Showing 210001 words to 213000 words out of 382072 words
mujiya.
Sahiba aikin ku na tafiya kamar yadda ya dace dai ba matsala ko sai lokacin na dago daga inda nake saman kujera a gaban dinning din na dan kallo shi ina murmushi nace.
Ba matsala saidai halin mutane ne sai an fito masu a inda basu zata ba don basu da niyar bamu hadin kai muyi aikin daya kawo mu.
Kenan sai kun hadasu da hukuma ko wani abu makamancin hakan zasu dauki abin serious sosai haka nake tunanen yi a karshe .
Baida matsala tun farko na fada maki ai idan da abinda zan taimaka maku dashi dai ki nemeni na danyi murmushi ina fadin lokacine baiyi ba na neman ku idan yayi zamu neme ka mun gode.
Nidai ban yarda na fadi komai ba cikin zancen su don sai naga zancen manya ne bai shafeni ba ai.
Mikewa tsaye ya don tafiya bayan ya dan duba agogon sau barkatai umma tayi maigodiya da kulawan shi a kan mu ya fice daga gidan har saida ya tayar da motan shi na sauke ajiyan zuciya a hankali.
Bayan tafiyan shi zancen su da umma ne na auren baby ya tsaya min a raina akan me za ayiwa baby aure ga su anty Nabila da anty hauwa a gida.
Amma sai baby din ce zatayi aure toshi wanda zata aura din waye shi waye mahaifin ta kuma danaji suna magana akan shi.
Shi kawai nake son sani dan haka naji kawai duk yadda za ayi zan halarci wanan bukin da zasuyi a gidan su saidai ta yaya zan tunkare su gida.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ANA DARA GA , , , , , , , ,
6️⃣2️⃣BY, , , , , , , , , , , ,
ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , , , , , ,
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AL BA,ITH , , , , , , , , ,
ONLINE PAID NOVEL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA BA TARE DA HAKKIN KOWA BA DON BIYA KI TURA DARI BIYAR 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK 08036959257
ALLAH SARKI AI RAINA BAYA BACI YANZU DON KIN FITAR DON NASAN AKWAI RANAN HADUWA SEE U👋👋👋👋
Zaune nake da tulin takardu a gabana ina aiki yayin da hankalina ke kan Laptop dina ina ina tura sako a cikin sa muryan oga Balane a office din yashigo a gagauce yana fadin anzo za a ganmu a lokacin.
Ban dago kai na kalle shi ba sai aikin da nake faman yi haka sauran duk wanda ya dago ya samu ina aiki sai ya duka yaci gaba da abinda yakeyi kada ya samu kuskure a cikin aikin sa.
Ya sake fadin Alh da muke hurda dasune a wanan company sukazo su ganku ayi maslaha a tsakanin mu dasu don sun samu labarin hakan.
Ka fada masu cewa ba kawo kansu ba a yanzu idan lokacin hakan yayi ai zamu gaiyaci mai hannu a cikin harkan nan yanzu muna tattara bayanai ne shine aikin mu.
Wanin kallo yayi min na banza kafin yai kwafa ya fita yana fadin yarinya baki san wuta ba sai kin dafa an gaya mamaki su Alh wasa ne komu don dole muke biye dasu ai.
Daga waje ina jin yadda suke surfa min zagi na ashar da cin mutunci murmushi na sake a fuskana ina godewa Allah a kullun.
Ita wacece waye ubanta a cikin kasan nan da za mu tako har nan tace bata shirya ganin mu ba a yau sai lokacin hakan yayi zata ganmu.
Bello dake jin hausa da sauran biyun suka dago kansu suna kallona don sun san danaji irin zagin da Alhazawan ke min dole zan tanka masu.
Don ago bala da zai fita yabar kofan a bude yadda zamu iya jin komai da ake fadi a wajen hakama suma zasu iya hango wasun mu daga cikin wurin.
Mikewa nayi kawai na nufi kofan kai tsaye su hudu ne manyan mutane saye da manyan riguna a jikin su dukkan su.
Daga bayan su sukaji muryana a daidai lokacin da oga Bala ya shake murya yana kara zugasu suko suna hawa ga mutane sun taro dan nisa kadan kowa na kallon ikon Allah.
Niyar ubanace da aka haifa a hanyar halas kamar ko wani dan suna na kwarai lokaci daya dukkan su suka juyo suna kallon inda nake tsaye ina fitowa daga office din.
Kallon mamaki kowan su ke mun don a cikin hausa nake magana gani saye a cikin suit kai da hulla daya boye gashin kaina a lokacin zakace no din wata kabilace da ban taba jin ko zo in kashe ka ba da harshen hausa.
Ba zamu ganku ba yau din nan don bamu tsara hakan daku zamu zauna daku ba sai idan bukatan hakan ya taso a garemu don haka idan kunga zaku iya tafiya sai ku tafi.
Dukkan su hudun kallon mamaki suke min na karanta da ganina na cewa nanjin hausa gashi inayi naku kama da ruwan fulani don da ka gani kasan yar wani nake a cikin kasan nan na hausawa.
Juyawa nayi na shiga office din na zauna naci gaba da aikin da nakeyi saidai banjin zan iya karasawa don yadda zuciyana yake hasala.
Daka zagan min uwa ko uba gara kayi ta zagina sau ba adadi zan iya hakkuri da hakan amma idan ka tabo min iyayye yanzune zaka jini.
Ai kafin mu fito labari ya gama karade ko ina na ckkin company cewa ashe yarinyar nan tana jin hausa kamar jakar kano don yau ta wanke su oga bala dasu Alh Buhari sosai.
Ni dai mun fito naga ido yayo kan mu caaa don inda sabo mun saba da hakan ai don sun nuna muna tsarguwa da kyaman kasancewa dasu wurin a filin Allah.
Figil figil nake tafe a cikin saurina da yar jakat laptop dina sai dan wayana dana riko a hannu na mun nufi wurin da motan Adnan yake don shi ya dauko mu har yemisi zuwa aiki yau.
Saiga manaja ya biyoni da sauri shida oga Bala a baya da waya duk mukaja muka tsaya lokaci guda muna kallon shi.
Yake fadin madam na dole badon yaso ba ga waya don Allah ki karba Alh ne ke son magana dake a wayan kallon wayan nayi kafin sauran abokan aikin nawa su kalleni.
Waitin concer me with him bada wani hadi da kowa a garin nan na fada mashi kuma nasan na cikin wayan yana jin mu a lokacin da nake zancen.
Alh kaji abinda ta fada ai yace yi kokari ka bata wayan yanzun nan kada ka bari ta daga baka bata ba don jin hakan yasa nakai hannu na karbi wayan tare da fadin .
Assalamu Alaikum, ba oga bala ba duk wanda ke wurin saida ya kadu lokacin don nuna alaman ni din musulmace ashe ?
Kada kadamu Alh ka dai kara shiri don zamu hadu da yardan ubangiji dakai lokacin hakan baiyi ba a yanzu sai anjima na mika mai wayan shi.
Figil na wuce shi na bude gaban motan na shiga na zauna tare da gyarawa naja kofan na rufe zuwa lokacin idanuwana suna canza kalla badon komai ba sai jin muryan wanda nafi tsana a cikin duniyan nan.
Wanan wani sabon masifane haka ke shirin faruwane yarinya karama nason tayi muna yawo da hankali haka a cikin garin mu.
Naga ko lagos indai akace harka damune suna tsoron hakan amma wata banzan yarinya can yar isk, , , , tarine ya sarke Alh a lokacin bai samu kai karshen maganan shi ba da zai fada.
Sai mika hannu yake faman yi wurin goran ruwan dake aje da sauri suka miko mashi goran ruwan ai yana kai bakin shi kamar an kara mai tarinne lokaci guda.
Rudewa wa yanda ke falon sukayi sai sannu suke masa yana amsawa da hannu koda kai sai da kyat ya lafa mai ya koma yabi kujera yana mayar da numfashi guda guda ga wani irin zufa yana karyo masa a goshin sa.
Ganin ya samu sauki yasa su masa sallama suka tafi sai kanin sa Buhari da babban dansa ne suka zauna a tare dashi basu tafi ba lokacin.
Sai bayan mintuna ya dago kai ya kalli kanin nasa yana fadin anya Buhari wanan yar bata zo muna da shiri ba kuwa yau nice yarinya karama haka ke fadawa magana haka.
Dan nasa ne dake kawar da goran ruwan a gaban shi ya juyo ya kalli uban yana fadin wace yarinya ke nan baba ?
Hannu ya daga mai yana fadin sanin hakan bai shafeka ba yanzu Dan hjy zancen sana, an mune yazo da matsala shi mukeyi.
Au daka nayi yar harkace take son ta kawo maku matsala ai yanzu nayi yaga yaga da ita cikin garin nan jeka nace uban ya fada wa dan a fusace ya fita badon yaso ba.
Kallon kanin shi buhari yayi yana fadin yaron nan ya kawo zance fa a nan buhari kasan ni ba a shiga hurumina a fita baki alaikum sai kasan ka shiga zance na ka raina kanka da kanka wallahi.
Yaran nan yan daba zan hada da yarinyar nan su hake mata zata san muna ba a kawo muna zancen banza a zauna lafiya.
Eh to gaskiya shawarane maikyau hakan amma kuma ni sai naga gara dai abi zancen nan sannu a kare lafiya ban faye son irin abubuwan nan yanzu sam wallahi.
Lokaci yayi garemu da za ace mun daina wasu abubuwa da zasu hanamu kwanciyan kabari lafiya gara dai muji da irin barnan da muka tafka na kurciya a tubawa Allah zaifi.
Allah bashin mu samu maslaha dasu idan ma biya su kudaden su zamu a zauna a san ta yadda za a basu kudin su tunda hakkin sune muma mun sani.
Kai tir da halinka buhari yanzu wanan dalilin yasa yanzu ban komai dakai wallahi dadin gyade ke nan da badon kafan nan nasa da makiya suka lalataasa shi yaki lafiya gareshi ba wallahi baka ma sanin halin da muke ciki.
Wai kai ko ka manta da zancen inna ne da ta tayar damu dashi takan fada muna kowa ya shiga gaban kada mu tausaya masa ko muji kanshi mu buge ko kashewa idan yakama mu kashe din.
Kai haba yaya zaka hada lokacin su inna da wanan zamanin da musulunci yayi karfi a ko ina a dai duba zancen don Allah abi sannu.
Kallon kanin nasa yayi yana gyada kai yace eh lalai buhari ka nuna min ka shiga izzala yanzu kan ashe ba karya bane da ake fadin kakai yaran ka makaranta masu dagagen wando karatu hakan ko gaskiyane ashe ?
To yaya baka ganin komu irin wahalan da mukeyi na rashin karatu da bamuyi ba yanzu zamanin nan fa da ilimin addini dana bokon yake tafiya dashi a rayuwan mutum.
Eh to yanzu kan na gane inda ka dosa buhari saidai kada ka manta ba a sakewa tuwo suna a duniyan nan yayi murmushi don gane me yayan nasa ke nufi yace Allah gafurul rahimun ne ai yaya abinda aka aikata a baya ya wuce yaya ?
Harda kashe yan uwa da mukayi a tare a baya kana ganin zai yafu a garemu ne ga Allah ya dukar da kanshi kasa jikin shi yai sanyi yayan nasa yaci gaba da fadin ko kana ganin wanan din baifi komai barna a cikin abinda mukeyi ba yo na kashe nawa nahau dukiyan shi waye zan bari a yanzu kuma ?
Dago kai kanin nasa yayi yana fadin da ace zanga iyalan Sambo a yanzu zan duka in nemi gafaran su tare da fada masu gaskiya in kuma basu kason da kuka ban a ciki koda kuwa ya kama na mallaka masu dukiyana a baki dayane yanzu in koma banda komai a hannu na.
Ido ya kura mai na dan lokaci kafin yace dashi yau daba kai bane buhe da wanine yayi wanan zancen haka a gaba ba abinda zai hana in halakashi a duniyan nan.
Sai dai kuma kai dinne saukin abin kuma ina zaka gansu a yanzu mutanen da boka ya fada muna sun dade da mutuwa a hatsarin mota wurin gudun mu ina kuma zaka gansu a yanzu baki nawa ya fada muna hakan cewa sun dade da mutuwa ko.
Har itama mairo din yan uwanta a yanzu sun gaji da nemanta dole sunyi hakkuri da hakan ai tunda abinda mukai masu ka manta dako suna raye ba zasu taba waiwayan gidaba ma balle ka gansu a yanzu ?
Mikewa yayi yana fadin shi zai tafi amma dan uwan nasa yadai kara dubawa kan wanan shawaran daya kawo a karshe.
Bai dago kai ya kalleshi ba kawai yasa kai ya fita sai lokacin ya bishi da harara yaci arzikin uwarsu daya da kuma abinda inna ta fada da zata mutu da ranan yasan koshi waye shima.
Dan nasa ya dannawa kira a waya tare da tambayab kana inane yace gani nan zan tafi tudun wada kazo ina son hanin ka ya fadawa dan nasa.
Idan mun fita umma takan kunna kira,a ya tayata hira tana bin karatun haka na dawo na sameta ita kadai a gidan .
Gaida umma kawai nayi na fada saman kujera tare da dafe goshina da hannuna daya na lumshe idanuna ina tunane.
Ganin haka umma ta kira sunana na dago kai na dan kalleta kafin na cire hannun ina kaiwa kwance nace umma yau nayi waya da wanan mutumin .
Wani mutumi kenan fa umma ta tambayeni na sake fadin wanan Alh Nuhun wan mahaifin mu a ina kika ganshi ta tambaya cikin mamaki ?
Dagowa nayi daga kwancen da nake ina fadin kusan kudin company da muke nema yana a hannun su sun rike haka bincikena ya nuna min.
Saidai ban yarda munyi magana dashi a yau na fada mai ya jira har lokacin haduwan mu dashi yayi.
Haka kikace dashi nace kwarai umma ban shirya haduwan mu dashi a yanzu don haka ba zan tsaya magana dashi ba ko mai zai fada min kuwa.
Kibi a sannu don mutanen nan basu da kirki ko kadan sanin koke waye a garesu yanzu zai kara saka masu tsanarki a zukatan su .
Da ace tun farko nasan suna cikim zancen nan babu abinda zaisa na yarda ki fara aikin nan mai yawan kasada a rayuwan ki yanzu.
Nasan da hakan umma nima saida muka zo din nafara bincikene na gano dasunan shi da wasuma da bamu zata ba a cikin wanan harkan.
Allah dai ya shige muna gaba nace amin muka dayi shiru kafin ta dago tana fadin dazun yayan ku yazo ya kawo muna goro da alawan bukin Baby da za ayi.
Na dago ina fadin yaushe yazo tace dazun nan bai dade da tafiya ba kuka dawo ya karbi takardan nan dayace zai duba ranan dake waje na.
Da sauri na dago kai ina fadin umma ya tafi dashine tace a,a yadai duba ya ban ajiyan zuciya na sauke tare da lumshe idanuwana .
Kafin in dago ina fadin umma ban takardan in duba in gani yau din nan ba bata lokaci ta mike ta dauko min ta kawo min.
Mikewa nayi dashi zuwa dakina na kwanta na fara karantawa a tsanake ina bin rubutun mahaifin namu da kallo da yadda yake tsara rubutun shi.
Da gani basai an fadama mai ilimi bane shi don irin turacin dake cikin takardan lokacin idona lumshe saiga hawaye sun zobo min a hankali nagoge.
Bayanin irin rayuwan da yake ganine a cikin yan uwanshi sai bayani kan rayuwan shi har neman gwago hari da hanashin da akayi ita kafin ya dawo ya samu tayi aure.
Sai kuma irin ci gaban daya samu da aikin daya fara da CBN tare da business din da yakeyi kafin in budo wani shafi daya rubutawa rayuwa mai kunci da takaici .
A wanan shafin kafin na karanta nayi kuka nayi kuka mai tsuma zuciya sosai ni kadai a daki don abinda na karanta a cikin takardan sharfi ne kan irin barazana da matsi daya fara gani daga yan uwan haihuwan shi.
Ban fito dakin nan ba saidana karanta wanan kudin sai tsakar dare na fito neman abinda zanciwa cikina lokacin.
Babu kowa a falon don dare yayi sosai a lokacin haka yasa nayi amfani da wayan hannuna wurin ganin haske a falon har na samu na debo abincin na dawo na fara ci a cikin duhu.
Naci kamar cibi hudu na dagata don motsin dana faraji a haraban namu duk da suna da nisa sosai da inda gidajen mu suke amma hakan bai hanani jin takon suba kuma na gane an shigo wurin namu lokacin.
A hankali na taka zuwa inda window falon mu yake numfashina naja sai na zabura kafin a mayar dani na furta