Showing 375001 words to 378000 words out of 382072 words
ke nan dama.
Lalai wanan yarinyar takai shu,uma itama tunda har ta gagari rayuwanta ta kwana mata da miji har da samun rabo a hakan ?
Muryan daya daga cikjn matan ya katseta dake fadin waiko ita ta haifesu ko kuwa sunyi aducting dinsune da sunan haihuwansu donsu batarwa mutane da hankalin su ?
Da sauri ta juyo tana kallon matar itako matar saicewa tayi yes kina mamakin hakane meye ba za a iya yiba a yanzu aikibar mutum kawai da makircin shi.
Shiru tayi tana nazari kafin ta mika hannu ta sake karban wayan tana nazarin fuskokin yaran kafin ta nisa ta fara fadin wanan zai iya zama gaskiya.
Saidai akwai inda zan gane gaskiyan hakan don duk illahirin zuri,an su suna da dan cindo a karamin yatsan hannunsu idan hakane ko dole ya kasance suma a sameshi a hannunsu.
Kwarai kuwa da kyau mun samu abinda zamu dogara dashi na farko da zamuyi challanges dinsu dashi bayan haka dole mu kara samun wani evedence da zai nunawa duniya yaran ba diyan mukhatar bane .
Ni duk ba wanan ba a gabana duk suka mayar da hankali suna saurarenta lokaci guda din suji meye damuwanta dake ci mata rai.
Ta nisa tana gyara zama tacesai wai ace yauni Falmata mukhutar yakeyiwa wanan irin halayen haka kan wata mace macen ma karamar yarinya.
Au bakisan mazaba ke nan hajaju ai idan kina son kiga true colour dinsu ki bari sai sun kara maki kishiya kiga tabara da tsiyataku a wajensu kala kala dama abinda matakewa gudu da karin auren ke nan ai.
Kina zaune kalau da mijinki daga sama wata tashigo ta bata maku tsarin zaman ku Idan baki kai zuciya nisa ba har a aikata abinda ba, a so a karshe.
Falmata ki natsu ki yarda da kaddara kinga irin abinda yasa tun farko suka boye maki wanan zancen cikin ke nan don irin wanan halinda kike nunawa.
Ke yanzu duk abinda ya faru dake a baya kin manta ke nan a yanzu keda aka samo rayuwan ki da kyat daga ballewan jini da ki kasha fama dashi.
Ace wai mutum dan musulmai, amma baya tawakkaki da duk kalan kaddaran da Allah ya aiko ma bawa dashi.
Mikewa tayi fuuu ta wuce zuwa sama inda dakunan kwanansu yake tabar kawayen nata tare da yan uwanta a falon.
Yadda kowa yaji zancen haihuwana yake shiga mamaki kwarai don sam ba wanda zaice yana da labarin cikin jikina hakanema yan uwana har ummana dukda tasan akwai cikin saidai bata san yaushene watan haihuwan nawa ba.
Lokacin daya kirata yana sheda mata zancen haihuwa da ace wanine ke fada mata wanan maganan ba mukhutar ba da ba wasa a tsakanin su.
Da sai tace maishi wasa yake mata ko yana zolayanta akan hakan wai Sahiba ta sauka lafiya ta samu babies twin's maza haka maganan yazo mata a bazata .
Har yaushe Sahiba din tayi cikin daya isa haihuwa ke nan koda mukazo sallamanta zamu tafi cikin na ajikina har ya tsufa a lokacin.
Gashi ya fada matacewa zuwa tuesday zasu tafi daga ita har Ammar da gwaggo kudidi sai gwaggo Amina wanan tafiyan nasu ya kawo muhawara sosai a cikin yan uwa.
Don sun fara fadin yanzu ke nan su gwaggo kudidi nafi dauka a matsayin yan uwa a gareni fiye da sauran yan uwa don me komai ya taso nawa sai ace su gwaggo kudidine kawai zasu tafi ?
An rigada an masu komai na tafiyansu a yanzu don haka dole kowa yayi hakkuri da zancen zuwa tunda su ta zabi zuwansu tun farko don haka ke hari da Asiya dake Addah sai kuyi hakkuri a faki gaba kuma, ai yanzu aka fara.
Don dole suka jaye zancen tafiyan don sun kula cewa sune zasuyi wanan tafiyan donsune ya cancanci sujeshi sai gashi waisu gwaggo Aminane zasu tafi irinwuce an wajen dasu ya dace ace sunje.
Ranan kuwa suka shirya zuwa lagos inda a can zasu hadu dasu umma su wuce a tare dasu zuwa Hong Kong din su samemu kamar yadda aka tsara tafiyan.
Akwai kanwar mahaifiyarsu da kuma wata dake zaman gwaggon shi daya da zasu tafi tare nan ma gida maiduguri an kashe kudi sosai ma anan don taro zasuyi tankar maijego da yaran suna kasan.
Ana gobe zasuyi taron suna Maiduguri hjy falmata ta shirya da tawaganta suka bar kasan ta koma inda ta fito ko maigidan baisan zata koma wanan lokacin ba.
Sai labari ya samu cewa sun tafi ita da diyanta da kannenta da sukazo gida yin babban sallah kamar yadda suka saba zuwa duk shekara a wanan lokacin sukan yi ziyara su gana da yan uwa suyi masu alheri .
Sai gashi wanan karon haihuwana ya hanashi tsayawa don tun washe garin da yamma ya koma ya barsu a nan su.
Sai gashi taji cewa itama hjyr tasa ta juyo ta dawo turai a wanan lokacin gashi ba zaman lafiya tsakanin shi da ita tun lokacin dayayi aure suke kwasan fitina da ita sai hakkuri da juna sukeyi tsakanin su.
Wanan yasa ko zancen haihuwa sai a waya ya kira ya fada mata ya kuma kashe wayan shi gudun kada bacin rai ya biyo baya tsakanin su.
Sun iso lafiya sun samemu kuma lafiya inda yara sukaci sunan mohammad da Ahmed sunan mahaifina da nasa zuwan su umma yasa yanzu na samu hutu sosai banda aiki sai barci ko wani lokaci.
Haka yasa jikina yayi kyau sosai da alaman jegon ga karbi jikina idan ka shigo ba zaks taba cewa nice na haihu ba sai idan ka samu ina ba yaran nono.
Yanzu ma barci nake tun safe dana shige daki bayan mun gama karyawa sai wajajen karfe biyu gwaggo Amina ta tayar dani in basu nono shine fitowana lokacin.
Kowa na falon zaune suna hira mukaji ana nocking Fatimace ta fita duba ko waye muryan hjy falmatane a kofan take fadin kauce ki ban wuri don Allah.
Fatima ta kauce da sauri ta basu wuri ta tun karo inda muke zaune din ni inabawa yara nono a cikin yare na fara fadin su boye min yaron dake hannun gwaggo kudidi tun kan ta karaso haka akayi .
Suna mata sannu da zuwa ko kallon arziki basu samu ba sai kokarin shigewa takeyi zuwa dakin shi suna kallon ikon Allah.
Suka shige sai gata ta dawo tana tafiya takalmanta na basa sauti tun kan ta karaso take fadin (ke ina makulin wancan part din ?.
Ban kallo inda take ba naci gaba da abinda nakeyi ke bakya jin ina magana ne ta kara takowa zuwa har inda nake zaune a cikin wani isa da takama.
Mrs may i know who are ?
Kin shigo gida bakiwa kowa magana ba yanzu kuma kina tambayana key din gida haka kai tsaye ?
Itama din kallon mamaki take min kafin tace samun wuri ni kike tambaya ko wa nake nace kwarai kuwa son banga alaman hankali ba a tare dake.
Naso baki girmanki na shekarun ki da matsayinki na babba a gareni gidan miji amma naga sam ke baki san girman na gaba dake ba balle harni mm a girmamaki.
Don haka ba zan bada key din gidana ba don bai fada min cewa zaki zo nan ba nima kuma ba zuwa inda kike zanyi ba don haka ki fice min daga gida yanzun nan kafin rayuka su baci.
Au ashe har gidan ya zama naki ko ban sani ba ko dan yaran da kike takama kin kwaso sun zama naki a yanzu kike son ki fara mallake gidan ?
Zaki iya mayar dasu inda na kwaso su ai tunda shine bakin cikin ki dama kada na haihu da mijinki gashi kuma na haihu din kamar yadda baki so haka ba.
Haba Falmata ana zaune kalau zaki zowa yarinya da fitina haka tana fama da jegon ta kanwar mahaifiyar shi ta fada .
Kune baku sani ba don babu mai labarin cikin wanan yar iskan saijin haihuwa kawai akayi don ta rainawa mutane hankali taje gidan marayu ta dauko rainon diya .
Salati matar ta saka tare da fadin falmata sherin har yakai nan kina son batawa yara suna ga banza kiwa Allah ki bar wanan sherin tun bai fita ba .
Yara kowa yasan na mijinkine don gasu kamar kakinshi wurin kama har wanan cindon dake dan yatsan shi duk basu ragoshi ba a wurin kama.
In ma wani abu ya kawoki sai ki zauna har maigidan ya dawo saiku yita a gabab shi zaifi amma haka ba daidai bane gaskiya.
Zama kan ai dole inyi a gidan nan har na kare kwanakin da zanyi kasan nan amma saina tonawa wanan yar iskan asiri kafin in wuce.
Bako a cikin gidan nan ba don ko yini bakya yi a cikin gidan yau balle kwana sai ta jefo min wani kallo nace kwarai kuwa In kina musu ne mu zuba dake ga key nan na mika mata ina kallon ta.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ANA DARA, , , , , , , , ,
BY ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , , ,
1️⃣1️⃣4️⃣
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM, , , , AL, RASHID, , , , , ,
YAR UWA KIJI TSORON ALLAH KI DAINA FITAR MIN DA NOVEL DON KIN BIYA KI BARI WANI YA BIYA SABODA ALLAH👋
Kallon fuskana tayi itama da kyau wanda da alama mamakin karfin hali irin nawa take mamaki wai har itace karamar yarinya ke fadawa irin wanan gatsen a gidan mukhutar yau gidan mijinta da take da iko da ko ina na gidan.
Hannu takai da niyar figar key din daga hannuna amma sai taji kamar wani abu ya soketa a kafadanta haka kuma hannunta ya rike a wuri daya taji bata iya mikashi.
Acikin mamaki ta dago kai ta kalleni kamar zatayi magana sai kuma ta kara kai hannu da niyar ta karba da sauri naga taja baya ta juya da sauri ta tafi tana dan sauri a lokacin.
Binta kowa yayi da kallon a cikin mamakin abinda ya hanata karban key din daga hannuna a yadda tayi niyar fisganshi da karfin dole.
A lokacin muryan mama kanwar hjyn su mukhatar ke fadin duk iya shegen mace da shu,umancinta ai tazo karshe yanzu.
Duk yadda akayi akwai abinda tagano kukaga ta juya da sauri haka mama din ke fadi cikin takaici da bacin rai ga irin halaiyan falmata din.
Idan kaga Allah yayi halittanshi ga bawa to kabarshi kawai da abinsa ko kabi shi da addua don Allah kadai yasan dalilin yin bawanshi a hakan daka ganshi.
Naga biyu ke nan a rayuwana wana matsalan jinnun na sahiba ga inda zaiyi ranan nasa a yanzu haka a baya kuma ya taimaka mata wurin kareta daga sherin yan uwan mu.
Yau, da,ace badon mutanen dake saman kan yarinyar nan ba masu karfine haka da yanzuma an share tarihin ahalin yaya sambo ga baki daya a duniyan nan gaskiya.
Saboda ko irin sherin dasu yaya Nuhu suka shuka a doron kasa ko littafi baya daukan shi kai tsaye haka don a lokacin har muna ganin ta tarowa kanta mutuwa sai gashi yau sune suka kare a tsare a gidan wakafi suna daure don kawai son abin duniya da suka kwallafawa rayuwan su.
Ga na biyunshi yanzun ma na gani a gabana don wanan matar tana ganin kawar da sahiba ba aiki bane a wurinta yasa tazo har nan da niyar tozarci da kazafi a gareta.
Sai gashi farat daya ta fara raina kanta da abinda ta taka lokaci guda don tsafinta baiyi tasiri akan sahiba ba kenan a yanzu yadda alama ya nuna hakan nidai na fahinta .
Don kila dama da shirinta tazo garin nan don kawai tayi tashin hankali da fitina ta batawa mutane zukatansu don irin su haka suke da jan fitina ga abokan zaman su dama dan kada a zauna lafiya.
Allah sarki aida tasan kanta kawai su zauna lafiya shine alheri yanzu a gareta don ba kowane sihiri yake kamawa ba don wasu baya tasiri a jikinsu amma tsafi ko wani shirka da takeyi can sam ba zai taba tasiri a wurin yar mu ba gwaggo ta fada.
Abinda hjyn mukhutar ke nan ta fada itama har ta dage saida akai auren nan nasu gashi yanzu kuwa abin yazama alheri a yanzu tunda har ga rabo an fara samu na diya.
Falmata ta shuka tsiyataku iri iri a gidan mukhutar tana ganin ba wanda ya isa yaja da ita tako ina saiga Allah ya kawo yar nan a cikin rayuwan su a yanzu.
Har yakai hjy da kanta data haifeshi bata isa ta tashi taje gidan danta da sunan ziyaran kwanaki ba haka kuma bata isa a kawo mata diyanshi gidanta ba kai abubuwa dai da dama na nuna isa da gadara boyar Allah nan ta fuskaceshi a wurin falmata .
Yanzu kinji sherin da tazo dashi bawai murnan arzikin samun yaran nan bane ya kawota, tazone da wani sheri da zata kafa don tayar da hankalin mutane kada a zauna kalau, shine tazo wai yaran rikonsu aka dauko a gidan marayu ba haihuwan yaran sukayi ba.
Wanan kan da hankalinta kuwa gwaggo Amina ta sake tambaya don mamaki daya cikata lokaci guda a wurin tana kallon al,ajabi a filin Allah.
Tsab take shedanane irin nata tana ganin uban kowa tana iya yiwa wullakanci balle wanan da take kallo a makiyiyar ta a yanzu fiye da kowa.
Umma dai suna daki da yara ita da Fatima duk wanan abinda akeyi a katon falon gidan su basu sani ba don haka duk yadda hjy falmata taso taga yaran a lokacin abin bai yuyu ba gareta.
Da yake gidan babban gidane bamu san wainar da suke soyawa ba a inda suke sai gashi mun gansu sun fito sun tafi ko magana basuyiwa kowa ba a lokacin.
Lalai kin haifu Sahiba a cikin iyayyen ki yau Falmatace tayi saurin saduda haka har ta iya barin gidan nan kamar yadda kika fadi ba zata kwana a nan ba ba tare da wani hayaniya ba haka.
Zaune yake a office din shi suna aiki wayan shi yayi kara ya dauka yayi mamakin ganin kiran yar babba yasa a lokacin da sauri yakai hannu ya dauki wayan.
Yana ambatan sunan ta yake cewa ya suke ? lafiya daddy ta fada kafin ta soma fadin na dawo na samu mommy mu wai ta tafi Hong a yau din nan da safe ita da Anty Nafy.
Hong ya ambata hankali a tashe yana fadin ina office yanzu zanje gidan na duba idan sun shigo OK daddy ta fada tana kashe wayan yasan yarinyar bata da hayaniya kamar ba falmatace uwar data haifeta ba.
Yadda ya shigo gidan zaka gane hankalin shi a tashe yake lokacin haka ya karaso yana kallon fuskana ko zai gane wani abu ga yanayina.
Bai fahinci komai ba don kamar kullun yadda na saba taron shi na taryeshi da sannu da zuwa ina gaidashi da aiki kafin na gabatar mai da abinci duk da nasan baya cin na rana a gida.
Baiki ba yace yagode bai zauna ba su gwaggo ya duba suka gaisa yayi masu ya gida kafin ya juya zai koma falo yaji muryan kanwar mahaifiyar shi tana fadin.
Falmata tazo yau din nan da wani sabon zance da mukaji a bakinta wai yaran nan ba diyan ku bane daukosu kukayi gidan marayu don ku tayar dasu .
Daga inda yake tsaye yake ambato sunan Allah har yakai ga dafa bango yana fadin wanan wani irin zancen banzane haka mama ko dai falmata ta haukacene wai ?
Shina gani don kishin ya koma mata kamar hauka yanzu kuma mama sunana falmata take son batawa kome don wanan ba fatima tayiwa sheri ba ni kaina tayiwa sheri ai a idon mutane don ta sheganta min yaya ko me mama ?
Ina tsaye bakin dinning din ya fito da yanayinshi da gabadaya ya kara sauyawa a lokacin fiye da yadda ya shigo da farko gidan.
Zama yayi ya kurawa waje daya idanu na dan lokaci kafin yace ya kukayi da Falmata data zo ?
Kallon shi na danyi kafin nace nothing naci gaba da abinda nakeyi da wayana nothing bayan yanzu mama ke fada min abinda tazo tayi a gidan nan ina son jin komai daga bakin ki yanzune.
Ban boye mashi komai ba har abinda na fada na kwashe tas na fada mai yana saurarena har na gama fadi ya jawo wayanshi da sauri na dan rike hannun shi ina girgiza kai.
Kallona yayi nace kada ka kirata don Allah ka barta wanan fadan tunda bata sakaka a cikiba fadane namu na mata so ka barni da ita kawai.
Falmata bata da kirki don hakane nake son nayi mata iyaka akan diyana duk Iskancinta zan iya hakuri na daure da komai da take min a kaina amma wanan sam ba zan lamunci hakan ba.
Ina son diyana fiye da komai