Showing 54001 words to 57000 words out of 382072 words

Chapter 19 - ANA DARA COMPLT BY MAKAWA

MAKAWA   

29 Jun 2024

28348

yanzu sosai don ni sai nake ganin kamar kamamu har umma yake son yi kan wani laifin da bansam dashi ba a lokacin.


ZAINAB IDRIS MAKAWA



ANA DARA GA, , , , , , , , , , ,

1️⃣7️⃣

BY ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , ,

BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AL QUDDUS, , , , , , ,

PAID ONLINE NOVEL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA ACIKIN SALAMA DON ALLAH KI TUNA DA HAKAN NAUYI NE A KANKI BABBA, , , , ,

Addu,an ku nake nema ubangiji Allah ya yaye muna matsalolin mu Allahuma amin, , ,

Wanan yar ko aljanace dai ya tambayi kanshi yana zaune bakin gado cike da mamaki isowan shi ke nan daga garin don kiran gagawa da akaimai cewa ana tuhumar shigowan wasu kaya da yan fasa kwauri zasuyi da shi a cikin daren ranan yasa ya baro kaduna ya shigo lagos din a ranan.
Duk da daddy yayi matukar fada da rashin zaman shi ta huta tare da amaryan shi da kwana biyu ke nan ras da kai mashi ita a gidan shi.
Zai tsiro da wani zance na ana neman shi a cikin gagawa har daddy na fadan cewa aikin bai taso ba sai alokacin da kake hutun amarcin naka modibbo suna wanan zancen ne kwatsam aka sake kiran shi a gaban daddy din nauyin bayanin da daddy yaji sunayi ne ya barshi ya garzayo lagos din.
Daidai shigowan su ne sukai kicibis da Sahiba wace yake mamakin ganin ta a wanan unguwan kuma har ta iya masu wayau ta bace masu lokaci daya haka.
Lalai wanan yar tana da abin al,ajabu a tare da ita ya ba kanshi amsa yana mikewa tare da alwashin koma wa take sai ya gano ko ita din wacece dai.
Kayan jikin shi ya fara cirewa a hankalin yayin da wayan shi ya dauki kara lokaci guda wurin sa yake tsaye ya baro zuwa bakin gado inda ya bar wayan nasa da sauri.
Don a zaton shi ai yan uwan aikin nasa ne suke neman shi a wanan lokacin sai yaga bakon nomba ya dauka.
Ya kara a kunen shi ba tare da yin sallama ba yaji muryan mace a cikin muryan kuka tana fadin ka tafi ka barni ni kadai a gida a daidai lokacin da nafi bukatan ka fiye da kowa a duniyan nan.
Dan tunane ya tsaya yi kafin ya gano yarinyar nan ne amaryan shi ta kirashi sai mamakin inda ta samu layin shi na boye ya kamata don shi yasan ba kowane keda wanan layin nasa ba a kasan nan.
Yana sauraren ta duk ta gama iya shegen ta lokaci guda tana wani shagwaba da maganganun da bai saba jin su a bakin mata yan uwan shi ba sai wanan lokaci.
Abinka da wanda baida lokavin soyayya a tare dashi sai cewa yayi ki bari ai zan dawo ya kashe wayan nasa yana tsuki tare da fadin.
Kawai an hadashi da wani nauyi a yanzu kuma yana fama da kanshi haka za a dauko laluran wata a dora mashi kuma cikin rayuwan shi.
Don shi abinda ke gaban shi kawai yanzu shine aikin daya shigo dashi kasan nan na yan fasa kwarin kayan da kasa da hukuma basu yarda ana safaran su ba a ko wani kasa.
Ina ganin na bace ma ganin su na dafe kirji ina furta thank god dey no cachi me waitin i do again dis solder wan cachi me again ?
Ban yarda na koma gida ba duk da tsoron da naji sai da na samu na sayar da katina na nufi gida tare da yan tsarabun dana sayo muna na amfani dama kaddara ya kaini wanan unguwan kuma Allah ya kareni garesu na kara fada.
Na shigo gidan wuraren takwas saura don yanzu yakai umma bata faye tayar da hankalin ta ba a kaina ban fada mata komai daya faru ba a lokacin.
Saidai a ranan nayi saurin kwanciya barci don kada umma ta fahinci halin damuwa da tunanen da nake ciki a lokacin.
Washe gari na falka tun asuba nayi sallah roban da nake diban ruwa na dauka na nifi famfo duk saida na cika kayan mu na debi ruwan na fara shirin barin gida.
Zuciyana yana cike da fargaba don in akwai abinda dan lagos ke tsoro sune soja ko dan sanda ko malam bahaushe.
Don su sojawa nan takene sun wullakanta mutum lokaci guda shi kuma dan sanda yanzu ne zai ja maka kashin kudi bahaushen mutum kuma dan takifene shi bai damu da duk abinda ya samu ya kare ba a wurin fitina.
Da sauri na watsa ruwa kamar yadda na saba yin wankana idan na shiga na fito dan mai na shafa sama sama kafin na jawo wani bakin dogon riga na roba dake tsaya min iya gwiwana nasaka na jawo takalma mai belt nasa hula na figo daga gefena na kakabe na rufawa kaina shi.
Kan da ya dade bai samu gyara ba sai dai na daba masa hula in fita kawai kitson duk a dankare don tsufa.
Dan jakkar baco dina na figa yayin da nake gyarawa kwagirina wurin zama a jikina da kyau na kalli umma dake zaune ta kura min ido duk abinda nake idon ta yana a kaina nace zan tafi umma.
O Allah Sahiba Allah ubangiji ya tsare ya kare muna ke kije lafiya ki dawo lafiya a cikin amincin ubangiji.
Allah ya duba muna wanan wahalan rayuwa da muke ciki ya kawo muna dauki a rayuwan mu nace amin umman a sayayye idona kamar zai fitar da hawaye na juya na kalli kanina dake barci abinshi hankali kwance nace a gaida min shi idan ya tashi nasa kai na fice daga gidan ina tunanen inda zan dosa a ranan.
Agege nan ya fado min a rai duk da ban faye son wanan wurin ba a rayuwana don haka nake shawaran zuwa Alaba ko agege din har nakai wurin bus stop ban yake shawara a raina ba a lokacin.
Tun ban karaso ba nake jin ana ihun agege din bus ya cika don kada in batawa kaina lokaci kawai na fada bus din agege din da sauri na mika kudin bus muka kama hanya.
Tun dana sauka bus nake bin ko ina da kallo ina nazarin abinda zan danyi a wanan yanki in samu kudin da nazo nema din.
Wata mai shago na nufa dake sayar da kayan sanyi na tambayeta idan zata ban sari in dauka matar da alama tana da fada don yadda na samu tana jidali da wani wanda ya rigaji zuwa tana kafa mai dukoki tsarinta na daukan kayan ta.
Amma haka na daure nace ta ban sari na bata kudin ta na dauki minerals din na hada da gyada soyayya na kama yawon tallata a kai.
Buy miniras buy dry g\nut nake fada ina bi layi layi a saman hanyan naji ance miniras da sauri na juyo zuwa inda aka kirani din su ukune zaune cikin mota baka da alokacin ban san sunan taba.
Dan nisa na tsaya dasu don duk yawon tallana idan ba akan go slow bane bana yarda in kai bakin mota mai maganan yace cock na juyo da sauri ina kokarin dauko goran cock din na kuma daga nace how many ?
Bring two and one sprite na aje da sauri na dauko na dan nufesu ina mikawa aka miko min dubu daya nace i don't have change.
U want me to go and find change for u nace na naw i start selling it oga i don't have one thousand naira change.
Dan mai karamin jikin ne a cikon su muke magana dashi sai na tsakiyan da kanshi ke duke yana aiki cikin computer ya dago kai yace dashi ya amsa don Allah su wuce.
Har ya duka sai kuma ya kara dago kai da sauri ya dan kalleni sai ya mayar da kanshi yana gyara hulan kanshi facecap daya dan rufo mai fuska.
Ban damu da hakan ba sai cewa nayi make give u dry g\nut with d change oga it sweet i swer ina dan daga hannu banji abinda wanan din yace mai ba naji yace oya bring d nut we are in hurry ya fada yana kokarin tayar da motan kama suna a uzurce da sauri na juya na kirgo gyadan a leda na kawo masu ina fadin thank u oga my god bless, .
Kai d nut is too much for us woo ya fada shi mai jan motan nace aina canjin kune duka na zuba maku yace dan dauki kullin da baikai biyar ba ya miko min sauran har na daga naga ana miko min kudi daga bayan motan na dago ina kallon mai shi dayan yace take naw, .
Na mika hannu na rawa na karba suna tayar da motan yace gret ur mama nd ur broda for me na kara kallon shi da kyau ina tunanen ina na san shi nasan fuskan shi kafin na kuma mayar da idona kan kudin masu yawa dake hannuna.
A daidai lokacin dana tuno shi har sun tayar da motan su ko a lokacin sun harba kamar walkiya sun bar wurin na busu da kallo ina tunanen idan nasan lalai shine shine naba kaina amsa a tsaye da kudi a hannu na masu yawa da ban san adadin su ba.
Da sauri na cusa kudin a cikin kwagiri na na tura ina dan waige waigen mutanen dake wucewa a wurin bai fi minti biyar ba sai ga wata mota da sojoji da yawa sun tsaya.
Suna bin mutanen wurin suna tambayan su game dasu nikan ina ganin haka nayi saurin bin wani hanya saidai duk yan sandane sun kewaye a wurin ga baki daya ashe.
Duk yadda ka iya dabara sun hana kowa motsi a wurin suna nuna photo mota suna tambaya ina tsaye sororo da kayan ruwana a kai ina kallon ikon Allah har suka gaji suka fada motocin su ta gabana motocin ke tafiya ina binsu da kallo don mun saba ganin tashin hankalin dayafi hakan ma fitina a garin.
A hankali shima ya dago ya bini da kallo saidai wanan karon da zance a bakin shi don hannun daya daga min irin na warning kada ki bari mu hadu din nan duk da sauran mutanen wurin da muke tsaye duk sun dauka dasu yakeyi a lokacin yana bada warning ne a kansu hakan.
Muna tsaye har suka gama wucewa kowa ya shiga harkokin shi kai tsaye kafin ace haka nikan na canza wuri ga baki daya nabar shiyan zuwa wani gun na sayar a cikin lokaci don haka ban tsaya a agegen ba kuma sai kawai naji ranan inje gidan hajiya halima in kai mata ziyara.
Na mayar da kayan dana dauka haya na yi mata sallama tana fadun bazan kara bane nace da idan zan tafi gobe zan dawo.
Na samu hjy a gida tayi murnan zuwana mun gaisa a cikin dadin rai ta tambayeni ummana da Amar nace duk suna lafiya.
Abinci tasa aka kawo min naci saida na koshi nace zan wuce take fadin tun yanzu nace eh da akwai kuma ida zan tafine yasa zan wuce din.
Tace in jirata tazo ina zaune ne nake jiyo muryan maza suna shigowa gidan ban damu in san kosu waye ba har suka shigo suna dan hiran su na gaida su a cikin turanci suka amsa min tare da zama a falon duk sai naji na takura da hakan.
Gashi ban taba matsawa daga falon ba ban ma san kan gidan ba ga baki daya don haka na zauna a takure suna magana akan zancen kayan da suke tuhuma din an shigo dashi.
A lokacin kuma hjy ta fito daga ciki dauke da leda a hannun ta ja tayi ta tsaya wuri daya tana fadin wa nake gani nan kamar ango a zaune ?
Ya dan dago kai tare da kallon ta yana murmushi ya fara gaida ita mijin ta na fadin wanan angon ai an kwareshi don baiyi hutun angwancin nasa ba a dole ya dawo bakin aiki ba shiri.
Sin dan dade suna magana yayin dana shiga zurfin tunane don ina tsuntan wani abu a cikin zancen nasu da sukeyi da hausa.
Naji hjy ta ambaci suna tana fadin sorry Sahiba mun barki a zaune ko gashi kina sonki tafi nayi murmushi ina mikewa tsaye.
Take fadin gashi ki gaida maman ki zanzo wata rana idan Allah ya yarda ya kawar da kai da sauri kuma ya juyo inda nake tsaye din.
Ya mike da sauri yana nunani a cikin mamaki tare da waro ido wajr yace you a razane nima na dan ja kusa da hjy na tsaye cikin tsoro suka bimu da kallon mamaki dagani har shi.
Sai da hjy ta miko min leda take fadin kasantane a cikin hausa komawa yayi ya zauna shima tare da dan basarwa ai kafin suyi haka koda hjy zata juyo bana wirin har na fice da sauri ba tare da mun tsaya munyi sallama da ita ba a lokacin.
Cikin mamaki ta kara kallon shi tana fadin kasan wanan yarinyar ne sai kuma ta juya wurin mijin ta haroon tana fadin itace muke baka labarin su da muka zauna asibiti tare.
Abubakar yace itace daddy ya zo nema kwanaki garin nan duk su suka hada baki wurin fadin itace suna tambaya yace itace sai dai gaskiya a yanzu na fara tsorata da yarinyar nan gaskiya ko dazun fa a agege na ganta tana talla anya ma mutunce kuwa wanan din.
Hjy tace mutum ce don nasan har mahaifiyar ta da kanwarta mun zauna a asibiti daya dasu ga kwanakin bayan kanin ta baida lafiya.
Da sauri suka bi bayana saidai ko mai kama dani basu gani ba a wajen sun rasa hanyar dana bi na tafi sai mijin nata ne ke tambayanta kisan gidan da suke zaune ne ?
Tace nasan dai inda tayi min kwantace a baya don yanzu sun ajagule sun koma semi boda a can suke zaune yanzu ta bashi amsa.
Da sauri ya kawar da zancen da fadin yanzun dai sunyi nasaran shigo da kayan kasan nan ta haramtaciyar hanya illa iyaka abinda zamuyi shine musan su waye wa yan nan masu kayan kuma wani jaha aka kai kayan a yanzu.
Sun dade suna tataunawa da haroon din kafin suyi sallama ya mike don zuwa gida zuciyar shi cike da tunane kala kala.
Nima haka na isa same ina son fadawa umma komai ina tsoro fadan da za ayimin din a lokacin don nasan yadda umma ke fada idan ranta ya baci dani.
Don haka na faki idon umma din na fice zuwa waje can na samu wuri na fitar da kudin na kidaya sai da gabana ya fadi ganin dubu dari cur din su ya ban ashe da kuma dubu dayan dake saman kudin da suka sayi abu wurina da dayan ya bani.
Jikina har yana ciri na mayar da kudin a cikin gwagirina danayi dan mara dashi ko ina nake bana rabuwa da shi a jikina dama don tsaro.
Ai kuwa ina shiga umma ke fadin ina nafito nake cewa na manta ban sayo muna maganin sauro ba da muma magani insha na shige kawai abina na kwata cike da tunanen mafita garemu.
Tabbasa shine wanda ya taimaka muna da asibiti kan matsalan Amar da yanzu yaro ya samu lafiya haka kuma umman nawa itama tayi lafiya sosai do manyan maganin data samu tana amfani dashi yanzu.
Wurin ya cika sosai da masu tashen arziki yan kasuwa da masu smogling din shigo da kayan nan Nigeria.
Sune zallah a wurin suka taru don nasaran da suka samu kayan su ya shigo lafiya ba kamar yadda suka zata zasu samu matsala ga hakan ba.
Tun daga wajen wurin zaka gane hakan don irin manyan motocin da suka cika a haraban wurin taron nasu da sukeyi a ranan.
Don duk wani dan kasuwa daya amsa sunan shi shi a nan suke hadu suna taron su idan hakan ya taso.
Gidane babba na gani na fada da kayan more rayuwa a cikin sa suka hada a wurin kana gani kasan kudi yasha kashi a wurin hada ginan nan.
Ga security nan ta ko ina tun daga bakin layin a banza har mazauna unguwar sun da haka don idan zasuyi taron su kowa na wanan unguwar yana natsa kanshi ne.
Don yawan security din dake zama wurin saboda tsaro da kariya ga ubangidajen nasu don wata rana fada kan barke a tsakanin su yasu yasun su har ajiji ciwo ko rasa rai duk da a yanzu sun shawo matsalan hakan a tsakanin su tun bayan shigowan yaro karami a cikin su yanzu wanda yake kamar jagora a garesu.
Bayan wa yan nan katai din yan ko ta kwana din ga wasu tsalalan yan mata a wurun suna


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login