Showing 27001 words to 30000 words out of 382072 words

Chapter 10 - ANA DARA COMPLT BY MAKAWA

MAKAWA   

29 Jun 2024

28419

him for dat.
Ai mun gode ko hakan wallahi Allah dai ya saka da alherin sa ta karasa fadi da hausa tana zama a bakin gadon don ganin ba cutar damu sukazo ba.
So u servi hausa ma self ki karbi kudin nan don na baki wanan ba komai bane a wuri nayi niyar taimaka maku ne don jin halin rayuwan da kuke ciki a gida a bakin mutanen gidan.
Don haka don Allah ku karbi kufin nan kiyiwa yaran amfani dashi Allah ya sada mu da alherin sa don ba lalai bane mu kara haduwa kuma saidai yarana zasu dinga duba ku lokaci lokaci.
A gadarance gashi duk da bakaken kayane sai kyali sukeyi kayan sun hade da fatan jikin shi chakulete colour .
Yana da tsayi gami da kirji mai fadi kiran zaki gashi da dan tsayi da alaman jiki kuma don Allah ya bashi kyau kira ga zati a gaban duk wanda ya tsaya.
Ga wani saje da mazan zamanin nake ajewa yanzu da suke kira da one million a fuskan shi ya kara masa kyau.
Basai ya fada ba duk wanda ya ganshi yasan shi din wani ko acikin dubu don zan iya cewa komai ya hada ban sanarwa na imani ba da bangani a fili amma kan kudi sun riga girma yawa a wurin nan.
Duk maganan da yakeyi da umman mu idona yana a kansa ina karewa halittan Allah kallo don yawan kallona har saida na gano fuskan shi na ainihi duk yana ganin shi ya rufe don a duke nake har lokacin don haka zan iya ganin hakan daga kasa.
Don da nasan kiyasta shekaru a lokacin wanan ba zaifi ashirin da wani abu ba a duniya don yarone a iya sanin matasan legos da nayi ko tsoho mai hurhura yana dabi,un yara sai in kira wanan din da yaro.
Na sake fadi a raina kyau da kudi ga kwaliya da kwarjini duk Allah ya tarawa bawan Allah nan sai dai kuma ya kaza don miskilin karshe ne shi.
Da gani ga girman kai nan a fili da jiji da kai da yake nunawa a fili yana nuna shi din wani ne a gaban kowa tun ganin farko da nayi masa.
Har ya juya ya fara tafiya bayan ya umurci a ajewa umma kudin a gefen ta a inda take zaune ta zuba masu ido cikin tsoro da fargaban su don basu da tabas.
Kowa yayi shiru umma na ganin sun soma tafiya tace na rokeka kada ka zama min sabon matsala a rayuwa .
Wani irin juyowa yayi har zuwa gaban umma din ya dan kalleta ya sake dan murmushi kafin yace.
Mama nayi domin Allah ne don abinda kike tunane ba hali mu bane iyaka mu muna neman na kan mu ne da zufan mu.
Idan kuma munga mai bukata mu taimaka masa don ya sakawa harkan mu albarka don gaba Allah ya kawo muna sa,a a rayuwa.
Me yuyuwa daga yau na fada maki kila ba zaki sake haduwa da muba balle har wani abu ya biyu baya na asha don haka ki saki ranki niba mugu bane kamar yadda kike zato.
A lokacin ya dan cire hulan daya rufo a kanshi ya kalleta da kyau tare da hada hannayenshi wuri daya kamar mai rokon gafara kana yayi wani abu kamar bissalam da hannu tare da dan rankwafawa daga haka suka juya suka ffice sauran suka bi bayan shi da sauri.
Ina ganin haka na mike da sauri na rufo kofan dakin tare da saka sakata na dawo inda umma tayi mutuwar zaune don ko motsi bata iya yi ba har lokacin sai bin kofa takeyi da kallo inda suka fita.
Umma idan baki yarda dasu ba ki kawo kudin nan yanzu inbi bayan su dashi duk inda suka shiga a garin nan.
Sai lokacin umma tayi wanin irin ajiyan zuciya tare da kallona tana fasin ke din Sahiba kike fatan in barki kibi wa yan nan da suka tsaya gabana kamar mala,ikun duniya.
Maza ki samu wuri ki koma ki kwanta saidai muyi adduan nufin su yazama alheri a garemu amma ba zan barki ki bi bayan wa yanda bansan asalinsu ba ko daga ina suka fito.
Umurnin umma din nabi cike da fargaba a zuciyana na samu wuri na kwanta a makure ina faman tunane sai gizo fuskan shi da ya tsaya min arai ya ke mun a lokacin.
Ina ganin kyawawan maza ban taba ganun mai kyau irin nasa ba a rayuwana har barci ya daukeni a hakan.
Washe gari nikan na makara da sallah saida umma ta tayar dani a gurguje nayi sallah namike ina gaida umma da kwana kafin na fara tattara kayan da muka dan bata na fita dasu wurin wankewa .
Tunawa nayi dana hjy na shiga dakin da sallama na samesu a ciki na gaida su a cikin ladabi nake tambayan mai jiki suka amsa da sauki
Nake fadi nazo na kwashi kayan na wanke masu ne don zan tafi na wanko namu a famfo.
Allah sarki yar albarka wallahi keda ai jiya an tafi dasu gida a wanke a can saidai cup din nan da suka sha tea da dare dashi.
Na duka na kwasa na fita yau kan ban dade ba son yanayin dana tashi cikin sa ba dadi don haka ban kula kowa wirin ba nayi abinda ya kaini na bar wurin.

Yanzu ya kike so ayi don ban fahinci inda zancen ki ya dosa ba ya dago yana fadi tare da kallon inda hjy karima take tsaye.
Eh akan zancen Abubakar daine nace kai masa magana idan zai bamu kyauta ya rika bayarwa ta hannun ka sai taja tayi shiru.
Ya dan dago ya kalleta yace uhumm ina jinki cigaba mana tace a, a shine dama nace zan ma magana don ka kafa wanan dokan .
Eh lalai karima tunda gani dattijon banza ko don kawai in farauta maki rai sai inyi bakin jini ga iyalina saboda ke kece ko ?
Wai karima ina tunanen ki yake zuwa kwanan nan ne ko dai wani abu na faruwa dakene ba a farga ba ta jefo mai wani irin kallo tare da fadin .
Watau na haukace ke nan ba a sani ba ake zaune tare dani hakan kalaman ka ke nufi yanzu Alh don kawai na fadi gaskiya shine laifi ?
Hakan nake nufi kin taba jin inda akaiwa uwa da danta shamki don kawai wani ko wata yaji dadi a rayuwan
Yau ko cewa Addah tayi ya daina baki kudin shi ga baki daya ai ban tambayan ta dalili don datane ita ta haifi abinta.
Balle ya bada sakon har abaki kike ganin kamar Addah ta rage ko bata son a baki din ko wani abu don haka zaki zo wurun dattijon banza ki izani in saba masu ko ?
Ai dama nasani nasan haka zaka fada Alh haka dinne ai har kin sani kuma kika fada min yanzu ?
Ta wani mikewa tana fasin ni in ma kyautan ya zama magana daga yau a bari don Allah ai ba rasa kudi nayi ba a hannu na.
Ina da aikina ko yanzu naga daman komawa sai in koma yace badai gidana ba keda aiki sai idan baki gidan nan.
Don Allah yaga halinki na boye da kika boye min da farko ya kareni daga fita aikin ki tun farko kyautan kuma abarshi zan fadawa modibbo din.
A daina sai me zaka wani lauyeni kace nace matar kana ragewa ko wani abu can don hadin fada ta fita daga dakin.
Tafita tana dan kunkumi don dabaranta ba soici ba gashi kuma zata kulawa kanta tsiya a gidan kan hakan.
Dama shawaran kawace data bata tace ta gwada duk ranan da maigida ya kwana da ita har ya nuna jin dadin shi gareta to ita kuma ta gwada sa,anta a wurin miji ga abinda take bukata .
Acewar kawar a take miji ke biyawa mutum bukatan shi a wanan lokacin don kawai jin dadin kasamcewan su a tare da suka raya dare suna sunna.
Shine tayi kokarin gwadawa gashi kuma ita batayi sa, a ba abin yana neman kwabewa da ita ga baki daya a yanzu.
Dakin ta nufa kai tsaye wurin wayan ta taje ta kira kawar ta nan take labarta mata komai daya faru tsakanin ta da Alh.
Wani irin tsukin takaici taja tana fadin Allah karima ke banza ce waya fada maki da safen nan ya dace kiyi wanan maganan dashi ?
Ai tun jiyan ya kamata a daidai lokacin da abin bai gama fita masa kai ba ke kuma saiki sako zancenki ki gani.
Sallaman da taji daga kofa yasa ta katse wayan tana amsawa tare da fadin waye hjy nice Talatu dama wai nazo na fada maki Alh karami zai tafi.
To sai akace me to hjy babba ce dai tace nazo na sanar maki Allah kai lafiya mana ko ta fada adan hasale.
Talatun ta amsa mata da amin ta juya ta tafi yana zaune kannen shi sun dan mane suna rokon shi kudin anko yana ja masu hankali da hakan talatu ta dawo.
Yanayin fuskanta kawai hjy Adda ta kalla tasan da akwai bacin rai a lokacin saidai bata nuna hakan ba don cewa da tayi Allah saukeka lafiya zata shiga wankane yana jin hakan ya mike tare da fadin .
To mommy ni zan tafi ke nan sai kuma Allah ya sake hadamu da alherin sa uwar ta mike da sauri a cikin yanayin rashin jin dadi da tafiyan da dan nata zaiyi a lokaci.
Modibbo Allah ya tsare ya kare muna ku a duk inda kuka shiga ya dawo muna da kowa lafiya shi da kannen sa suka amsa da Amin.
Sai lokacin ya kalli kannen sa yana fadin to ni zan tafi ko sukace aaaa yaya gaskiya ka ganmu kafin ka tafi.
Wani gani kuma zan maku bayan wanan gaskiya mudai ka ganmu yana dariya ya saka hannu ya ciro kudi masu yawa mika masu suka hau murna da Allah ya tsare Allah ya kiyayye a cikin murna .
Nabila ya kalla yace nasan su Amira ba barci yanzu basu tashi ba idan sun tashi sai ku basu wanan suma su sayi alawa suka ari bakin yaran suna mashi godiya.
Haka ya karasa inda daddy ke tsaye yana magana dasu malam mudi ya dan kai rusunne yana fadin daddy zan tafi ke nan .
Dafa kafadan shi mahaifin nasa yayi ya mikar dashi yana fadin ka gama da yan rikicin can ke nan yace wallahi daddy .
Na dai sallamesu ai mun rabu lafiya yanzu yau su Amira basu fito ba ke nan eh daddy naba Amira nasu ta basu idan sun tashi.
Dan murmushi mahaifin ya sake kafin yace ka kyauta dan ko yanzu nasan akwai rikici idan sun tashi sukaji ka tafi ai .
Cikin dabara ya fara tafiya da dan nasa don su bar wurin dasu malam mudi suke tsaye ma,ana zaiyi maganan siri dashi ke nan.
Ganin hakan suma suka ja suka dan tsaya daga nisa dasu kadan sai da suka danyi kamar tako biyar suka tsaya har lokacin hjy da yaran ta na tsaye daga kofa suna kallon su.
Don jira suke suga tashin shi su koma cikin gidan haka ka,idan rakiyan su yake idan maigidan na gida iya kofa suke tsayawa.
Yanzun lagos din kuma zaka koma ya dan murmusa kadan yana fadin can zamu koma daddy don yau akai min waya sun gano mai wanan sunan.
Allah ya bada sa, a ya amsa da amin ya kara fadin ka kula da kanka don Allah irin wanan aikin nasan hatsatin dake cikin sa sai anbi a hankali.
Daga yayi mai fatan nasara ya juya ya dagawa mahaifiyar shi hannu tare kannen shi ya nufi motar da za a kaishi airport dashi.

Likita yazo round ya duba Amar din yaga ya samu sauki sosai don haka yace zai bamu sallama zuwa yamma idan yaga yadda jikin nasa yakara samun sauki.
Ranan umma ta dan daure ta fita har ta shiga gaida hjy nan datake taimaka muna tun haduwan mu da ita.
Sun dan dade suna hira tana jan umma da dan hira sai dai duk dabaran ta umma bata yarda ta fada mata komai daya shafi rayuwan ta har ta fito.
Ta samemu zaune muna hira da Amar din dake zaune saman kujera tana shigowa dakin nake fadin umma kinji danki ko .
Wai keke za a saya mashi idan mun koma gida da kudin nan wani irin kallo umma ta watsa muna kafin ta juya ta kalli kofa ta koma da sauri ta rufo kofan ta dawo wurun mu duk muna binta da kallon tsoro dan yadda tayi din.
Ku saurareni kuji a binda zan fada maku dukkan ku a yanzu kada inji wanan zancen a bakin kowa duk tambayan da wani zai maku akan zancen yaron nan daya bamu kudin nan kuce baku sanshi ba.
Mena fada maku muka amsa da bamu san shiba har muna kada kai kada ku nuna tsoro a fuskan ku ko kadan don nuna tsoron ku zaisa su dauka mun sanshine.
Shiru mukayi gaba dayan mu na dan lokaci kafin can na dago ina fadin umma wani abune kuma yanzu ?
Babu komai jikinane kawai ke bani cewa akwai abinda bamu sani ba a game dasu kawai nayi shiru ina tunane saidai na kasa gano komai a yanzu.
Dakin yayi shiru na dan wani lokaci kuma kafin Amar ya mike ya koma saman gadon ya kwanta.
Allah ya gani nice duk silan jefa umma a cikin wanan halin damu kan mu ma yanzu idan wani abu ya samu umman mu fa ina zamu saka kan mu na tambayi kaina.
Dakin aka turo likitane tare da nurse suka shigo ya dan kara duba jikin yaron kafin yace zai bamu salama sai mu tafi gida.
Najin dadin jin hakan don na matsu mu bargidan saida likitan ya gama bayani ya mikowa umma wasu kudi yana fadin canjin mu ne da suka rage ta bamu kudine kuma masu yawa.
Saida muka shiga mukaiwa hjy nan sallama take tambayan umma lamban waya umma tace bata da waya ita ai.
Tana mamaki take fadin har da ke nayi murmushi tace a kwatanta mata gidan mu wata rana zata kawo muna ziyara.
Nan dai mukai mata kwantace ko ta gane ko bata gane ba muka kara gaba abin mu muka barsu a asibitin don sukan basu san ranan sallama ba sukace.
Kamar ba asibiti muka fito ba don yan gidan ba wanda yai muna an dawo lafiya ya maijiki.
Karshe mu muke gaidasu da u na weldone su amsa muna a gadarance da thank u jo mu wuce har muka kai dakin mu da har lokacin a hargitse yake.
Umma taga yadda aka tone dakin wurin bincike ta tsaya nikan ban tsaya ba dole na shiga gyaran dakin namu don ba zamu iya zama haka ba dakin a hargitse.
Nan dai har na gyara suka koma ciki ni kuma na dan tsaya waje ina wanke wasu kayan mu a lokacin ne naji gudu na dago don ganin me akewa gudu din.
Yan sandane cikin wani irin kaya mai ban tsoro suka shigo gidan yasa kowa ke gudu zuwa dakin shi ashe.
Nima na shige dakin mu na mayar da kofa da sauri na rufe suna shigowa gidan mukaji ana sanarwa kamaf haka.
Mun san kana cikin gidan nan don haka ka mika wuya a cikin saukin kai a hankali na kalli umma ina fadin wa sukazo nema umma ?
Bakina ta kaiwa duka tana fadin inyi shiru da surutun tsiya can mukaji na banke banken kofan muka kara make junan mu mu uku a dakin a cikkn tsoro har suka kawo dakin mu da ba wani kofan kwarai ke garemu ba dama.
Wani dan sandane ya shigo yana fadin ku shigo kofan a bude take ya shigo babu dadin gani yana bin ko ina da kallo.
Har kayan mu ya dan dadaga ya fita yana fadin bai wanan dakin karshe suka tataro kowa na gidan dayan su ke nuna muna photon wani guy yana fadin mun san wanan kowa yaba hirgiza kai mukace bamu sanshi ba.
Wani tsawa ya daka kowa ya firgita yace a gidan nan yake har tsawon mako hudu yake nan ma shiriru akayi ba wanda yace ya san shi a gidan.
Sunyi iya binciken su basu gane komai ba har suka aikinsu da yan tambayoyi akace ba a sanshi a gidan suka gaji suka tafi bayan sunce zasu sake dawowa


ZAINAB IDRIS MAKAWA



qANA DARA GA , , , , , , , , , , ,

1️⃣0️⃣

BY ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , ,

BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM WA, LAL DALIN AMIN, , , , ,


YAR UWA PAID NOVEL NE DON ALLAH KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DARI BIYAR NE KACAL YAR UWA.

Hankalin mu bai kwanta duk da sun


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login