Showing 285001 words to 288000 words out of 382072 words
uwan ki wanan zagin haka nazifa ?
Yar uwata ta ina me muka hada da ita kaima maye hadin ka da sune wai don ban gane me haka ke nufi ba wai kai kadaine a cikin dangi halan da komai sai kai ?
Ganin sunan ummane a screen din wayan yasa yace umma zan kira dan anjima kadan to yana asibiti uwar bin didigi sai a barshi ya huta.
Wani iri naji har cikin raina umma kuma na fadin don me zaki biye mata kuyi haka wanan ai shi zaku tayarwa hankali shida baida lafiya.
Umma wanan matar ko tana da hankali kuwa daidai baki biye mata ba kunyi wanan don shi kike gani bana son kiran shi idan bashi ya kiramu ba son gujewa irin hakan.
Zanko dinga kiran shi sai tayi abinda zatayi din idan na kira na fada ina haran gefe kamar itace a tsaye wurin.
Kinji wai asibiti ciwo ya kaishi gashi taki bari muji meke damun shi saboda bakar kishi irin nata na hauka rai bace umma ta kalleni tana fadin a, a banga laifinta ba akan mijinta take hakan ai.
Nikan kodana ce zan kira tun wanan ranan bankara komawa takan wayan shi ba kuma amma nakanji suna waya da umma tana masa ya jikin ?
Mun shirya zamuje kauyen su umma amma sai mun tsaya kaduna mun gaida ya Abubakar dan kafin mu dawo sai lokacin shiga kotun mu hakan zaisa yaga badon shi kanshi muka zo ba.
Mun shirya tafiyan mun isa kaduna a cikin dare don haka saida muka kwana washegari muka nufi gida daddy duk da bamu san irin taron da zamu samu ba a lokacin wurin su.
Sam nika bamji komai a raina ba don wanan ne karo na biyu da zan shiga gidan daddy kuma da ranan da ya Abubakar yazo damu daga lagos daga baya aka mayar damu kan wani dalili dabamu sani ba a lokacin .
Sai yau kuma da zan shiga don kaina ba kawoni wani yayi ba don ko yanzun din kan bin umurnin umma ce da tace a nunawa ya Abubakar bamu rike da mahaifin shi tunda ita umma tasan komai.
Karma yadda mukasani gidan nan kamar yadda muka sanshi a baya komai ba a canza mai ba in kin debe fenti shima din nasan lokacin bukin baby ne akayi shi.
Tun kan mu shigo muke jin muryan su a falon gidan babba suna dariya a daidai lokacin da mommy ke fadin kai hari wallahi baki da dama wallahi.
Wallahi Addah haka kawai ai gara in fada mai gaskiya kan wata wai Sahiba can daga sama dama ace mahaifinta yana raye ne har yanzu .
Ko kuma ta tashi a nan cikin mune kinga ka shedi tarbiyan yaro amma ni da nake son ya banbaro min yar gidan wani babban kusa zai kawo min zancen wata wai Sahiba can ana zaune kalau ?
Abin ko dadin ji babu fa yaro ya gigice min shiko mahaifin shi har da son mara masa baya akan karya wai meye ga Sahiba din ?
Mommy tace Allah dai ya sawake ai hanyar jirgi dabam ta mota daban dariya suka kara kwashewa dashi mommy na fadin aini tuni na kakabe shi da wanan zancen haukan modibbo zai kalli idona yace min shifa daya sani da sahiba ya aura tun farko.
Dafani naji umma tayi a bayana ta kada min kai sai na dan hade bakin cikin daya tokaremin makoshi lokaci guda.
A take nayi sallama daidai da shigowana falon nasu umma suna bayana har lokacin suka juyo a razane suna amsa muna a cikin rikicewa dukkan su daka gansu kasan a rude suke da ganin mu alokacin gidan.
Hjy mairo wai kune a tafe haka suna mikewa tsaye lokaci guda, mune fa umma ta fada har da fadin ikon Allah yanzun nan kuka saukane ?
A,a anan dai muka kwana jiya mukazo da dare zamu yola ne muka ratso nan mu gaida modibbo da jikin sa.
Ayyah aiko kinyi zumunci hjy hari ta fada tana wani dan kame kame a, a Ammar kin koyi waya da mutumin naka kuwa ?
Yace No a cikin turanci don shi yadda nake dan jin hausan baya ji sam sai guda guda yakan fada kuma ba daidai ba .
Zaune dai nake a inda na zauna sai mamakin su nakeyi don abin nasu ya kara kulle min kaina sosai lokaci daya.
Yanzu kan nasan tabbas wa yan nan mutanen ba zasu taba son mu ba kenan a rayuwan su gwaggo hari matar da muke ganin mutuncin ta sosai.
Don ta nuna muna so har da kauna a fili yanzu take fadan wanan maganan haka a kan mu mara dadin ji can da sauraro ga kunnuwan masu ji.
Ke ku fito ga Sahiba mommy ta fada a cikin waya nasan da yaran ta take wanan wayan lokacin ba dauki lokaci ba kuwa saiga Faiza da gudunta ta fito.
Muka rungume juna da ita ana yaushe rabo duk da raina yana bace a lokacin amma ganin Faiza din sai na dan sake jikina da ita.
Yan jan ajin saida suka dauki lokaci suka fito sun fito da fara,an su da farko amma lokaci daya fuskansu ya murtuke.
Don sun tsorata sosai da ganina wani irin kyau da dress cikin shiga ta alfarma irin namu na manyan yan matan lagos.
Su kansu yanayina kawai ya nuna masu a yanzu ba ajin su nake ba mun gaisa dasu a cikin girmamawa kamar yadda aka saba a can baya ban nuna masu komai a fuska ba suka samu wuri suka zauna.
Faiza ke fadin kwanaki kikace zaki dawo baki dawo ba Sahiba nace sorry my dear wallahi tafiyace ta kamani zuwa england daga can na wuce dubai mukayi kwanaki.
Na fadi hakan ne kuma da gangan a gaban su mommy din da diyan ta kice dai har fita kikeyi yanzu abin dai ko sauku babu ashe.
Nace kin san yanayin aikin namu haka yake muna shiga kasashe da dama ko yaushe da wuya ki sameni a lagos yanzu ai.
Dan guntun tsoki Nabila taja daga baya dukda taki sake sautin shi amma nasan ko umma taji wanan sautin na dago ina fadin Anty Amarya fa ?
Oh sun fita wallahi dasu Fatima dazun ana buki walima a gidan babban yayarta duk a cikin harshen turanci muke magana.
Diban lokaci nayi ina fadin umma mu tafi a cikin yarbanci gwaggo hari harda fadin ba zaku tsaya akawo maku abin sha ba yanzu ta aika yar aikinsu ciki ai No abarshi kawai zamu tafi jirgin karfe biyu zamu bi zuwa yola yau .
Amma muna son don Allah idan ba damuwa Faiza ta nuna muna gidan Abubakar din mu je can kallon juna sukayi don ita kanta gwaggo hari rikicin shi da matar shine ya kawo ta gidan.
Eh to ko yana gidama yanzu waya sani eh zamu daije gidan mu gaisa dasu koda baya nan idan tazo za a fada mai mun gaida ku ai umma ta fada tana mikewa.
Tare da fadin idan Alh yazo muna gaidashi suka amsa kamar ba komai a zuciyan su gaba dayan su kuma suka rakamu zuwa waje din ganin kwan koda me mukazo.
Rudewa sukayi lokacin da sukai arba da rantsatsiyar motan oga da muka shigo zuwa gidan nasu wanda nice kuma ke ja bamuzo da driver ba.
Umma ce tabawa su Nabila kudi har suna musawa tace bazan baku alher ku karba ba Nabila ko kuma kuna cikin masu zargin muna aikata wani abinda bai dace bane a can.
Da saur har suna hada baki wurin cewa yaran nasu su karba nidai na bude motar na zauna sai lokacin na kalli Nabila nace anty ya aiki kuma ?
Kallon juna sukayi kafin suyi magana Faiza tace cab aiki a yanzu ana dai nemane ai kaina na dan girgiza daga cikin motar nace ko zaku iya aiki a company nan garin.
Yanzu kan naga fuskan su sosai don washewa sukayi lokaci guda zamu fadawa daddy suka fada nace OK idan kun shirya saiku hada takardun ku zan tura akarba.
Daga haka Faiza ta shiga muka dauki hanyar gidan yaya Abubakar muka barsu a tsaye suna bin mu da kallon mamaki da al,ajabi.
Aiki fa yarinyar na ta fada gwaggo hari ta fadi tana sauke ajiyan zuciya nima wanan zancen barazanan ai nake mamaki yanzu.
Ku hada takardun naku koda yaya baisani ba idan yayi magana kuce dashi ninace ku bata muka karyan arzikin nata inda ya tsaya wanan kuma wani sabon sallo wai asan ita watace komai ?
Tasan cewa daddy ba zai yarda da wanan zancen ba yasa ta fadi hakana amma ai zamuga karyan ta a lokacin muna kwanan gidan ya Abubakae kiran su ya shigo ta wayan gwaggo hari take fadin.
Zancen aikin yaran nan a ina zasu sameki da takardan nasu ok za a aiko a karba ranan Monday din nan mai zuwa sai su fara fita .
Mun gama wayan ban tsaya wani abuba na kira malam bello na fada mai komai yace an gama har inda nake son a jemin su koba komai nayi hakane mu rama alherin dan uwan su garemu.
Suna ko gida ko awa daya ba akai ba aka sallama anzo karban takardun su da komai nasu ga opper din aikin guda uku an kawo masu har albashin da za a dunga biyan su a company sugar din dana filawa.
Waya mommy ta dauka ta kira number gwaggo hari da imani ya kasheta tana dauka take fadin me kika samu kuma ko daki ban shiga ba fa yanzu na iso gidan.
Bari ke dai yar uwa abin mamaki zai kasheni yau wallahi wai kin san yarinyar nan da gaske takeyi an kawowa yaran nan takardan aikin su har gida da albashi su da komai a wata.
Ke don Allah ki daina wanan zancem zolayan ina Sahiba taga wanan daman mustaphan ta dake zaune ya dago jin an ambaci sunan sahiba .
Mommy tace wallahi Allah zancen wasa ya wuce ga takardan a hannuna imani ya cikani nan zaune hari.
Wai ya akayi wanan yar ta samu wanan daman hakane waya tsaya mata take wanan iskancin da take so hakane .
Addah waiko kin san kila irin wanan baiwan na mahaifinta ta kwaso don in baki manta ba shima haka yake fa duk abinda ya dafa sai yayi albarka sosai wallahi.
To yarshi shita gado a yanzu ke nan kome don kaina ni ya daure ga baki daya don wallahi, , , , sai taji ta kashe wayan ashe Anty Amarya ce da yaranta suka dawo a lokacin.
Lafiya dai na ganku haka Anty Amarya ta tambaya saida ta nisa take fadin aiki yaran nan suka samu yau aiki kuma a ina aiki ya fito haka tsawon wanan lokacin da ake neman sa.
Wallahi ikon Allah daine idan rabon ka ya rantse sai maishi Sahiba ce tazo gidan nan itace daga tambaya sai ga opper mun gani har gida na company tauraro.
Sahiba fa a gidan nan tana ina ta sake tambaya tana dan waige waige sun tafi ai suna gidan modibbo dama shi suka zo gayarwa.
Mama don Allah mu bita can mu ganta Fatima data dan fara tasawa yanzu ta fada tace kuje ku gani ko zaku samesu a can din.
Yana da wuya su sameta don sauri sukeyi tace yau zasu tafi yola suyi sati daya a can jirgin karfe biyu zasu bi.
Yaran suka mike da sauri suka fita har sun manta su karbi kudin Napep saida uwar ta kirasu ta basu kudin suka kama hanya suna Allah Allah su samenu a can.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ANA DARA GA , , , , , , , ,
8️⃣5️⃣ BY, , , , , , , , , , , ,
ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , , , , , ,
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AL MUQADDIM, , , , , , , , ,
ONLINE PAID NOVEL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA BA TARE DA HAKKIN KOWA BA DON BIYA KI TURA DARI BIYAR 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK 08036959257
ALLAH SARKI AI RAINA BAYA BACI YANZU DON KIN FITAR DON NASAN AKWAI RANAN HADUWA SEE U👋👋👋👋
Haba mami kin ko san abinda kike fada ayanzu akan yar marainiyar Allah yarinyar dako lafiya bata dashi na kula maza har kike kokarin aibanta ta da irin wanan kalamin.
Me kaji na fada akanta yanzu na aubantawa gaskiya kawai na fasa game da ita shine kuma wani abin aibanta don kawai baku son ana fadin gaskiya idan an ganta.
Mami barun fada maki wani abinda baki sani ba akan yarinyar nan yau wallahi mami koda kikaga ina tallafawa rayuwan sahiba da suka fada maki tun kafin hakan .
Sahibace ta ceci rayuwana ta wankeni daga mugun zargin da ake min har gaskiya yanzo ya baiyana suka daina harata da sun kamani a wanan lokacin wallahi daurin rai da rai zasuyi min a lokacin.
Alh mahammoud da kanshi yake duke yana karatun jarida saidai yana jin su abinda ke wakana a tsakanin su yace.
Au itace yarinyar da ka fada min ke nan ashe data boye sani ka ta boye akan bata taba ganin fuskan kabama din da itama suke zargin ta.
Yace Daddy wallahi itace tana karama sosai a lokacin ko yanzu ma ai karaman yarinyace girman daine Allah ya bata a cikin lokaci.
Kafin ya juya wurin gwaggo hari din da tayi suman tsaye tana sauraren makusantan nata lokaci guda kan bayanin da bata taba sani ko jiba sai yau data tsunci zancen a bakunan su.
The boy kai ta nunashi da yatsa yace wallahi mami nafi karfin shekara uku muna wanan case dasu modibbo da kike gani kike tambayan shi abindake hadamu wanan matsalan ne ya kafe akan sai ya kamani ya danka a hannun hukuman su an kaini kasan biyu da suke zargin mu.
Labarin komai ya bata har zuwa wanke shin da nayi da fada mai wanda sukai mashi sherin ya kuma bincika har aka gano gaskiyan hakan gareshi.
Yanzu ga irn sakayan da take binku dashi ko ranan ina jinku da Addah a gidan kuna mata irin kazafin nan ke ga naki itace silar fitar muna dashi cikin wahala.
Yanzu kuma yaran Addah din duka uku ta sanadin ta sun samu wurin da zasu dogara da rayuwan su.
Irin wanan halin da kuke nunawa shine yaci yan uwan ku a yanzu dama shi sherri ai dan aikene don komai dadewa watarana sai ya dawo kan maishi yanzu me gari ya waya garesu don Allah ?
Don shi Nuhu ya dauka arzikin kota halin kaka yin sa akeyi a zauna lafiya baisan tarin nauyi da wahalan daya daukarwa kanshi ba ga hakan .
Idan baku daina hakan ba wanan halin karshe a kanku zai dawo har ita Addah dake da diya mata har uku a gabanta dakema mai da daya tilo ki jawa kan ki fitina a sanadin hassada irin na dan Adam.
Shiru tayi na dan lokaci tana kallon su kafin ta kai hannu ta share zufan dake karyo mata a goshin ta duk ko da sanyin Ac daya karade falon a lokacin.
Sahiba in banda wayau da suke mata suna amfana da basiranta da Allah ya bata ba wani hakalan iskanci ko shashanci a tsakanin ta da kowa idan tace eh ga mutum ita sheke nan a gurin ta eh din
Wai modibbone yaso ya kamaka daurin kuma daurin rai da rai dama ashe har akayi hakan ban sani ba ashe mami ta fada cikin mamaki ?
Kallonta dan nata yayi yana fadin wanan kuma kada ki zarge shi don aikin shi yakeyi shi, kowa kuma yasan haka ka,idan aikin su yake tunfarko.
A kan me zata zargeshi ma mijin nata ya fada shiba rantsuwa yayi akan aikin shi ba cewa ko mahaifin shi yai abu zai fada .
Faizace a gaba muna binta a baya tayi sallama a bakin falon nasu da kamshin girgi da yar aikin gidan keyi a lokacin ya karde gidan tun daga waje.
Waya takeyi yarsadan wanda hakan bai bata daman karba sallaman mu ba lokacin sai dai bin mu da tayi da kallo muna shigowa a wanan lokacin ne kuma shima ya tsaya da motan shi kofan gidan.
Yaran suna wasan su a falon koda muka shigo babban ce ta dago kai ta kalle mu ta sheda mu sai tayo gun umma tana muna oyoyo kafin ta sake umma ta dawo gareni har Ammar.
Wai amma kukan kunci da fari da har yar nan ta yarda daku haka kamar ta sanku dama ai ba wanda ya isa taje wajen shi banda mamanta da baban ta.
Wayan ta aje tana cewa yar ke maryam jimun yarinya daga ganin baki sai kiyo kansu da gudu haka kamar ta san su tana zarewa yarinyar ido a daidai lokacin da karamar tazo