Showing 147001 words to 150000 words out of 382072 words
abin kyama ya faru maki da yarki ba.
Ki yarda dani don Allah ina rokon ki ki bar yarinyar nan rayi amfani da daman ta data samu a wanan lokacin wanda zai kawo mata cigaban rayuwa idan Allah ya yarda.
Shiru umma tayi na dan lokaci tana nazarin kalaman shi kafin kome ta tuna tace na yarda dakai da imanin ka Abdulhamid don na tabbatar ba zaka taba barin yarinya na ta cutu ba ga hakan.
ZAINAB IDRIS MAKAWA, , ,
ANA DARA GA, , , , , , , , ,
4️⃣4️⃣ BY, , , , , , , , , , ,
ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , , ,
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AL KHABIR, , , , , , ,
ONLINE PAID NOVEL YAR UWA DON ALLAH KADA KI KARANTA MIN IDAN BAKI BIYA BA, , , , ,
Washegari a Ekoyi muka wuni ga wani girma da haba haba da mukr samu wurin mutane don kawai muna tare dasu da muke samu .
Ban san kowa ba a wurin sai Adnan da muka fito company daya dashi koshi dan zaman aiki wuri dayane ya hada mu dashi ba wani sani nayi mai ba.
Ban yarda idan lokaci yayi na ibada duk aikin da mukeyi zan aje naje nayi sallah sai suma masu sallah a cikinsu su mike zuwa yin sallah din.
Aikin aikine kan tukuru don babu magana ko wani abu bincikene kan kayan da aka shigar da kudin su bisa riban da aka saka a sama.
Muna gamawa da Ekoyi din wurine na sayar da babura masu kafa biyu sabbi fill din su a leda suna cikin kwalayen su na part.
Magana suke a tsakanin su ganin an gama yasa na mike tsanman na suri jakkata wanan Felix din dake dan min magana yake tambayana ina zanje nace gida.
Ba zaki jiramu ba nace ina saurine kada mahaifiyana taga na dade ban dawo gida ba wow babban yarinya dake maman ki zata tsaya maki fadan baki dawo gida da sauri ba ?
Felix ya ambata daga inda yake ba tare daya juyo ba yake fadin ka dauketa ka kaita gida ka fada mata gobe zamu hadu a gidan mota na ebony dake idi,eroko kusa da bakin titin dake kallin custom office .
Tsayawa nayi ina kallon su gaba daya din ko lokacin ina yawin tallana ai sau daya naje wanan unguwar ban kara marmarin komawa ba tun lokacin.
Gani kamar ban gane ba Felix yace karfe takwas daidai in fito in jirasu a main road na Apapa zasu daukeni a wurin.
Nace OK Sir na juya na fita na barsu ciki titi na nufa duk a gajiye nake ina neman abin hawan da zai kaini gida don bada motana nazo ba dama taxi na dauko drop.
Na dan jima wurin a tsaye kafun su fito daga cikin comoany sunyi mamakin ganina a wurin Felix din ne dai ko wanan karon ya tuko har inda nake yana tambaya bada mota nazo bane ,?
Nace drop na dauko zuwa nan din shiga muje yace dani yana bude min dayan gefen nasa na shi muka kama hanya.
Ba abinda ke tashi cikin motan sai kidan turawa shi kuma yana bin sautim da wakan har muka dauki hanyar da zai hau damu titi da kyau.
Motan yayi shiru sai shi dake bin wankan jefi jefi idan an kawo inda yake jin dadi kunsan kafirai da son wanka.
Na tare da ya kalloni ba naji yace miss sayiba don't you know dat you're now different than before ?
Why are u not used your car ?
Bai kallo inda nake ba saidai jin ya kira sunana nasan dani yake magana lokacin yasa na dan juyo ina kallon shi.
Our oga don base with you today.
Don't ever repeat dis mistake again when we are going on mision, he's not happy with d way he is seeing your behaiviours.
Saida naji yayi shirune nace dashi iam sorry i will not repeat it again but what have i did wrong in dis ?
Murmushi yayi kafin yace baki san waye guy din nan bako shi mutum ne mai kirki kwarai baida kyatan na kasa dashi ko kadan.
Shi mutum ne mai sakakwn hannu ga duk wanda yake tare dashi sai dai kiyi hankali don akwaishi da kaifin basira sosai da ilimi dan adam kallo daya zai maka ya fahinci rayuwan ka da abinda kake ciki.
Don haka ki kara kulawa ki kuma ci gaba da kawar da kanki ga komai da yake kiyi aikin daya kawo ki nan tare damu baya son yaga baka da tsabta don wanan yana hadashi da mutum gashi da son kamshi aikon gashi dai shi yadda yake ko na gyada kai yace ki kula da abubuwan dana fada maki din.
Jin yayi shiru nace nagode na kawar da kaina gefe ina cigaba da tunanen dan zancen daya fada min din.
Ba komai nake tunane ba sai shi din waye wai da yake da wanan dukiyan haka mai yawa a cikin kasan nan.
Gaskiya nasan kabila suna da arziki fiye da yadda muke tunane a Nigeria din nan sai dai ai yayi karami da mallakan wanan dukiyan haka.
Muryan Felix din ne yake fadin kin san shi haka ya taso a cikin daula uwarshi hausace yar erewa sai dai yanzu ba zakice ita din hausa bace don yanayin larabawa da dabiun nan daya shige mata gaba.
Ance mahaifin shi dan nan lagos shi saidai shima mahaifin nasa ya gaji dukiyan shine a wurin mahaifin shi kamar shi.
Sunyi aure ne a can lardin labawa inda suka hadu da ita taje karatu shi kuma harkokin business din shi sun kaishi can .
Kafin ya aureta yana da wasu mata yan yaren nan lagos din saidai bai taba haihuwa ba sai haduwan shi da itane Allah ya basu haihuwa.
Haihuwan su biyu kafin shi basu tsayawa kinsan mutanen mu da canfi don har sun fara camfa mahaifin cewa da diyan shi dukiyan shi ke habbaka.
Sai gashi sun haifi Sha,aban ya tsaya har ya girma yakai haka yana da kanwa mace daya sai yan uwa dake karkashin shi a yanzu.
Duk da har yanzu yan uwan mahaifin shi ba wani shiri ke tsakanin su dashi dalili uwarshi ta kasance ba yar yaren mahaifin shi bane sai kuma kiyayya irin wanda ake samu gun yan uwa wani lokaci duk da kyautatawan da yake masu din.
Daga nan yayi shiru ya barni da tambayan kaina ashe dama haka yan uwan uba sukan kasance a ko wani bangare ke nan ba mune kadai keda wanan matsalan ba ashe ?
Saidai kinga duk wanan harkan da yakeyi a nan din yafi samu a can kasashen larabawan don sun fimu dukiya mai yawa fiye da nan din.
Yanzu ma wanan aikin da mukeyi an samu matsalane da wasu manajojin dake son durkusar dashi a wasu bangaren yasa wanan binciken ya taso a haka yanzu da can bai haka a wuraren sana,an shi ai.
Hango layin mu da nayi nake cewa dashi your right hand idan kaje wancan jection din yace ashe baki da nisa da ma,aikata dama na gyada mai kai don kaina daya daure a lokacin Allah Allah nakeyi na sauka ko zan samu dan sa,ida a zuciyana.
Yana kawowa kofa mu nace yayi ina kokarin daukan jakata tun kan ya kashe motan nakara mai godiya na bude na fito yaja motan shi ya tafi.
Watan su biyu a kaduna koda wasa bata taba lekowa kancewa zata gaida mahaifan mijinta ba ko zata kawo yara su gansu.
Tun abin yana damun hjy Addah har ya koma bata mamaki akarshe kuma ta watsar da zancen kada ya zama mata ciwon zuciya.
Har Allah yayi dawowan Ya Abubakar kasan bai fadawa kowa dawowan shi ba saida yayi kwana uku a cikin gidan shi yana hutawa kafin ya tako zuwa gidan su da safiyan jumma,a sai ganin shi kawai yan gidan sukayi suna karyawan su da safe ya fado masu.
Da murna suka tare shi don an dade ba,a hadu ba har yasamu wuri ya zauna aka shiga jero mai abincin lokacin hjy karima ta shigo tana mai sannu da zuwa da yaranta baki daya gaba daya yaga sun girma mai lokaci guda sunyi tsawo ga ganin shi.
Har sun gaida shi sun mashi sannu da zuwa zasu wuce Amirah tace ina anty Sahiba ?
Gaba daya falon sukai tsit sabanin shi da gaban shi yayi mai wani irin faduwa lokaci guda don gaba daya ya manta da zancen wasu iyalin su sahiba a lokacin.
Sai wanan zancen da yarinyar nan tayi yasa abin ya dawo mashi a rai baki daya lokaci guda sukuma sauran na fadin.
La,ilah ji yarinyar nan ashe bata manta ba don tasan cewa shi ya tafi dasu lokacin yasa ta tambaye shi su a yanzu.
Ta dauka suna wuri dayane yasa ta tambaya yanzu din hjy ta fada ya dago yana fadin basu zo garin nan bane tun lokacin mommy.
Suzo wurin wa mu ko waya bamu tabayi dasu ba tun wanan lokacin don gabaki daya ma mun manta dasu wallahi.
Take yanayin shi ya sauya yana fadin kun manta dasu hjy kun manta dasu fa mommy ya fada cikin manaki ?
Au su basu nememu ba sai mune zamu zauna neman sy a kullun ?
Daga inda hjy karima take tsaye tace dashi wanan ce ma mai karanbanin tunawa dasu ita da fatima can ba,a rasa ba.
Innalillahi ya fada yana shafo kanshi daga sama zuwa sama a cikin damuwa irin na tashin hankali ya mike tsaye daga inda yake zaune din.
Ina kuma zaka ya koma ya zauna hjy Adda tabi dan nata da wani irin kallo na ban mamaki ganin yadda duk ya rikice lokaci guda kan zancen su.
Ko ni wani lokaci dan sabon da mukayi dasu zaman mu dasu a nan gidan nakan ji kewan su sosai sai dai baka da wani alaka da mutum kaga duk yadda ka damu dashi dole ka kyale.
Hjy karima ce ke fadin wanan zancen daga inda take tsaye kafin ta juya tana fadin ai Amira kan naga ranan da zancen sahiba zai fita zuciyar ta gidan nan.
Fitan hjy karima da yaran ta ya dago yana fadin gaskiya mommy ba a kyau ta ba da baku nemi mutanan ba sai su dauka wani abu hakan ai.
Kai yaya kaci abinci ka karya ka tsaya kana zancen wata sahiba can da bata ko damu da kowa ba dama fa zaman dole sukeyi a nan dama.
Ke kikasan abin fadi ya dago kai yana kallon nabila din dakw magana kafin yace zancen yan uwan ki akeyi bana wani ba ke idan haka ya sameki suna a matsayin ki zasu kyaleki ne ko me ?
Ka tafi gidan kane ko nan ka sauka mommy ta tambaya tana kawar da zancen da yaran keyi a lokacin don kada maganan yai nisa.
Don Allah ya gani ita dai bara son zancen ganin mutanen nan ta bangareta gara aje can ayi duk wace za ayi idan wani ya gansu ba ita ba.
Ta sake tambayan shi da fadin kakai kayan ka gidanka ne yace tun shekaran jiya ai nake garin nan ya fada har lokacin fuskan shi a daure.
Ba abinda yake tunane a zuciyar shi sai yaya muke rayuwa a can tunda ya barmu ne ga bai samu nemawa ko Amar gurbin karatu ba ya tafi.
Yasan ko ba zamuyi azancin cewa muci gaba da kararu ba tunda shi bai dawo gare mu ba balle ya taimaka muna da hakan.
Abinci fa ta yaya muke samu yasan wanan ba wani babban matsala bane don zanyi talla in tallafawa rayuwan mu yasan da wanan din.
To amma abinda ya daure mashi kai shine, idan shi baya kasan daddy fa me zaisa daddy yafita zancen bayin Allah nan haka ?
Shifa abubuwan nan suna daure mashi kai kan game da daddy akan wanan zance wani lokaci anya kuwa koshi ma din ya gano hakan ne don yana kwararen dan sanda irin mahaifin shi.
Muryan hjy ne ya katse shi tana fadin ke nan Nazifa da yaran suna gidan ka yanzu haka ke nan uwar nasu ta tambayeshi tana mai tsura masa ido don son jin amsan da zai bata.
Ban fada mata na dawo kasan nan ba kuma bazan fada ba sai idan taji ga wani kamar yadda tayi maku itama yana fadin haka ya mike tsaye.
Kallon kayan abincin da aka aje a gaban shi tayi kafin tace ka zauna ka karya kafin ka fita shima ido ya saukar ya kalli abincin kafin ya ja dan tsuki yana fadin ba zan iyaci ba mommy.
Akan me ko ka karya a gidan kane ya kada mata kai alaman a,a yana fadin ban ci komai ba tunda na dawo kasan nan.
A razane ta mike tsaye tana fadin bakaci komai ba mekakeyi ka tsaya haka da cikin ka bakaci abincin har tsawon kwanakin nan modibbo ?
Kawai bana jin cine mommy ai wanan ba komai bane idan akwai diyan icce sai mutum yaci na dan lokaci.
Zancen matar ka kana ganin hakan zaifi ba zai jawo matsala gareta da mahaifinta ba kasan halin yaya Nuhu da daukan zafi da gangan.
Mommy ku wanan ya dama ni bashine a gabana ba yanzu zancen Nazifa kuma banyi fada da ita ko wani sa,insa ba amma ta zabi taci wa iyayyena mutunci da yan uwana.
Don haka mommy na rokeki da kada ki fada masu zancen dawowana don girman Allah ya hada hannayen shi a wuri daya yana rokon ta arzikin hakan.
Yana fadin haka ya juya zai fita Nabila tace wanan shine daidai ai mommy wallahi ayi maganin ta ta gane kuren ta zaifi.
Baidai juyo ba duk dayaji abinda kanwar tashi ta fada haka yasa kai ya fice yana jin zuciyar shi tana masa kuna.
Gidan sa ya koma ya kulle kanshi a cikin dakin yana faman tunane shi yanzu ma da wani ido zai kallemu yacewa wayan nan mutanen me a yanzu shekara nawa yanzu rabon su da su waige mu an dauki lokaci mai tsawo haka da wani ido zai kalli umma da yaranta yanzu.
Yayi shiru taci gaba da tunane can yace bayan wanan shi daddy dake kasan meya hanasa neman su ne ?
Anya kuwa ba wani abu a boye da daddy don shima ya boye kan wa yan nan ahalin dake cikin ukuba da gararaba a cikin duniya.
Duk dai yasan a yanzu basu saura gararanban gidan haya ba tunda ya sama masu wurin zama ya sani kafin ya wuce .
Kuma yana da yakinin cewa ba zasu daga, daga inda ya ajesu din ba in bada wani dalili mai karfi ba da zaisa su bar wurin.
Bai sake fitaba a ranan sai washe gari da yamma ya shirya ya fita zuwa wani super market don ya dan sayi abubuwan bukata na gida.
Tunda ya tunkaro wajen da motar shi samarin dake tsaye suna hira suke satin motar tasa har yazo kusa dasu ya wuce.
Daga cikin su dayan ne ya sake murza idanun shi ya duba da kyau idan ba idon shi ke masa gizau ba tabbas modibbone a motan yake tukawa .
Da mamaki ya bishi da kallo tare da fadin yaushe guy din nan ya dawo garin nan ?
Abokan shine suke tambayan shi ko yasan shine yake fadin mijin Naziface fa datake aure suke zaune a kasan waje dashi.
Kai mutumina kace zaka dauko muna dani ke nan ashe wata rana mu faso gari a cikin sa yace ku bari kawai aisai na dana motar nan kota halin kaka duk shi din jan wayane shegen kanshine sosai shima.
Har ya sawo abinda zai sayo din ya dawo ya wuce su a wurin bai shedama akwai mutane a aurin ba lokacin.
Sai bayan sati dayane ya shigo cikin gida ya samu yar nazifa na kuka yake lalashin ta kafin can yace dasu ke nazifa ashe mijin ki ya sawo wata kafiran motane da zai dawo ?
Da mamaki kowa ke kallon shi har mahaifiyar su yace Allah wata rana zai ban motan nan in dana ta don nima na faso gari zama cikin salebiritin garin nan.
Mahaifiyar nasu tace kai ina kaga mijin ta a garin nan da naka shirmen kuma yace kai ji mama fa ?
Shi modibbo din ne kuma ban sani ba ko me sau nawa ina haduwa dashi saidai kin san sbi da ahegen daukan kai yasa nima nake kyaleshi .
Sai dai mota kan saina dana motan nan nasa komai jin kan shi kuwa don nayiniyar hakan a zuciyana.
Na shiga ukku modibbo fa dan wajen Addah kacw ka gani yace tun yaushe nake ganin shi a garin nan.