Showing 6001 words to 9000 words out of 382072 words
kada ya sameni a wurin ya dakeni a banza umma tace dako kin tsaya abinda zai maki ke nan ya dakeki ya daki banza.
Iya wale dake jin hiran su ta juye baki tana fadin kin san kuwa baku da kudin zuwa police station yin kara.
Jin ta tsoma baki kuma sun san hakan neman fitina kawai takeyi dasu irin nata yasa da ido umma tayi ma yar nata signal da tayi shiru.
Suka kyaleta don zasu iya cewa dasune kawai iya wale bataje police station ba wurin sharia a gidan duk da yawan da gidan ke dashi na yan haya tallakawa irin su masu karamin karfi a garin suke dandazon zuwa wanan unguwan don kama haya acikin saukin kudi.
Karshe dai mahaifiyar sune tayi masu nuni da su tashi subar wurun jin iya walen bata bar zancen ba har lokacin.
Suna shiga daki Sahiba ta fara shirin fita uwar na kallon ta yadda take sauri tace yau ina zaki ke na ?
Ta juyo tana saka hula a kanta tace kati zan sara in kai titi in gani ko za a dace don yau na makara da fita taba mahaifiyar ta amsa tana mikewa daga duken da take tana daure igiyan takalman da zata fita dasu.
Dukawa tayi gaban uwan tana fadin zata fita sai ta dawo ta kalli yar nata tana mata adduan kariya da samun sa,a ga wanan fitan da zatayi din kamar kullun.
Shagon da suke sarin kati su yawata a cikin gari ta nufa da farko mai shagon ya hana mata yace yamma yayi a lokacin.
Sai dai yawan rokon shi da magiya data dinga yi yasa ya ji dan tausayin ta don sun saba dashi tana yawan zuwa shago yasa ya dauko suka kirga na dubu biyar ya bata katin don yasan yarinyar tana da kwazo sosai ga wanan sana,ar.
Ba nawa da sauri ta yanke shawaran a ranta ta bin layin motoci tana sayar da katin don idan an hada go slow wani lokaci suna ciniki a wurin sosai.
Nan ta fara bin motocin a gurguje da dan sauri tana fadin buy credit mtn or eirtel glo yin ko, inda wasu suna saye wasu kuma su koreta akan ta damesu da yawan talla din a lokacin suna cikin uzuri.
Har karfe shida ya buga ba tare datayi cinikin kwarai ba don ko layi daya ba ta kai ga sayarwa ba a lokacin.
Ganin hakan sai jikinta yayi sanyi hankalin ta ya tashi sosai ga yamma sai kara karatowa yakeyi a lokacin.
Hakan ya kara tayar mata da hankali sosai a hankali taja jiki zuwa gefen titi ta zauna don duk motocin dake jere a titin tabi ta tallata kantin basu saye ba .
Gashi tasan da cewa abincin su ya kare idan sunci yau dan cinikin da tayi ba zai ishe su shiga makaranta da safe ita da kanin ta.
Duk tunanen da takeyi bai hana idan mota tazo wuce ta gaban ta tace dashi buy credit Oga five hundred, two hundred own or one by credit na all services we have .
ZAINB IDRIS MAKAWA
ANA DARA GA, , , , , , , ,
BY ZAINAB IDRIS MAKAWA
BISSIMILAHI RAHAMANIN RAHIM ALAHAMDULLILAHI RABBIL A,LAMIN, , , , , ,
LITTAFIN NAN NA KUDINE YAR UWA KI BIYA DON ALLAH KADA MU RIKE JUNA DANI DAKE AKWAI GOBE YAR UWA, , , ,
Kanta yana duke tana faman kirgan katin dake hannun ta idan bayi missing din wani ba a cikin su biya ya hau kanta ke nan don mai shago baida hasara shi.
Card seller aka fada a cikin wata bakar moto da baka ganin wanda ke cikin ta sai idan ya bude zaka ganshi.
Irin wanda mu hausawa muke kira da motar muggan mutane don ba,a faye yarda da masu irin wanan bakin glass din ba.
Da sauri ta dago zuwa wurin da taji kiran ta tsaya saidai window motar kuma a rufe yake bata kaza ba tana tsaye kafin a kara bude glass din a daidai lokacin da take fadin.
Hurry, up Oga i wan, go nd pray is time for pray now ba tare da ta dago kai ta kalli wanda ke cikin motan ba da gani kuma tana a cikin sauri ne a lokacin.
Don yadda take dan girgiza jiki alaman sauri dai takeyi da gaske taji daga cikin motar ance.
Give me ten thousand mtn card da sauri ta dago tana fadin sir pardon you means mtn card only for ten thousand naira.
Sai kuma ta dan ruga da gudu kafin ta juyo tace i dey come oga i wan go nd bringam now zata ruga da gudu aka kara fadin and eirtel for ten , , , ,
Ai bata tsaya ba ta ruga a guje don tasan duk dadewan ta ba zasu wuce go slow din nan daya jeru a layi ba zata samesu ko gaba ne.
Tana zuwa bata tsaya magana ba ta figo roll din katin don tasan a yadda yake zuwa ta hado dana glo dana etisalat ta juyo da gudu mai shago na ihun fadin you you .
You abi you de crazy today play with my money like that ai bata tsaya sauraron shi ba ta tafi da gudu kai katin wurin motan.
Kamar yadda ta tsamata haka dinne ko sunyi nisa a lokacin haka ta bisu a guje tana kwala ihu har ta samesu ta dan kwankwasa glass din tana fadin here is d card oga all is for ten ten thousand making Fourty thousand Naira.
Ta saka a cikin motan saman jikin mai shi da sauri yace you be mad who ask you to bring all dis daga gefen shi aka miko kudi yana fadin ya bari ta wuce kawai ga kudin ta.
Godiya ta fara sake mai tana fadin oga tank you may god bless all your family and protect dem tana daga masu hannu .
Yau itace farar rana a gareta cinikin dubu arba,in da dan kai haka tasan tana da kudi da yawa ke nan a yau sai lokacin tasan ta gaji sosai ta fara dan jan kafa a hankali zuwa wurin mai shagon data dauko katin ta iske shi ya cika fam yana zaran ido yaga ko zata dawo gareshi.
Sai gata ta bullo gaban shi tana washe baki tare da fadin oga don bese with me na market matter isee that is why a run to catch d money now now i sell fourty thausand own.
Beautyful girl you good wor ya fada yana washe baki a take ta hade rai tunda ya fara fadin hakan ta katse shi da fadin .
Oya give me my share, i wan go home now my mama are wetin for me at home to come with something.
Haba beauty u no go livan till tommorow to get more money than dis one wen i go give u now.
No give me my money today ta fada cikin kara tsuke fuskanta gareshi don ta gane wayau zai mata ga hakan don yana iya fadin ba haka bane idan har ta bari goben yayi.
Don dole ya bata kada ta tara mashi mutane a shago don haka ya debo kudin ta ya bata bayan sunyi lissafi ta tafi.
A hanya sallah ya risketa don haka ta tsaya a wani masalaci nan bakin layi tayi sallah maimakon ta nufi gida wurin da ake sayar da masara sari ta nufa don taga kamat za a caba a wanan sana,an zata gwada ta gani ta dan hada da sayayan dan abinda zasuci ta nufi gida.
Koda ta isa ta samu ana hayani a gidan fada ya hada mijin wata matar gidan tare da iya mulika suna cacan baki kamar zasuyi danbe ga wasu hausawa suna girke a part din su tayi masu sannu ta shige zuwa nasu dakin dake can kurya da gidan.
Ta samu umma da Amar hankalin su a tashe don karo na biyu ke nan umma tana tura Amar zuwa kofa ya duba idan zai hangota dawowa gidan.
A gurguje ta shigo ta gaida mahaifiyar nata kafin ta juya ta fita da sauri alwala tayi a wajen ta gabatar da sallah isha,i dake kanta .
Sannan ta zauna a gefen su tana bude kayan data dawo dashi din ta zaro abincin da tasan mahaifiyar su tafi so tuwo shimkafa da miyan taushe saidai ita da Amar basu damu da tuwo din ba sosai.
Nan umma tashiga tambayanta take bata labarin komai suna cin shikafa dafa duka a cikin take away tare da Amar.
Umma gobe idan Allah ya kaimu masara zan gasa da safe ba zan shiga schoool ba ta fada tana kai shikafan dake shakesu a bakin ta.
Masara Sahiba ina kuma kika kwaso masara tace da kudin dana fada maki na samu a yau di naga an fara wanan sana,an ko ina yasa zan gwada in gani ko akwai samu a cikin sa.
Karatun ki fa Sahiba uwar ta tambaye ta fuska ta bata a lokaci guda kafin can tace umma na dan lokacine wanan tallan ai.
Kaga wanan unguwar mazauna cikin ta yan kazo nazo ne shine mafi hatsarin unguwa a cikin garin nan kaf don in kana neman yan iska a ko wani irin yare kazo nan zaka samesu .
Ya juyo yana kallon mai maganan daga gefenshi sai alokacin ya dan nisa ya juyo yana fadin naga alaman hakan tun shigowan mu ai.
Meye sunan unguwar kai tsaye yace dashi AJAGULE sunan unguwar ai kaga baida wani nisa damu amma yanayin su yasha bambam sosai
Don shi gaba daya erea din yayi kama dana yan duniya tun daga yanayin shigan su zaka gane hakan ai .
Shi yasa ka gani ban faye shigo wanan erea din ba idan ba aiki ya kawoni nan ba sam bana yarda in shigo don sai su nakasa mutum a nan ga banza ba wani aiki bane garesu .
Ai kuwa dai da alama ga zancen ka don yanzu na fara nazarin yan unguwar a hankali simo ya juyo da sauri yana fadin dama kasan wani ne a wanan unguwar ?
Kai ya girgiza yace ai na fadama wanan ne karo na na biyu danazo aiki a lagos yace i see.
Saidai ka shirya gobe iwar haka zamu saje a cikin su don dole mu aje wanan kayan da komai namu mu zama daya da yan unguwar.
Hakan na da kyau ya fada yana lumshe idanu har suka kai inda zai sauka sukai sallama ya fita ya shige masaukin shi dake cikin APAPA.
A gagauce ya samu wuri yayi sallah cikin sane dake kugi ya tuna masa da abinci don tun karin safe yana office suna tsara yadda zasu kamo mai laifin dayazo kamawa din.
Yana zaune a wurin yayi odan abinda zaici wanda ba wani abu bane illa dan ruwan zafi da kayan shayi har aka shigo da abincin yana zaune yana nazari.
Babu abinda yake a zaunen sai nazarin da tunanen ta yadda zai fito wa wanda yazo kamu tun daga wani kasa kuma suke tuhumar yana nan Lagos ya boye.
Gwaunati ta saka hannu ga aikin nasu don a yanzu ne idan yai nasara ga kamun wanan mutum din sunan shi zai yi fice a cikin aikin sa sosai.
Sanin inane lagos yasa ya zauna yake nazarin komai yadda ya dace yasan kowaye zai kama da irin alakarshi da wasu manyan kasan shi yasa akai komai a asirce ba tare da kowa yasan da hakan ba.
Don hakane yake son shiri na musanman akan wanan aiki don ko simo abokin aikin nasa na nan bai san wani shiri da yakeyi ba.
Don simo din ma dan adam ne zai iya juyawa a barshi a ciki tako wani lokaci kuma gashi dan kabalan yarbawa kuma dan kabilan zasu kama ke nan dolene yayi taka tsantsan da hakan.
Mace mace ce ta fado mai a ranshi don haka ya zama dole ya hada da macen to ina zai samota agarin nan ya tambayi kansa ?
Da wanan tunanen ya kwana a ransa yana faman nazarin ta ina zai fara gashi baison Simo yasan komai akan shirin shi din a yanzu.
KADUNA
Hajja Addah ta fito don jin gidan shiru da tayi babu motsin kowa daga cikin yaranta a lokacin gashi har karfe shidda da rabi na safe.
Dakin ta tura taji shi a bude suna kwance dukkan su suna barci hankalin su kwance kamar ba su ke fita karfe bakwai da rabi na safe ba zuwa school.
Hjy Addah ta tsaya cak ta rasa abin da zatace don takaici a fili ta furta wai ya zanyi da yaran nan a rayuwana ?
Wanan wani irin rashin hankaline haka ace ko sallah safe babu wace ta tashi a cikin ku tayi shi kan lokaci balle kuma har kuyi shirin makaranta.
Tana fada dasu cikin hasala sai Nabila ta dago tana fadin mommy har gari ya waye ne haka ashe shine ba,a tashe mu ba tun dazun .
Wani harara Addah ta watso mata kafin tace a hasale ai to ku jarani kullun nazo na tayar daku kada ku saba da lokacin sallah a zukatan ku ta juya zata fita daga dakin
Sai kuma ta juyo tana fadin wani albishir da zan maku shine kada ku manta yau kune zaku mana abin karyawa a gidan nan don talatu ta tafi kauyen su tun safe a can zata kwana.
Ba shiri kowan su ya mike daga yadda suka lafe da farko suna hada baki wurin fadin mene mommy talatu tayi tafiya ?
Ta juya tana fadin idan kunga dama kada ku tashi ku gaida Allah sai ku gyara kwanciyan naku ina daki in an gama abin karyawa kukaiwa hjy karima nata a part din, nikuma ku tayar dani nima in karya ta fita abinta daga dakin ba tare data kara sauraren su ba..
Ba shiri suka mike suna rige rigen shiga bandakin a lokaci guda dan gaba daya yau sun san nasu ya samesu dan sauki shima karfe takwas zasu shiga lecture kuma yau uku zasu dawo gida.
Sun halin mahaifiyar nasu kan abinda ta fada ba fashi koda hakan yana nufin zasu rasa karatun sune na ranan ba zata janye abinda ta fada aiki kan sai sunyu shi a gidan ranan.
Sunyi dabaran raba aikin a tsakanin su su ukun mai gyaran gida da mai fere dankali da wace zata dora ruwa da sauran aiyu ka har Allah ya taimaka suka hada komai.
Addah batayi barci ba koda ta fadi hakan tana zaune tanaci gaba da azzakar don neman gafara da dacewa ga ubangiji tare da neman kariya da tsari ga iyanlanta ga baki daya.
Suka shigo suna fada mata sun hada komai yana danning din ta kai kawai ta gyada masu taci gaba da abinda takeyi.
Uwa ta gari ke nan idan yaro yayi ba daidai ba a cikin hikima zaka hukuntashi gobe da kanshi zai gyara kuskuren shi kan abinda ya aikata din idan ya gane hakan.
Wayan tane yai kara ta dauka tana duban mai kiran ta da safe haka dan murmushi ta sake kafin tace modibo da safe haka.
Ta dauki wayan da sallama ya amsa mata yana a cikin shagwaban daya saba yana fadin uwata mai sona da kaunata antashi lafiya ya kuke ya gida da sauran yan uwa.
Ta dan lumshe idon tare da fadin lafiya ya aikin anyi nasara ko har yanzu da saura mami aiki ai bamu ko fara ba tukun nan dai yai mata bayani a gurguje tayi mai adduan nasara dana kariya tare da fadin ya kula da kanshi kamar kullun.
Yau tun safe babu abinda nakeyi sai shirin fita da masara da zan gasa a bakin titi duk da alaman hadarin da ake hadawa a garin sam wanan bai daga min hankali ba ko kadan.
Umma daga daki take fadin Sahiba idan masaran nan ba zai baci ba ki bari har zuwa gobe don yau kinga yadda garin ya tashi da hadadi haka.
Ga wuri ya koma tankar gari bai waye ba umma ko kin manta nan lagos ne ba ruwan su da hadari ko ruwa don wanan baya hanasu harkan gaban su.
Dole tana kallo haka diyan nata ta shirya ta fita zuwa vakin titi da kayan gasa masaranta data ara wurin iya wale data bata aron kayan da gaiya bisa rijejeniyar bata dari biyu idan ta dawo daga tallan.
Dukko da tasan ko ita riban da zata samu ba zaifi dari uku ko biyun ba ga dan masaran data saro din don gawa a bakin titi.
Don kyata da ganin iyakarsu tayi hakan don kawai ta samu hanyar da wani fitina zai hadusu ta kware masu zani a kasuwa don sunfi kowa zama matalauta a gidan hayan nasu.
Tun fitowan Sahiban taga yadda hadin yagame baka ganin komai sai duhun ruwa mai shirin tsunkewa a kowani lokaci.