Showing 204001 words to 207000 words out of 382072 words

Chapter 69 - ANA DARA COMPLT BY MAKAWA

MAKAWA   

29 Jun 2024

28381

watau shu,umace ta gaske fiye da yadda kake zaton ta.
Don ka duba fa wanan file din Bala ya fada muna cewa shida hannun shi ya cire shi kuma ya boye shi amma yarinyar nan sai gata da files din nan a hannun har kuma ta zakaloshi cikin yan uwa tasan dashi.
Koda muka shiga muyi yadda kace sai cewa tayi damu me muke nema wanan nan din ta na hannun ta saita miko muna tana fadin gashi ai ta gama dashi ko mu dauka.
Ke nan ta kwashe komai na cikin sa ke nan ta dawo muna dashi din muyi abanda zamuyi dashi wallahi Alh yarinyar fa kada kaso ka ganta duk batafi shekarun yata ta biyu ba da haihuwa.
Dan shiru yayi kamar yana nazari can ya dago ya gyara babban rigan shi dake saye a jikin shi daga shi sai ita dama kana ganin jikin shi daya fito daga cikin .
Yace yanzun dai manaja a takaice ba zaka iya ba ke nan da wanan yarinyar manaja ya gyara yana fadin gaskiya kusan hakane Alh dole sai kun saka hannu a zancen nan.
Zamu saka ita sin me ko oduduwa kakan yarbawa ya shigo gonan mu a yanzu ai zamu kawar dashi ne kamar kauda kara ba wani aiki bane kubani yau da gobe ki gani sai ta nemi agaji ta bar garin nan a gagauce nina fada maku.
Godiya suka shiga mashi cikin nuna jin dadin su ga hakan nan kuma sai hira ya barke a tsakanin su oga Bala na nuna masu yadda nake turanci wai nasha mai nayi fari kamar baturiya nazo zan masu barazana da fari a nan shiko yace su za a nuna ma farin shago suda sukaga yan matan kano bila,adadin mai zai basu tsoro kafiram banza kawai.
Alh na jinsu kafin ya dago yace meye sunan yarinyar ne koba ta fada maku sunan ta bane ta fada ya dago yana kallon manaja shi oga bala dake ta faman zuba lokacin.
Gaskiya na manta don sunan dai gashi kamar na yarbawa kamar na hausawa haka ko larabcine oho ?
Sa,ba ko me kusan haka dai ta fada koma waye ai zamu sani ya fada ku bani lokacin dana fada daga gobe zaku ban labari da bakin ku yadda za a kwashe da ita.
Godiya suka karayi kadin su bar falon nasa ba tare da sunyi wani maganan akan dawo da abinda ke hannun su don har lokacin zancen haka baizo a zukatan su ba.
Shi Alh ma shirme da haushin su yake gani yadda suka wani tsorace akan mace macen ma yar cikin su kwaranya da ita.
Tsab na shirya a cikin wando da rigan aikin mu na can mai daukan hankali ga duk wanda yaga kayan namu na fito daga daki zuwa da yar jakar tafiyana ina fadin umma zamu tafi ke nan.
Tace har zaku tafi baki karya ba dauki ga tea nan nasan dama haka zaki ce zaki bar gidan nan bakici komai ba.
Dole na dan kai zaune nayi bissimillah na kafa kai na dan fara kurbawa saboda akwai dan zafi umma ta kura min ido daga inda take zaune .
Nagama nace to umma zamu tafi ina mikewa tsaye tace Allah ya tsare ya kare Allah ya haushe ku a saman su ya sa a dace da abinda akaje nema.
Na amsa da amin kofa na tsaya hakan kusan dabi,atace ban fita gida ba tare da addua ba bani ba kusan dabian yarbawane hakan da yawan su haka suke wanan dabian nagama na shafa nafita umma tana bayana.
A kofan mu ta tsaya tana min sai mun dawo na amsa na tafi bakin motan Adnan nan na shiga muka dauki hanya mu hudu a nasa motar shida felix a gaba zaune nida yemisi abaya.
Felix ne ya fara magana yana bada labarin irin wullakancin da akai masu a can din yana mamaki sosai na yadda suka nuna basu san aikinsu subama sam.
Yaja hausa hausa are terreble people ya fada dan gyaran murya Adnan yayi yana masa signal da ido gani nan fa yace.
Ainikan yarobace don ban san komai ba ga hausa karshema kila bana jin yaren sosai suka kwashe da dariya nidai murmushi nayi masu kawai.
Allah da ikon shi mun isa da wuri kai tsaye muka nufi cikin ma,aikatan kamar dai yadda wacan din ya mutu sai ince wanan din ma kamar ya fishi mutuwa ga ma,aikatan a warwatse wani wurima na hango dabbobi suna kiwo a cikin wurin mota ya tsaya a gaban ginan daidai inda Felix yace ya parker da sauri na dago kai nace ya kara gaba gadan ya tsaya a barin dama.
Sun rigani fitowa dukkan su a cikin motar har na dayan motan sukazo suka tsaya a daidai inda motar mu yake tsaye suma suka fito daga cikin motan.
Hankalin wa yanda ke ma,aikatan ya dawo gare mu ganin mu a cikin bakaken kaya lokacin ganin Felix da yemisi .
Kafin na fito ina bin ko ina da kallo na haraban wajen yadda ma suka bamu lavarin dai naga basu fadi daidai don gaba daya wurin ya lalace sosai.
Bamu shiga ba sai zaga ko ina da mukayi har idona ya kyallo min an cire injin biyu dake sarrafa alkama a wurin.
Mun shiga muna dan gaisawa da wanda muka gani nice baya ina waya da umma da harshen yarbanci muka kai kofan muna tambayan manager wurin.
Wai yau bai fito ba suka bamu amsa naja na tsaya daga baya suma din kamar can da muka barone don gulman sukeyi suna ina kwarin nan suka fito hakane wai ?
MD da da sauran manyan wurin muka sama sun kira chairman din wurin shima wai baya gari wani ya gama waya dasu ya juyo yana muna bayani cewa wai yace ace yayi tafiya sai next week zai dawo.
Har abokan aikina sun fara maganan kan yanzu ya zamuyi ke nan sai sukaji nacewa mutumin excuse me can i have his number please ?
Sai naga sun kalli juna sun juya da hausa suna fadin wa zai yarda a koreshi idan oga ya dawo ya gane nina bayar gaskiya bazan basu ba nikan.
Ba zasu bayar ba fa yemisi ta fada tana fadin ranan wallahi ba karamin wullakanci sukai muna ba a wurin nan saida kyar muka samu suka fada muna koshi wanine ya nuna muna tabaya lokacin zai fita ya haumu da fada sosai a wancan wurin.
Muje kawai nace dasu suka biyoni baya na bi hanyar matakalar benen zan hau da sauri wancan daya buga waya ya biyo mu da waya yana fadin gashi ya kara kiran layin kuma yana mika muna wayan sai Abdul ne yakai hannu ya karbi wayan a wurin shi.
Yz miko min na dauka kuma ban tsaya ba har muka hau saman na kara a kunnena ina ji wai bayanan shi don haka sai kubar, , , ,
No problem koda baka nan ai company na nan zamuyi aikin daya kawomu mu wuce kada ka damu ai na fada ina mikawa wancan mai wayan wayanshi.
Tsarin ginan nabi na gane offince din da nake nema din na nufi can murda kofan nayi yana bude sai nadanyi nocking tare da sa kai cikin officen ga baki daya.
Saura suma suka biyoni a baya waya yakeyi a lokacin jin yadda aka shigo mai yasa ya dago a fusace yaga ko waye sai mukai arba dashi ya mike da sauri.
Sannu da zuwa yayi muna kafin ya tambaya mudin su waye Adnan yayi mai bayanin daga inda muke da abinda mukazo wurin su yi kuma na bincike kan company.
Nan ya fara muna inda inda yana fadin ai tun da suka samu labarin muna kaduna suke kokarin shirya files din saidai basu hada ba har yanzu.
Baida matsala ai tunda mun sameka zaka iya debo muna wanda ke nan sai mu fara dashi na fada bayan na kare bin office din da kallo.
Yace gaskiya ba zai iya bayar da komai ba shugabanin sa basa nan don haka muyi hakkuri har su dawo din.
Kana tsamanin bamu san shirin da kukeyi bane a kai yau din nan da muke son su a hannun mu inyaso saiku cinawa wurin wuta kamar yadda kuka shirya yi din da daren nan ko ?
Na fada na kallon shi tare da dan sake mai murmushi har dimple dina ya dan lutsa a lokacin bashi ba kowa na office din saida ya kalloni na dan duka kadan ina aje computer na dana fitar tare da fadin files guda dubu biyune ko da dari takwas da muke dasu a nan a cikin shekara goma sha hudu dayin wanan masana,antar .
Yanzu kuma kuna kokarin fitar muna da guda dubu da dari takwas sauran fa malam idan kun boyesu koda yake no need ku fitar muna da wanda kuyi niyar fitarwa din ba matsala zamu samu komai a cikin wa yan nan din na hannun mu.
Sorry mah ya fada da dan rawan jiki ba laifina bane yin hakan nima umurni akabamu muyi hakan daga saman mu waya kawo wana idea din na tambaye shi ina kallon shi ido a cikin ido.
( Mai karatu zaki iya cewa wanan shirine don labarin yayi dadi haka Allah sarki ranan da Allah ya hada ki da wani dan baiwa mai abin mamaki zaki tuna da ni Sahiba ashe labarina ba karya a cikin sa.
Ni kaina haka dai Allah ya haliceni nake gani banda matsalan ciwon kai gaskiya bansan ina da wani matsala a jikina ba .
Bana bada magani amma zan iya kallon ki in abin ya biyo a kaina zan fada maki komai game dake kuma hankalina bai bace a tare dani ba.)
In takaice maki dai ranan bamu daga a surin ba saiga manaja mai tafiyan sati daya ya dawo garin ashe baije ko ina ba yana garin dama.
Wani bakine mai dan jiki da tsawo sajen fuskan shi yana gauraye da baki da fari da tsaga uku uku a bakin sa.
Yo don me zasu shigo muna babu sanarwa haka kawai suce sunzo aiki damu ana ce masa yallabai kayi hakkuri a bisu a sannu tunda sun zo ko ba abinda zamuyi yanzu.
Saina ci musu mutumci na nuna masu nan arewane ba ai muna kutse haka shi idan ba yana mutumin kawai ba bazai nemu mu sulhunta a tsakanin mu ba.
Sai kawai ya turo muna comitten bincike haka suzo su wani cika muna wuri da guntun turancin su iya wuya don Allah ku bari in shiga muyita yanzu dasu yana fadin haka ya fado offince din inda muke kai tsaye.
Kowa daga inda yake zaune yana aiki suka dago kai suna kallon shi Bellone cikin wanda muka dauko daga kaduna yake fadin malam lafiya dai.
Bin kowan mu da kallo yayi kafin yace ance kuna nemana kuma kun shigo baku fada muna zuwan ku ba kun fara aiki bada masaniya ta ba?
Who is he na tambaya ba tare dana dago kai daga abinda nakeyi a cikin naurata ba yace iam the chairman of this place.
And then so what na fada idona kan laptop din na dago ina mikowa na kusa dani takarda yana tsaye ya kura min ido a cikin mamaki.
You can go now mr chairman you are not invet here ka barmu muyi aikin daya kawo mu mubaka wurin ka daga inda Adnan yake ya taso zuwa inda nake zaune yana nuna min abu a computer shi nayi masa bayanin komai ke ciki.
Ina kokarin dukar da kaina inci gaba da aikinane Felix ya jefo min tambaya na bashi amsa duk yana tsaye kamar an dasa shi a wurin ya kasa fita.
Ku bashi kujera ya zauna wanan tsayin yayi yawa haka jin haka ya bashi daman fita yana fadin yana zuwa ya fice da sauri.
A kano suna jiran fitowa mu yau su sha kallo kamar yadda Alh ya fada masu cewa zaiyi maganin mu su bari suga abinda zai faru damu a kwana biyu ras.
Suna zaman saka idon ganin fitowan mu shiru har sha dayan rana babu alaman mu sai suka dauka ai abinda akace zai faru damu din ne yafaru din.
Suna mayar da zance ne kiran chairman din can ya shigo masu a wayan yana sanar dasu muna wurin su munyi kaca kaca muna musu binciken kwakwaf.
Yan iska a can suka dura maku yau kuma ashe akwai ta kuwa da wanan shu,uman yarinyar mai kwakwaf da isa.
Sundan jima suka kashe wayan suna murnan can kuma iskan namu ya kadamu ke nan mun gama dasu ke nan ashe dama me zamu iya dasu .
Abinda basu sani ba shine Alh na can ya shiga wani hali don ya kira bokan su ya fada mashi komai yace ya bari zai kirashi idan ya bincika.
Ya binka din ya kumaga abinda bakin sa bai iya fadawa Alh kada su raina mashi wayau ga aikin shi abincin shi ya dakile a wurin su.
Yasa yace dasu gaskiya subi aikin nan a sannu don mutanen nan sun wuce yadda ake tsamani don me basu fada mai da wuri ba su san abinda zasuyi a kai.
Yanzu aikin gagawa ba zaiyi tasiri akan su ba dole sai an dan bada lokaci kafin a samu yadda ake son samu.
Su bashi shanu ayi yanka da bakaken busurai guda uku da kudin da za a sai turaren da za ai aikin dashi yace zai aiko masa zuwa yamma.
Ankan sayo shanu wai a hanya haka kawai shanun ya mutu a cikin mota haka kawai ba a san me ya sameshi ba.
Jin wanan labarin ya sa Alh shiga cikin wani yanayi na tashin hankalin don ba kudin shi bane shi kadai shi yanzu me zai fadawa sauran abokan harkan nasa akan haka.
Bawai shanun yafi karfin shi bane kawai dai bakin haline irin na wasu don yana ganin idan ya sai wani shanun kamar shi kadai ke nan ya biya masu aikin amma yasan abinda zaiyi .
Adaren ne kuma yayi mafalki da wata fitsitsiyar yarinya a gaban shi tana bashi warning kan abinda suke shirin aikatawa din a cikin tsawatawa ya ganta tana mashi kashedi.
Hannu ya daga yakai mata mari takama hannin wai har hammun shi ya kare a cikin ya falka a firgice yana maida numfashi lokacin ne kuma yaji baya iya daga hannun da yaga an rike masa din a cikkn mafalkin .
Duk yadda yaso ya motsa hannun abu ya kiya gareshi tun yanayi shi kadai dole ya bidi taimakon iyalin shi kan hakan.
Abu wasa wasa har gari ya waye aka nemo mai duba kariya yazo har gida ya duba yaja masa hannu ai sai abin ya karu mai fiya da yadda yakeji da farko ma.
Dole aka danganta shi da asibiti can ma sunyi iya duban su basu gane komai ba suka saka mashi ruwa da alluran kashe zafi don ya samu dan sassauci amma ina .
Awanan halinne Oga Bala ya kirashi don ya sheda mai halinda ake ciki babban dan Alh din ya dauki waya yana masa bayani halin da mahaifin nasu yake ciki.
Takawa yayi ya kira chairman da manager ya fada masu abinda ke faruwa da Alh din ranan kallon juna sukayi kafin shi oga balan ya basu shawara cewa su isa asibitin suga halinda yake ciki daga can suyi masa bayanin komai.
Saidai sunje din abinda idon su ya gane masu babu dadi ga Alh dole sukai mashi sannu suka kama bakin su suka tafi.
A hanyane manaja ke fadin anya anya kuwa ba wanan dalilin bane ya jawowa Alh wanan fitinan karo da yarbawa fa ba banza bane.
Kai ina sam Alh fa da kuke gani shima shegen kanshine na gaske indai wurin wanan harkan ne yaci gaba da cika bakin sa kan Alh suna sauraren shi.
Yanzun mommy wanan abinda kukewa gwaggo baku sakata a hanya ba sai biye mata kuna dulmiyewa shine daidai mommu ku baku sakata a hanya maidaidaiciya ba.
Me kuma mukayi don kawai mun je nuna mata farin cikin mu shine laifi kuma yanzu ?
Ok kiyi hakkuri mommy idan ranki ya baci amma ni gaskiya na fada maku ai don kawai yana shi kadai sai a diga yin wanan abin haka fissabilillah ?
Tau ubana nida abu ke samuna su zo min din fa shiba laifi bane yin hakan ko tunda ni akaiwa ko na fada ma kadaina raina min wayau irin haka.
Don ko banza kasan dai hari yar uwatace kuma tare muka tashi da ita kamar kawaye sai yanzu kuma kan danta in kita.
Ya mike yana fadin zan tafi dama kayan yarinyar nan da nayi odane suka iso nazo in fadawa daddy dasu


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login