Showing 60001 words to 63000 words out of 382072 words
wai see dis small girl no someti like magic kafin tace wani abu nace make give u dis for free ur hair go grow dan dis u will look anty yayalash if ur hair start growing.
Ta farkom tace No give me d one my oga die for me, on bed, if we are making sex ido na dan rufe kafin in tuna da wanda ya ban yace na wanan harkan ne.
Nace if u user am today, tomorrow u will, come back, to look for me, for anoda one, tace oya make u give me dat one, a daidai lokacin kuma motocin dake gaban su suka fara muna horn su basu hanya don haka muka dan gusa kadan suka sake kirana a takaice dubu goma na samu a hannun wa yan nan matan don wanan abin.
Wasa wasa ina tallatawa wasu su zageni su koreni wasu kuma su kirani su saya sai gashi zuwa yamma na hada kudi mai yawa ga wanan tallan maganin.
Jin dadin hakan yasa na ware dubu uku daga ciki don irin riban dana samu ta wanan sana,an naba wanan tsohon daya ban maganin na tallata .
Shi kuma jin dadin hakan yasa ya zaunar dani yana min bayanin yadda sa,anan nasu yake da abubuwan da yake amfani na kwarai da wanda baida karfi..
Anan na shiririce wurin sa ina daukam ilimi ice da ganye wurin tsohon bahaushe din .
A karshe nace ya kara ban sari don gobe ba zan shigo wanan unguwan ba wani wuri zan nufa shima kuma na bashi shawaran ya gwada hakan yace zai gwada insha Allah don nan kawai ya sani yasa yake zama a wurin har nomban wayan shi na karba don kira idan wani abu ya kakare min a rayuwa.
Ga wanda ya ban yace nayi amfani dasu don tsari don sana,an sai kaci ka koshi ake sanin ka ni duk ban damu da hakan ba .
Ni kawai naga wurin samun kudi na karba nayi godiya tare da sallama na kama hanyar komawa unguwan mu da yamma lis sai dare na isa gida da dan kumshin kayana a cikin buhun siminti.
Duk da warim ganyen da sake saki da umma keji bata tsaya tambayana ko me na dauko ba a lokacin har saida na gama abinci da naman kai dana kwaso muna a gidan.
Wanka na fara yi kafin in fito in zauna muci abincin sai bayan mun gama umma take tambayana abinda na dauko a cikin buhu.
Hannu na tura a cikin kwagiri da ban yarda in ajeshi ko a dakin mune don masu shigowa dakin na fito da damin kudin da zaikai dubu ashirin da dan kai .
Na fara bawa umma labarin duk abinda ya faru a ranan jikin umma yayi sanyi sosai take fadin bana tsoro nace da zuciya daya na karbi wanan sana,an nan dai da daren na fara yan hayakin da tsohon nan ya ban nasha nasha.
Barci nayi ranan sosai har da makara saida umma ta tayar dani don makara agurguje nayi komai diban ruwa ne naso makara don layin dana samu a wurin.
Nagama na shirya na fita haka nake samun alheri a wanan harka sosai don sukan sun yi amanna da maganin gargajiya so sai a garin.
Har ya kai na hada da irin nasu dana sara a wurin wata mata da na yan ghana ina sayarwa ina kuma samun alheri ga hakan tsohuwar bayeraban cema taso kawo min matsala sai da zan tafi kome ta gani kuma ta ban sari na hada ina yawatawa ana saye kuma sosai.
Duk ban sani ba tun ranan Chiku yana biye dani duk inda na saka kafa yana ba ogan shi bayani a kaina.
Saidai ogan baya gari yasa baiyi wani kwakwaran motsin da zan iya gane hakan ba ina harkoki na don har gidan mu a yanzu ya sani yasan lokacin fitina da dawowa na gida.
Haka rayuwa taci gaba da tafiya har na tsawon makoni ina hatkokina na sayar da magani da yanzu yafi min komai kawo kudi don har an fara sanina ga wanan harkan .
Saidai inda nake samun matsala shine wurin sayar da maganin maza saboda wasu yan iskan zasu iya ma maganan banza amma haka nake matse fuska ina saida masu shi.
Duk abindake wakana tana ji daga part din ta don Alh Nuhu har ciki ya shigo ya karewa hjy Addah fada dk bai samu miji su da yayi tafiya a gida ba lokacin.
Wani irn shu,umin dariya ta sake dataji fitan shi yanawa kanwar tashi warning kan lalai dan nasu ya dawo gun matar shi watau yar su zuwa gobe in ba haka ba su hadu da fushin shi dukkan su.
Son tun lokacin da yar tasa ta bugo mai waya tana kuka a cikin dare tana fadin Abba Abubakar ya cuceni yaci amanata ashe dama da gaske ba son auren mu yake dani ba gashi yana shirin mayar dani karamar bazawara a yanzu.
Ke ke Nazifa ki kwantar da hankalin ki kimun magana yadda zan fahince ki Alh Nuhu ya fada cikin dakatar da yar tasa lokaci guda don duk son da yake masu bai hana inta baci ya tsawatawa diyan nasa kan abinda sukeyi.
Ki kwantar da hankalin ki ki fada min abindake faruwa ya fada a dan hasale don kukan nata yana taba mashi zuciyar shi.
Don akwaishi da son diyan shi har bai iya boye haka a gaban kowa waye don son kai da yake dashi balle ita Nazifa da yar yar gaban goshin sace sunga wurin ci ne ga Abubakar din suka dauki yar suka bashi.
Lokacin da wanan zancen nason hadi da diyan shi yazo masa don shi bai amince da irin wanan hadin auren da iyayye da kakanni suka bar masuyi ba a yanzu.
Don shi ya fara aurawa diyan shi bare na waje wanda basu da alaka na jini dasu don bai yarda da hadin nan ba a karshe yarinya taje tana wahala.
Kuka take sosai rake labartawa mahaifin nata abinda ke faruwa tun bayan tafiyan Abubakar din wai ko wayan ta idan ta kirashi yanzu baya dauka.
Ga dan iskan yaro Alh Nuhu ya fada yana fadin shi din me shi din banza ni ina da wani manufa akan shi tasa na yarda na bashi auren ki don kar ya dauka ko wani abu yake dashi da har zai fara wullakanta min ke a yanzu.
Wani iri Nazifa taji da zagin da mahaifin nata yayiwa Abubakar din a yanzu don da Alh Nuhu yasan yadda a yanzu take son guy din da bai furta haka a gaban ta ba taji.
Don tun asali tana son Abubakar din har kasan ranta ahiyasa ma tayi amanna da aure ba tare datayi gardama ga iyayyen nata ba.
Don a yanzu data dandana ko waye Abubakar din jinshi take shine komai nata shine ma kamar rayuwan ta gaba daya a yadda take jin shi a cikin ranta a yanzu.
Amma jin kalamin daddy su sai take ta dan sauko ba kunya take fadin daddy kayi mai magana kawai ya tafi dani ko ya dawo.
Allah daddy gidan nan yai min girma da bashi a cikin sa kuma kasan ni ban saba da zama haka ni kadai ba.
Abban nasu ya fahinci halin da yar nasu ke ciki a yanzu yasa ya dan sauko ga yadda yake jin zafin wullakanta masa ya da Abubakar din ke shirin yi a yanzu shine yaje gidan su hjy Addah tun da faran safiya ya buga gida suka tashi ya shiga yayi mata masifa ya fito sai gidan yar nasa kuma can yaje ya karbi wayan ta ya kira mijin nata ya zuba mai tunda safe.
Dole hjy Addah ta kira dan nata cikin bacin rai tayi masa fada sosai tare da umuratan shi akan kome yake ya dawo gida zuwa gobe.
Wanan dalilin yasa ya taso don ya fahinci ran mahaifiyar nasu a bace yake kuma koda bata fada mai ba ya gane Alh Nuhu yaje ke nan yayi mata barazana irin wanda yayi mashi shima da safe.
Don haka ya shirya ya dawo kaduna din don mahaifiyar tasu ba don wani ba can yace a zuciyar shi.
Yayin da hjy karima kuma ta shige sakewa hjy din arashi a yinin ranan kan auren dan nata tana fasin mutum ya daukowa kansa alalkakai don son kai ko tace gamu gani rashe ya na shirin juyewa da mijiya idan mutum yace son kai ya iya shi.
Wanan dalilin tafiyan nasa yasa ua dakatar da duk wani shiri da yake dashi duk da kiran da chiku yayi mai ya sheda mai ya gano wasu abubuwa a tare dani a yanzu.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ANA DARA GA , , , , , , , , , ,
1️⃣9️⃣
BY ZAINAB IDRIS MAKAWA
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AL MU,MIN, , , , , ,
PAID ONLINE NOVEL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA KADA KI RAINA GIRMAN ZUNUBI, , , , , , , ,
Adduan ku nake nema ga bakunan ku masu albarka yan uwa Allah ya yaye muna matsalolin mu ga baki daya dani daku duka amin.
Duk da ba wani sabo mai tsawo a tsakanin su har yanzu a matsayin su na ma,aurata a yanzu hakan bai hana ita ta kawar da komai ba a fili don irin tsananin son da take mashi har cikin zuciyarta ta nuna bata damu da yadda yake daure mata ba.
Yanzun ma dakin ta shigo a cikin kwaliyan ta tun bayan fitan ta daga dakin misalin karfe taran safe ta shiga nata dakin waya tayi da yar uwarta kuma aminiyar ta na gidan su tana bata labarin irin gwarzon min mijin da Allah ya hore mata daga sama irin wanda suke mafalkin samu ita da aminiyar nata a kullun.
Yau ma dai Nazifa bata barshi ba don itace mai neman shi bashi ke nemanta ba duk wanan a cikin wayen wata yake kuma take nuna hakan cikin rashin damuwa don tasan wata rana daina hakan zaiyi idan sun saba.
Aure irin na fulani asali sukeyi a family su wanda kwatsam zakaji an daura auren wance da wani ba tare da sun san juna ko sabiba a tsakanin su kuma a zauna lafiya baka taba jin bakin su ga hakan.
Ta shigo dakin a cikin takon izza da isa da gadara irin na yan gidan su da suke jin Naira na motsi a jikin su sun kuma tashi da wanan akidan kaf din su maza da matan su haka suke da nuna isar su acikin jinin su hakan yake masu.
Da dan fara,anta a fuskan ta taja tayi tsaye tana bin shi da kallo tare da tsuke fuskanta lokaci guda tana kallon shi a gadarance tace dashi.
Wanan jakar da kake hadawa fa na menene shi ta fada daga inda take tsaye fuska daure hakan yasa ya dago jin yadda tayi mai magana a cikin gadara yana kallon ta kai tsaye shima ya bata amsa da fadin tafiya zanyi yanzu.
Babu wani shakunta ko firgici a fuskan shi ya bata amsa kai tsaye kana ya juya yaci gaba da abinda yakeyi din.
Tashin hankali tace ina kuma zai tafi bayan Abban ta yace zai zauna da ita har na tsawon sati uku a gida yanzu ko sati daya bai rufe ba da dawowa har ya fara shirin wani tafiya can.
Zip din dan jakar tasa yaja ya mike gabanta yana kallon firgitatun idanun ta da suka juye tankar tana cikin maye a lokacin.
Cikin daurewa yace lafiya dai naga duk kin canza lokaci daya ko wani abune ya faru kuma ?
So nake na gaskanta wai da gaske tafiya zakayi kuma a yau din nan bayan Abba ya fada ma sai kayi sati uku tare damu a nan ko zakayi wani tafiya a yanzu.
Yayi murmushi tare da girgiza kanshi kadan da daga kafadan shi yace shi Abban naki ya fada maki hakan game dani ?
Wata karfafan ajiyan zuciya ta sauke tare da fadin nasan kunyi hakan da Abba don Abba ba zai mun karya ba ka sani idan kuma kace zaka tafi yanzu zan daga waya na kirashi.
Ya saki murmushi yana duban ta kafin yace a wanan karon kan ya fada maki ba daidai ba don ni bamuyi hakan dashi ba.
Na shiga uku kana nufin ke nan Abba karya yayi min ko me ya Ababakar don haka maganan ka ke nufi a yanzu.
Anyway duk yadda kikace haka din ne nidai nasan ba mace nake ba balle har a kafa min doka inbishi dole ina fatan kin gane.
Ya sure jakar shi tare da wayoyin shi ya rataya yana fadin sai na dawo da sauri tayi kanshi a rude tana fadin.
Wait wallahi ba zaka tafi ka barni ba ni ban gane wanan irin rayuwan ba kullun ace mutum na hanyar tafiya ni kwata kwata sam ban ganewa hakan ba.
Hannu yasa ya jayeta a hanyar yayi ficewan shi rai bace bai ko kara waigo ta ba ya fice daga gidan yana jin wani iri a zuciyan shi a lokacin har zuwa lokacin da faruq yakai shi airport ya shiga jirgi suka daga.
Duk da yasan ranan babu jirgin lagos haka ya daure zuwa Abuja daga can ya fada na lagos din din kiran da chuku yayi mai na gagawa akan mu.
Yanzu kan sai ince faduwan gaba ya zama min jiki har na dan saba da hakan a rayuwa ganin ba abinda ya sameni tun ranan.
Haka na fita daga gida sai ras ras nake ji lokaci lokaci ina dauke da dan buhun sassake na ganyanyaki sai garin magani a kule.
Apapa na nufa kai tsaye inda nake zaton cabawa ga matan wurin don a gaskiya ina ciniki sosai a wanan erea din idan nakai kayana can.
Wata hamshakiyar mace ce ta fito daga motan ta tana kullewa zata shiga wani botiq nake mata talla ina fadin, madam come buy local medecine for pink,
Ta dan kalloni a yatsune taci gaba da tafiya nace madam try,am nd see ego work for u well,well sai taja ta tsaya wuri daya na sake fadin may try my medecine and see ma god go give u fine fine pikin i swear.
Da mamaki take kallona na sai ta karaso har inda nake din tace dani how d u no, dat i no born ? nd i de looking for dis medecinen ?
Emm, i just look at u and saw u problems in ur face na fada yadda masu magani ke fadi idan zasu sharota ga mutum.
Tace Surprise u small pikin u know all dis tins in ur life ? d u have d that my ogo no look anoda worman again after me.
Na shiga kiciniyar bude leda ina fadin if u use dis one e no go see any woman again i swear ina daga hannu.
Mukai ido biyu da chukuma dana fara zargi a yanzu don sau uku ke nan ina yawan ganin shi a inda nake yawon tallana.
Dan rudewa nayi na shiga yiwa matar bayani a gurguje ta karbi na haihuwa dana kama miji a cewan ta .
Ta miko min kudi mai yawa na karba ina godiya tare da fatan maganin ayi nasara abinda ake nema tana fadin Amen ta hanyar daga hannuwan ta.
Ina sauri nake tattara kayana in bar wurin naji muryan a baya na ana fadin i wan buy local medecine for my pikin.
Ba tare dana juyo ba nake fadin i no go sella,am for men ina sauri naga an tare min hanya bayan wanda ke bayana din.
Waitin u wan do for me now, comot for d road , or i will shout oley for u naw, na fada a dan hasale .
Katin shedan su ya ciro ya nuna min ban fahinci na meye ba sai kayan kakin dana gani na gane me hakan ke nufi.
Waitin i do for u, see me see wahala woo, me i no do antytin wain solder man wan cach me naw, .
Motan dake gefen shi ya nuna min da hannu na dan saci kallon bindingan dake gefen shi da ido ba musu na nufi wirin motan ina waige ko zan samu mai cetona.
Allah da ilon shi kuwa a take yan wurin suka taso suna fadin ogo waiti dis gurl do for u she no fait with any body here.
Why you go arest her naw, waitin she do for u ? suna kallona suke tambaya daga inda nake tsaye da naji sun fara magana naja na tsaya inacewa , me i no do anytin for dem broda.
I don't no dem, nd even who dey are ma self, still card din shi ya ciro ya nuna masu sai suka fara darewa daya bayan daya suna sulalewa daga wurin don ba mai son wahala ta ritsa dashi a cikin su.
Tare da buhuna suka turani motan suka bar wurin kamar walkiya har mukai nisan tafiya ban kula