Showing 342001 words to 345000 words out of 382072 words
.
Kowa ya tsaya a matsayin shi don bamu kawo gareta ba mu har yanzu don haka kada ki jefo muna zancen ta a nan ki zo zaki kafa muna doka haka tsarin mu yake ga al,adan mu.
Kallon gwaggo hari din matar tayi ba laifi don a tsare take da gani itama watace mai fada aji ga yanayin ta don haka ta dan daure ta sake fadin .
Au naku sallan da kukazo dashi ke nan munan kujerane daidai muke da mazaunan kowa don haka zamu zuba daku ga haka.
Zakuyi kunya kuya kuwa wanan karin dan yar mu na daidai da kowa ta kara binsu da wani kallon yare dayan tayi mata suka fice daga dakin a fusace kafin hjy karima tace kai nadai gode da hanza ya tsara hakan baki ga wani kallon wullakanci da suka shigo muna dashi ba da farko.
Sai bin mu da kallo takeyi daga sama har kasa tana wani mere bakin ta sun shigo da niyar wullakanci sin zo gida ai kodame suke takama kuwa gwaggo harin ta sake fada.
Lalai za ai zama a wanan wurin kuwa gwaggo Amina ta fada sai hjy kafima tace in dai wanan ne zasuyi daidai dan banjin komai a gun Sahiba ni.
Karamci kan mun gashi karfe takwas na dare an gama shirin dinner din da aka shirya za, ayi harni din na gama duk wani shiri don nasan da hakan kada a girsheni yasa wanan custermer din nawa ta hada min kayan dinne na gani na fada tun daga dubai aka kawo min su a hade.
Duk wani wanda ke wajen saida shigana ya burgeshi don zakace nidin wata yar sarkin yarbawane a yadda nayi ado da tsara jikina don ba doguwar riga bace a jikina lokacin, zanine da riga na wani lace dinkin buba irin na yayi daya sha haduwa wurin kyau.
Don duk inda na juya walkiya nakeyi wal wal daurin zaninma na yarbawane nasan yadda suke komai dan haka tsarin yarbawa na tsara a komai nawa wurin.
Kowa ya zuba ido zan shigo aga fuskana a lokacin don duk basu sanni ba auren ma a bazata yazowa mutanen shi da yan uwan shi.
Saidai lokacin da muka shigo din fuskana yana a rufe da dan wani mayafi dayai shige da kayan sai walkiya yakeyi ba mai iya ganin fuskana lokacin.
Kamshi kan shi angon sai da abin ya hau kanshi balleni da kamshin yake a jikina yana hawa min sosai ina jinshi aikin anty amarya da gwaggo hari ne wanan din.
Cool music suka saka na oldscul a wurin na wani mawaki nan abokansa suka dauki tafe da shakiyanci gareshi wasu yan mata masu kaya iri daya suna gaba da bayan mu su hudu.
Daga inda hjy Falmata take zaune da tawaganta tace wanan ai iskancine ashe dama haka suka shiryawa abin ban sani ba har suna fadin wai yazo a kuraren lokaci haka ?
Bana fada maki naga suna shiri ba lokacin a bayana su anty hawauce faiza hamida da zainab yar wurin gwaggo Amina sune a matsayin yan matan bukina.
Ba irin zagin da anty Nabila bataiwa hauwa ba da gwaggo hari tace sune za a dasu ba a yarda wani dan waje ya shigo yaci da cewan sauran yan uwanmu dake wajen bukin wai.
Nan yaren kanuri ya tashi don ganin su don ba wace bata hadu ba a cikin su wurin sai nasu adon ya bambamta dana gaban mu din.
Bayan mun zauna aka dan gabatar tare da bayanai nan shagali ya fara masu bayanan da sharhi suna fitowa sunayi.
Gwaggo hari ta karbi abin magana ta soma magana tare da gabatar da kanta a matsayin gwaggona take nan ta fara fadin tau yan maiduguri.
Ga amanan uwargijiyan ku nan Sahiba bafulatanan asali sai wurin ya dauki hayaniya kowa da abinda yake fadi tana dariya, .
Tace OK duk da dai gida tazo ba wani waje ba don nan gidane gareta ango kuma uncle dintane yanzu kuma mijinta.
Kiji min abinda wanan matar ke fada wata daga gefen uwargida ta fada tace haukane kawai irin nasu kafin ta gama zance taji gwaggo hari na fadin.
Nace hakane don shi mukhatar kamar wani jigo yake gun yar mu koda bai aure taba ga kuma aure a tsakanin su yanzu Allah ya hada.
Don haka zan kira garesu da a zauna lafiya uwargida muna mai baki hakkuri tare da kara danka amana a gareki dan nauyin bana mukhatar bane shi kadai a yanzu nan dai taci gaba da bada shawara kan zaman lafiya tare da dan barkwanci ta fita wata kawar gwaggo din darta rakota ta shigo tayi bayani itama kafi ta fara bayani .
Inda ta bukaci hankalin mutane kan za ayi budan kai a lokacin daga can hjy falmata da kungiyan ta suka soma fadin wanan ai iskancin yan kadunane zasu kawo mutane a nan su nuna wayewa da iyayi kowa wasukafi wayewa suke gani oho ?.
Kowa na kallo aka kawo kujeru biyu yadda ta buakata aka bukaci ango ya fito ba bata lokaci ya fito ya zauna a zaton mutane nice za a kira sai kawai ta kira dj dama ta fada mai sai ya saka mata kidan uwargida rangida don Allah jama,a ku tafawa uwargida hajiya falmata mukhatar wurin ya dauki tafi lokaci guda.
Yatsine ta fara daga cikin su wata wace ta fisu shekarune ta taso tayi mata magana kafin ta mike sauran suka biyo bayanta suna tafe da ihu suna zuba mata kudi.
Nan su faiza su fatima suka fito suna kwasa don wanan fagen amaryane wai shine hikimar su gwaggo don wani idan ya wuce ba zai bada komai ba.
Ta isa a cikin izza ta zauna don gaba take da maigidan don haka ko kallon inda yake batayi ba ta samu wuri ta zauna kafin a bukaci su kauwace amarya zata fito fili.
Nan ta fara fadi a cikin yare tana fada tana fadin na fada maku bazan fito ba wurin wanan iskacin amma ya hafsi tace sai nafito waya sani ko sabon iskanci zasuyi min a nan kuma.
Shidai murmushi yayi yana jin abinda take fada baidai yi magana ba iyakan shi ido kallo daya zakai mai kasan yana cikin damuwa a lokacin.
Bayan sun fice daga ita sai shi a tsakiyan filin zaune kowa yayi shiru ana kallon su sai kuma hasken wurin ya dauke aka saka dum light wakan fulani ke tashi a cikin cool music zabayen ke kirari ga amarya.
Gudan da wanan hjyn tayi yayi daidai dana cikin kidan su faiza ce suka hawo sukai min rakiya har zuwa inda suke zaune din ina zuwa gaban su na tsugun na duk hankalin jama,a yana wurin mu ana kallon me zanyi a lokacin Amira ce ta iso da cup's biyu a hannun ta saman ture ta miko min.
Na dauka na tsiyaya ruwan madaran dake cikin kwali na mika wa mukhatar din ya karba sai tare da dan matse hannuna a cikin nasa sai dai na danji zafin na daure na sake tsiyayya wani na mikawa uwargida kin karba tayi naji yayi mata yare ban dai san meya fada mata ba lokacin ta karba.
Gurfane nake gaban su sai ihu ke tashi holl din ina nan a yadda nake mai magana tace Alhamdullahi amaryan mu da alama mai ladabice ga shugaban nin ta .
Yadda ta gurfana haka a gaban maigida da uwargidan ta tana neman zaman lafiya a tsakanin su sai muyi masu fatan alheri dangin ango kuma su fito tare da abokan arziki da masoyansu suzo su taya uwargida da ango sayen bakin amarya .
Wuri ya dauki ihu da sowa dangin shi suka fara fitowa suna jefa kudi kafin na abokai su shigo suka cika wurin da takardun dolers na kudi.
Har lokacin gurfane nake a gaban su sai kokarin bude min fuskana wasunsu keso na hana suga fuskan suna fadi ai sin biya don haka in bude har anty hauwa tazo tafitar dani a cikin taron tunda mutanen ba karewa zasuyi ba lokacin.
Amma har aka watse kaina yana saye da wanan gyale da bazaka iya ganin fuskana ba sosai hakan ya fara saka zukatan su wasi wasin ko yaya yanayina yakene oho.
Gashi dai a jiki ya nuna ni farace sol ga tsayi ma daidaici alaman dai zubin fulanice ni kuma ance masu ai bayerabiyar lagosce ni da farko.
Da dabara muka sulale dan ba wani dadewa akayi ba a wurin dagani har angon kowa zuciyar shi yana cunkushe da abubuwa.
Ko sha biyu mu bamu kaiba muka dawo gida ba tareda kowa yasan da barin wajen namu ba sai su gwaggo da na dan rubutawa text a waya lokacin.
Suka sanda mun bar wurin zuwa gida hakama shima ya turawa wasu abokan shi da uwargidan shi cewa ta tafito zai tafi gidashi .
Ta dauka ina cikin wurin taron take fadawa kawayen ta wai ango fa yace ya gaji shi zai tafi gida ai dama tasan irin wanan taron ba damuwan shi yayi ba shi shirin yan uwanshi ne kawai.
Bayan tace ya tafi zata zo tare da kawayen ta ai shine kuma wata yar uwarta ke fada mata cewa ai amarya tabar wurin tun dazun itama.
Sai kuma ranta ya baci dajin hakan nan suka fara fada wai ana munafuntar ta ance amarya ba ranan zata zo gidan ba kuma gashi sin tafi da maigidan gida akace.
Nan take ta mike a fusace makarrabanta suna mara mata baya itama tabar wurin zuwa gida saidai ta samu gidan a rufe da alaman ma bai karaso bashi.
Mamakin hakan kuma taji zuciyarta na azalzalanta ta shiga danna mashi kira taji yana inane yace gashi karasowa dashi dasu maina ta kashe wayan.
Tana maijin zafi a zuciyar ta na kishi yana azalzalanta lokacin suka shigo katafaren gidan nasu bata ko son yin magana sosai a lokacim don kishi.
Karshema ta haye sama ta barsu a falon ana mayar da fadi tun bayan fadin da wata yar uwanta tace da alama dai amaryan tana da kyau a fuskanta don yadda naga yan uwata din suma.
Daga haka tamike tsam tare da fadin wai ni mukhatar yau yayiwa kishiya har ana kiranshi tsakiyn fili yana fitowa kamar wani karamin yaro can dashi tana kaiwa nan taja wani irin uban tsuki .
Shigowan mu gidan kai tsaye na shiga cire kayan jikina da alokacin sun dameni da nauyi bayan uban kudin dana kashe wurin hadasu iyakar aikin su ke nan wanan ranan don ni a rayuwana banson saka lace ko atamfa nauyin su nakeji a jiki ko don ban saba bane oho ?
Wanka na shiga na dade a cikin bayin koda na fito na samu su gwaggo sun shigo an dawo dasu gida suma lokacin.
Sai hiran bukin sukeyi a tsakanin su kafin anty Amarya tace amma wanan uwargidan kan da alama tana jin wani abu wai girman kai da izza ko madaran da sahiba ta zuba mata fa bata ko kurba ba.
Daga can inda gwaggo hari take zaune take fadin ai irinsu dama sai anyi takai dasu tunda bai taba mata kishiyaba dama yanzu zatafi jin abin a zuciyar ta sosai.
Kinsan idan an maka a dan tsakatsakiyan nan yafi sauki da ace saida aka kwashi shekaru irin haka za aima balle wanan kan gaskiya akwai aiki.
Shine ni ban gane ba wanan aikin da suke faman kira ko wani lokaci a iya tunane na kasa gano aikim da suke nufi dani har yanzu gareta ?
Sallama akayi aka shigo muna da wasu manyan kulolin abinci tare da plate dakin nan su gwaggo suka shiga gaidasu da aiki suna fita wasu kuma suka shigo dauke da kayan shayi dakin.
Gwaggo hari ce ta kalleni tare da fadin diyata me zakici ko shayin za a hada maki tana bude kulan abincin ferfesu ne a cikin dayan na kayan ciki.
Shi kuma dayan kuma na soyayyan naman kazane shake a cikin shi sai plates masu yawa da aka kawo dan bukata.
Nan wasu suka fara ci wasu kuma suka shiga wanka tea mai kauri anty amarya ta hada min ba tare da bread ba ta zauna a kusa dani saida na shanye na miko mata cup din.
Karba tayi ta aje kafin tace dani saura wanan abin ta miko min wani dan cup dake cike da fresh milk na karba ina bata fuskana don dole nasha sai a lokacin ta dan fara min bayanin amfanin sa dayasa suke ban tun a kaduna kuma yanzun ma zata bar min saura na karasa sha.
Fuska na kara daurewa lokaci guda kafin nace da bata ban ba gaskiya duk wanan ban dauke shi da wani amfani ba .
Zakizo ki nema a guna wata rana tafada tana dan dariya na girgiza kai tare da fadin ku daina wahala da kanku ga wanan din koda yake dai kun yarda dashine don nayi saidashi ina karama a lagos na fara bata labari yadda akayi na fara wanan sana,an har mata suka gane suna saya a guna sosai lokacin .
Tayi mamaki kwarai ga labarin dana bata din take fadin kai sahiba gaskiya an auna arziki da basu sakin bacewa mutane ba tun lokacin.
Don irin hakan sai a nemi mutum a rasa sun daukeshi tunda suna son shi har zai iya ganin su dan zaman da mukayi da Anty Amarya a yan kwanan kin nan yanzu.
Yasa na kara fahintar ko ita waye a yanzu mace ce mai saukin kai da saurin fahinta amma kuma bata son sam wani ya zo ya nuna shiya fita mussanman a gidan mijin ta ma,ana dai macece dai mai kishi ita da jajircewa wanda hakan wasu mata suke.
Wanan yasa naji na yarda da ita har zan iya maganan abinda ya dami zuciyana da ita din kafin su tafi su barni koba komai yadda suke nuna min kulawa da kauna kai tsaye ita da diyanta a yanzu yafi min wanda mommy ta nuna min a baya.
Sai naji kawai na aminta da ita tambaya na farayi mata akan zaman auren hausa tana ban amsa tare da bayani daki daki ina gamsuwa da hasken da take kara min din a lokacin.
Na kuma gamsu din da abinda ya daure min kai din sosai a yanzu ta walwale min su ta yadda na fahinci yadda abin yake.
Munkai wani lokaci bamuyi barci ba muna hira kusan mutanen duk sun shige dakunan da zasu kwanta sin kwanta ko a lokacin mukasha hira yadda har banso tace zata kwanta din ba.
A nan take fada min zamu zauna da fatima don Amira tana da jerabawa in yaso idan ta gama sai fatima din ta dawo ita ta zo ta zauna dani.
Nayi godiya don gaskiya hankalina ya tashi da ganin irin mutanen da zama ya hadani dasu a yanzu suma din dai kamatace don ba hausa sukeji sosai ba yare yafi karfi a harshen su gaskiya .
Don haka nasan zaman za,a dan sha wuya a tare dadin abin dai akwai matsala gaskiya duk da dai nasan ba wani kasancewa a tare zamuyi dasu ba dama.
Washegarima abin arzikin bai kare muna ba don abin karyawa ne aka dinga shigo muna dashi a daidai lokacin da wasun mu suke barcin gajiya wasu kuma suke wanka a lokacin.
Ni dai tun kan gari ya gama haskawa nayi nawa wankan na shirya na koma na zauna a can kuryan dakin da muke ni dasu Faiza da sauran yan uwa ina bin kowan su da kallo tare da nazarin su da abinda suke fadi lokacin.
Sai bayan sun gama karyawa ne su gwaggo Amina suka shigo suke fadin in saka mayafi zamu gaida hjy mahaifiyar su mukhatar din.
Buje da rigan atamfane yar super a jikina da akaiwa dinkin buje da riga fetet daya dane jikina ya fito da shekaruna a fili sai kamshi dake tashi ko ina a jikina.
Mayafi na yafa daya shiga da kayan sai flat shoes a kafana simple makeup ne a fuskana da nayiwa kaina don nasan abinda zai min kyau a fuskan nawa.
Tsakiyan su nake sun kewayeni mukayi sallama a kofan falon da zai sadamu da dakin hjy din idan mun shiga daga cikin part din gaskiya ginan ya hadu duk da kaina a dan duke yake amma ina ganin yadda ginan ya tsaru.
Tana zaune falonta tare da bakin su da gani basu jima da gama karyawa ba suma a lokavin don anata fita da kayan abincin da akai amfani dashi a falon.
Sallaman mu yasa su kara dan natsuwa suke fadin sannuku da zuwa muka shiga muka zauna su gwaggo suka zauna a saman kujera yayin dani da yan matan muja zauna a kasa daga gefe aka shiga gaisawa.
Nan su gwaggo suka dora da fadin toh hjy ga yarki nan mun kawota gareku amana yo ai wanan gida tazo don nan gidan sune itama.