidai ba hjy Falmata a cikin su.
Wani tasha na yarbawa da nake bin season dinsu tun a tv duk ranan laraba ina zaune a falon gidan nake kallona hankali kwace sai ga sun shigo anyi nocking suwaiba ta nufi kofa ta duba ta samu ai sune sukazo.
Don dama mun sanda zuwansu shiya kirani sister kuma ta kira duk sun sheda muna zuwan su ya fada zasu zo su ban hakkuri ne kan abinda ya faru tsakanin mu.
Don haka banyi wani abu na nuna masu rashin hankali ba don mutuncin matan da suka shigo dasu gidan a lokacin muka gaisa dasu cikin mutunci da girmanawa.
Ta fara koro magana na katseta da fadin do me, i do you so no base me i no wan wahala gyare .
Duk kallona sukayi na nuna masu cewa banda tsoro ko fargaban fitina koda da namijine don haka fada dashi na bude ido da ban iya ba ban amsa suna yar geto ba a yanzu.
Ke na nuna dayan ai kafin kuzo nan sai da friend dinki ta fada maki cewa kada kizo amma kika nuna kinfi karfin barin fada maku ko sister din ku aiken da tayo min yana nan dawowa gareta indai ni sahiba ce bata san ko wacece ni ba ta barni a inda ta gani kome tayi zai koma a kantane.
Allah dai ya sauwaka yar nasu ta fada tare da kara bani hakkuri na nuna ai komai ya wuce a wuri suka fita bayan sunyi muna sallama.
Kallon naji ta fita raina a lokacin don haka na mike na shiga dakina ban kara fitowa ba sai washe gari don ba yadda fatima batayi dani ba kan na fito naci wani abu naki fitowa a ranan.
Haka hjy Falmata ta shirya ta koma inda ta fito tare da tawaganta da sukazo bayan taga duk wani abinda take ganin zatayi wanda zai min katanga da maigida.
Data sani ta barwa Allah idan muka zulunce ta sai Allah ya isar mata tun a nan duniya amma ta kasa hakkuri ta barwa Allah lamarin tayi ta addua a gare shi.
Sai ubangiji ya dorata a kaina idan nazo mata da wani cuta ko ha,inci a cikin rayuwana idan kuma babushi sai yasa mu zauna lafiya a tsakanin mu.
Amma gagawa aikin dana sanine daga baya idan kana da rabo a wajen ubangijin ka sai kayi daka sani baka kaucewa Allah ba.
Sai labarin tafiyansu naji a bakin Fatima ita da take waya dasu sister lokaci lokaci wanan bai dameni ba tunda dama ba a gida daya muke zaune tare dasu ba.
Hankalina kwance nake rayuwana a gidan muna waya dashi lokaci lokaci yana kirana har mu danyi hira dashi ko ya rambayeni idan ba wani damuwa a tare damu nan maidugurin.
Har yakai wata daya da sati biyu lokacin yazo maiduguri koshi daga South Africa ya wuto zuwa Nigeria muna nan da yamma bayan magariba muka gashi ya shigo unexpected.
Ina dakina lokacin na idar da sallah ke nan ina shafa mai don nayi wanka lokacin dana shiga yin alwala dama na fito na tsaya yin sallah.
Ganin mutum kawai nayi a bayana tsaye yana rataye da suit din shi a kafadan shi sai farar riganshi yar ciki da hannunshi ke sama yana kokarin balle bottom din rigan daga sama a lokacin.
Dan juyowa nayi gareshi ina kokarin kama dan tawul din da nake da daura gaba dashi lokacin ina fadin you're wellcome ansan man dake hannuna yayi a hankali ya mayar saman mirrow din.
Zagayowa yayi zuwa gabana inda nake zaune kallon juna mukayi na dan lokaci na sada kaina kasa cikin nauyi da kunyarshi.
Kokarin mikewa nayi sai naji ya rikeni lokaci guda na dan kara kalloshi zaiyi magana na rigashi ina fadin let me dress my self first.
Sautin murmushin shi naji yana fadin ko kin manta cewa ni mijinki ne a yanzu haka nake son kallonki ya fada yana kokarin son mu hada ido dani dashi amma sai naki hakan.
Sai yakai hannu kamar zai kama ma daurin tawul din na jikin nawa da sauri na mike zubur sai ya rikoni gaba daya zuwa jikinshi lokaci guda yana sauke wani irin ajiyan zuciya tare da fadin baby i miss you.
Jikinane ya fara rawa lokaci guda ina kokarin janye jikina daga gareshi don a zatona irin wancan yanayin zai dawo min na ciwon mara da zuban jini shi nake gudun kada ya faru a yanzu din kuma dani.
Saidai har muka gama tsayuwa mu a wurin ya sakeni banji wancan bakon yanayin nawa ba da nakeji idan mun dan hada jiki dashi saidai hawayen daya dinga fita min daga idanuwana kawai a lokacin.
Wanda bansan dalilin zuwanshi ba a lokacin amma har yafita daga dakin hawaye bai daina zuba mi ba nasan bai kula da hakan bane a lokacin.
Da kyar na samu na saka riga a jikina na koma nayi rub da ciki kwance gashi ina son tashi naje koda falone amma na kasa yin hakan a lokacin.
Haka ya dawo ya sameni a cikin wani yanayi na daban da bai fahinta ba zaune yakai a kusa dani yana fadin na dauka akwai abinda zan samu indanci a yanzu.
Jin nayi shiru banko motsa ba a lokacin a yadda nake kwance yasa ya dan dubani da kyau saiya fahinci ai barci ma nakeyi a lokacin.
Dan bin dakin yayi da kallo bayan ya dago ko ina na dakin tsab yake kamar ba a amfani da dakin koba mutum a cikinshi dake rayuwa.
Ajiya zuciya ya sauke kafin ya mike ya fita ya hado tea da kanshi ya dawo dakin ya sameni yarda yabarni a kwance har lokacin yasha tea dinshi ya fita ya dan jima ya dawo ya rufo kofa tare da bissimillah a bakinshi.
Kafin ya jiyo ya dan tsaya tare da karato adduan tsari masu nauyi da tsayi yana tofawa a ko wani kusurwa na dakin nawa a hankali.
Duk kunnuwanshi sunji mashi kamar anja tsuki da dankarfi ko a hasale baisa ya dauki wanan wani abu ba a zuciyar shi.
Bissimillah ya kara tare da dan rage wutan dakin yana kaiwa zaune daga gefena tsukin ya kara ji anja da da karfin sauti tare da jin motsi kamar an taba handle din kofan dakin daya rufe din da da karfi da sauri ya dan kallo wurin saidai babu komai daya gani a wurin illa duhu a lokacin.
Wayan shi ya dauko a aljihunshi ya bude page alkur,ani mai tsarki ya fara karantawa a hankali yayi nisa sosai a cikin karatun shi sai ji yayi nayi wani irin mika da nishi lokaci guda tare da juyawa a yadda nake kwance da farko.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ANA DARA, , , , , , , , ,
BY ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , , ,
1️⃣1️⃣1️⃣
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM, , , , AL, BADI
YAR UWA KIJI TSORON ALLAH KI DAINA FITAR MIN DA NOVEL DON KIN BIYA KI BARI WANI YA BIYA SABODA ALLAH👋
Tsukin dai bai kare ba saidai a yanzu ya fahinci badaga bakina wanan sautin da yake ji yake fitowa ba haka yasa yakara kaimi a wurin daga sautin karatun nasa.
Sannu a hankali ya fara jin numfashina yana komawa normal haka yasa ya fahinci cewa bani kadai bane a lokacin yayi mamakin hankan sosai a zuciyanshi dama ashe da gaske akwai wanan matsalan ashe ga al,umma ?
Bai daina karatun da yakeyi a lokacin ba sai gabanin asubahi sosai shima barci ya daukeshi saidai lokacin sallah yanayi ya falka ganina mane a jikin shi na dunkule a wuri daya da alama sanyi ko tsorone a tare dani lokacin.
A cikin dabara ya zare jikinshi daga nawa ya mike zuwa bandakina nan ma ya tsaya yana bin ko ina da kallo kafin ya daura alwala ya fice zuwa sallah.
A daidai lokacin da aka tayar da sallah lokacin na falka a cikin mamakin ina duban yanayin lokaci na biyar saura na safe a lokacin mikewa nayi da sauri kada in makara ga sallah.
Sai bayan na idarne na lura da alaman mutum ya kwana a dakin nawa lokacin don waya da jakkashi na laptop dake saman gado a lokacin ga wasu takardu da agogonshi duka a wurin.
Mamaki naji sosai da ganin haka har yaushe ya shigo dakina ya aje wanan abubuwan kodai a nan ya kwana na tambayi kaina ganin ba amsa yasa da sauri na juya na kalli inda zan samo ansa din sai naga alaman dai mutum biyu sun kwana a wurin.
Da sauri na mike na isa zuwa wurin da nake zargin an kwanta din babu abinda ke tashi lokacin sai kamshin turaren da yake amfani dashi.
Mamakine ya kara kamani lokacin how comes har ya shigo dakina ya kwana a nan ban sani ba me yasa ya kwana a dakin kuma ranan ?
Ban kaiga karasa tunanena ba sai gashi ya shigo dakin da sallama shi fuskanshi kuma yana nuna mamakin gani a tsaye a laman har na idar da sallah ke nan a lokacin.
Ahankali na juyo na sauke kallona gareshi tare da kaiwa kasa ina fadin good morning uncle morning ya bani amsa tare da fadin how was your night Alhamdullahi na fada ina dan jada baya kada jikin mu ya hadu da nasa.
Zama yayi a bakin gado tare da daukan kafanshi daya ya dora saman gadon ya dan bubuga gefenshi da yake zaune tare da nuna min inzo in zauna.
Dan jim nayi kafin na iya dago kafata zuwa bakin gadon nakai zaune a gefen shi dan shiru yayi yana duban wayanshi kafin can yace ki fada min abinda kike gani a cikin mafalkin ki inji ?
Cikin mamaki na dago na kalleshi kafin in maimaita tambayan da fadin in my dream ?
Ya lumshe idanuwan shi yana fadin yes akwai abinda nake son in gane a game dake yanzu dan shiru nayi don ban san ta ina zan fara fada mai abinda yake sonji din ba.
Mafalkin me kiyi a daren jiya daya baki tsoro kika firgita suwaye suke binki haka a cikin mafalkinda ya zamo ba mafalki bane zahirine ?
Da sauri na dago kaina na kalleshi yace yes zahirine ba mafalki bane kawai kikeyi haka don tareshi nayi da fadin I know wanan yanayin da nake gani sabone a gareni.
Amma duk da hakan ba nasara ga maishi son muna buga fada sosai da abinda nake gani din a yanzu barshi kawai maishi zai koma mashi insha Allahu a kwanan kuwa.
Kallona yakeyi har na kare zance na ba wani alaman tsoro a tare dani lokacin kara maimaita min tambayan yayi nan na shiga fada mashi abinda nagani yana bina da kokarin son daukan wani abu a cikin jikina da karfin tsiya.
Shiru yayi na dan lokaci kafin ya nisa yana fadin insha Allahu komai zaizo karshe ina jin dadin yadda baki fadawa kowa matsalan dake damunki din a cikin haka har