Showing 201001 words to 204000 words out of 382072 words
bama balle har su fara aikin da sukajeyi a can sun kira oga sin fada mai yace su sanar muna nan kaduna.
Ku dawo nan kaduna kawai kada ku kara kwana a kano din zan shiga da kaina next week in Allah ya yarda.
Yemisi ta karbi wayan tana maganan banza da dan sauri sauri nake magana dan haushi kawai sai na katse layin.
Na dago kai na kalloshi sau biyu muna hada ido dashi yayin da nake wayan don haka ina gamawa na mayar da hankalina a wurin shi.
Daga umma ke zaune take fadin sun samu matsalane acan din ko na gyara zama ina fadin dama nasan hakan zai faru tunda mutane basa son gaskiya yanzu .
A sake ya dago yana fadin suwa ke nan umma kaida gani kasan a cikin dauriya yake maganan tasa lokacin.
Umma ta fara zuba mai labarin abinda ke faruwa duk da daure fuskan danayi lokacin amma haka ta labarta mashi komai game da zuwan mu din.
Kanshi ya kara girgizawa kafin yace dani wani company ne a cikin kuke bincike a kai ya tambaya yana kallona.
Madaidaitan idanuna na lumshe kafin nace dashi na maigidan mu dake garin nan tare da yi masa kwatance yadda zai gane su.
Kina ganin zaku iya da wanan aikin kuwa da kuke rainawa a yanzu don nasan masu hurda a wurin a baya can shu,uman mutane sosai don haka yawancin baki masu masana,anta a garin nan suke kuka dasu.
Na sani yaya saboda hakan ne ai na zabi nazo nan din don sanin irin halinsu danayi tun kan muzo din.
Kibi a hankali don yanzu mutane sun baci sosai balle suna ganin ki karamar yarinya haka dake zasu nemi illanta maki rayuwan ki.
Nasan komai yaya a kansu har dama abinda basuyi tsamanin zan sanshi ba game dasu don haka zan gwada sa,a na a kan su yanzu.
Haka nada kyau idan kuna da wani matsalan da sai kun nemi taimakon mu zaki iya kiran layina insha Allahu zan taimaka maku dashi.
Nagode yaya Allah ya kara girma amma nasan basu shirya yin lalama akan matsala ba don tun yanzu sun fara kawo muna hari akan aikin sun gamu duk yarane ba wanda yakai shekarun su a cikin mu.
Mikewa yayi yana fadin mama ni zan tafi dama wanan tracker din ne ya jawoni a yanzu sai na sake juyowa da fatan baku da matsala a yanzu dai a nan ?
Bamu da matsalan komai a na gaskiya don komai kawo muna shi akeyi basai mun saya ba ta fada mai cikin kulawa.
Ok ni zan tafi ya fada lokacin kuma na mike tsaye nima ina fadin mungode ya tare da bin bayan shi dan dan kallona da umma tayi lokacin.
Har bakin motar shi na rakashi ta juyo a yana fuskantana a cikin karamar murya ya kira sunana yana fadin .
Kuyi hakkuri nasan abinda akai maku mm a banza daku a cikin duniyane yanzu yake maki zafi har nake ganin kamar shima ya dawo gare mune don ya cuta muna yanzu.
Banyi magana ba sai wasan da nakeyi kawai da yatsun hannuna lokacin a karshe dai ya kara da bamu hakkuri har yake fadin yanzu haka a kan case din mune yasa bai koma ba don akwai binciken da yakeyi a asirce ba tare da kowa nasa yasan yanayi ba.
So yake ya gama kafin ya fito masu da zancen a banza shine dalilin daya kira umma din har ya gane muna kaduna a lokacin.
Idona ne ya kawo kwala kafin nace dashi ai dama kabar wanan zancen inda suka aika muna mahaifi gaba dayan su can zasu tafi ai idan anje lahira Allah yai masu shari,a a can.
Don wani tone tone a yanzu sai nake ganin baida amfani tunda sin riga da sunci dukiyan ko nake gani a yanzu tunda Allah ya fitar damu daga kangin wahala da a bar zancen kawai zaifi a yanzu kada rayuka su baci don naga akwai wa yanda basa son zancen.
Shiru yayi ya dukar da kan shi kafin ya ce dani sai anjima idan kuna da wani matsala ki nemeni a waya zan taimaka maku dashi in Allah ya yarda.
Yana fadin hakan ya shiga motan ya tayar ya bar unguwar namu a hanlali na jawo kafana zuwa ciki ban zauna a falo ba don umma ma bata falon na shiga ciki.
Wanka nayi kafin na fito na hada muna abin karyawa muka karya dashi na koma daki na kwanta.
Gwago Hari ce da kanta taje airport ta dauko dan nata cikin jin dadi da nuna kulawa a gareshi sai wani haba haba takeyi dashi lokacin kamar dai karamin yaro.
Agida kuma tarbo na musan man ya sama an shirya mashi duk saboda dawowan shi wanan wahalar da kai din da sukeyine yasa baison fadawa mami din nasa dawowan shi saidai su ganshi kwatsan ya shigo garin.
Bai tsaya falon su ba kai tsaye bayan gaisawan shi dasu gwaggo Asiya dasu mommy da aka gaiyato suzo taron dan lelan kai tsaye ya shige part din shi ya barsu zaune a falon.
Wanka ya shiga duk da baida wani datti amma yana jin kansa a takure lokacin son haka yake ganin watsa ruwan zaifi mai sauki.
Bin bandakin yayi da kallo na dan lokaci kafin ya fito ya dan sauya kaya wanan karon zuwa riga da wandon yan Pakistan mai laushi har farin singleting shi na maza yana haskawa daga cikin kayan.
Yasan suna jiran shi a falo aci abinci don inda sabo ya saba da irin rayuwan mami din nasa kan yadda take nuna masa rsagwaran so zalla a gaban ko wayema zata gwada hakan.
Ya samu ma sun karu a yarda ya barsu a baya faifan Nazifa suka bude a gidan kan iskacin da tayi masu a gidan buki da sujaje.
Har gwaggo Asiya tayi mata magana bata ganesu bane halan ta zaune yadda take take fadin na ganeku mana ba su gwaggo Asiya bace bata kuma gayar dasu din ba ta kyalesu.
Wanan yasa duk ta kara fita cikon ransu shine yanzu gwaggo Asiya din ta tayar da zancen suke mayar da magana akan abinda ya faru a ranan.
Fitowan Almustaphane yasa suka dan sassauta muryoyin shi daya karade falo gaidasu ya sskeyi kafin uayi kokarin samun wuri yana kaiwa zaune.
Gwaggo Asiya tace zaka zauna kuma bakaci abinci ba dan murmushi ya sake yana fadin a koshe nake yanzu mama sai zuwa dare zanci wani abu.
The boy kayi wanan uwar tafiyan mai nisa kace ba zakaci komai ba yanzu maza muje danning ko wani dan abu ka taba a ciki.
Tashi sukayi zuwa cin abincin shikan zaune yake kawai a wurin yana kallon uban abincin da aka zuba mai cilin plate a gaban shi gashi bai iya mussa hakan.
Ya dan yi spoon uku da kyar ya dauko abin goge bakin shi yana gogewa da sauri uwar ta dago kai tana fadin boy zamuyi fada yanzun nan .
Murmushi yayi yana mikewa tsaye tare da fadin zan ci anjima mami idan na dawo yanzu ina son hutawa ne kadan ya dan rungumi uwar tashi.
Nan ya barsu zaune sukan suci abincin su sosai basin sun rasa a gidajen su ba sai don marmari da kuma haduwa da juna.
Basu bar gidan ba sai da akayi sallah la,asar kowansu ya kama gaban sbi cikin jin dadi da kasancewa da junan su a lokacin.
Daga gidanshi yaje gidan su ya dubasu ya samu mommy bata gida Nabila ke sheda mashi inda ta tafi din ranshine yaji ya baci sosai.
Ya rasa meyasa suke bata lokacin su akan wanan mara tarbiyan da gata yayiwa yawa har baisan abinda yakeyi ba bai kallon kowa da daraja yana ganin kamar yafi kowa.
Bai zauna ba yayi masu sallama suka suna masa magana yake fadin zaije ya dawo ya gansu ya fice daga gidan .
A get motan su ya hade dana mommy din dake dawowa ita da gwaggo Asiya yana gani su ya bata rai a tsatsaye ya tsaya ya gaidasu ya wuce.
Mommy ta fahinci dalilin sharesu da yayi a lokacin don haka ta danji ranta ya baci a lokacin yadda ya nuna masu din.
Ta shiga cikin gida su Nabila suke gaida da ita ta amsa tana zama tare da tambayan Nabila din yayan ku ya shigo gidan nan ko ?
Me kuka fada mashi daya shigo gidan nan mun fada mai inda kika tafi gidan gwaggo Harira wurin dawowan ya mustapha.
Dariya sosai Fa,iza ta kwashe dashi lokaci guda duk suka juya suka dubeta suna mamakin abinda takewa dariya a lokacin.
Wallahi ba komai bane sai Sahiba dana tuna ranan da mommy ta aikemu wurin gwaggo muka samu yaya a gida mun fito muna gulman shi ashe yana falo a kwance yana waya.
Ya jiku Hauwa ta tambaya yajimu mana tana surfa mai zagi da katon banza a saman jikon maman shi ya kwanta gashi da wani geme kamar sai gashi gaban mu.
Dariya suka kwashe dashi dukkan su lokaci guda me yayi mata ko bai nuna yajiku ba ai kin san halin Sahiba mana anty karasa tayi duk da yana jinta kuwa.
Wanan yatinyar ai yar iskace ta kwarai Allah yaga abinda ya gani ya barta a cikin tsiya da suke ciki yar iska kawai.
Wallahi ni yarinyar bana son zancen ta kodan ta faye zama fayau ne duk inda kaje da ita sai ansan da tana wurin zakaji wai mutane fa sai su dinga tambayan ka diyar waye ita din shiyasa ban son fita da ita wallahi.
Wani kallo Faiza ke mata daga inda take zaune kafin tace kai kai mutum ya dinga aibanta dan uwan shi haka don kawai tafiki tsari.
Waye tafi tsari din Nabila ta tambaya har tana dagowa don bacin rai tana fadin mommy wallahi kiwa yarinyar nan magana kona fafasa mata baki yanzu a wurin nan.
Kaji min yar iska ni ta ina Sahiba yar kabilu waccema ba a san asalinsu ba sun zo su danganta da uban wasu har zaki wanice dani tafini.
Sahiba din ce bata da asali uwar ta dago kai tana tambayanta a cikin mamaki sai ta bata rai kafin tace mommy to waya san ubanta din.
Ni mommy ta fada rai bace duk suka kallo inda take a cikin mamaki taci gaba da fadin na karaji kin dangata yar nan da mugun suna zan bata maki rai a gidan nan wallahi.
Wai mommy dama kin san mahaifin su ashe shine Anty Nabila take fadin wai basu da asali kila daddy suke kokarin lakawa ita yasa aka koresu.
Salati mommy ta fara yi tana tafa hannayen ta a wuri daya kafin tace yanzu sherin da kuke kokarin kulawa mahaifin ku ke nan akan yaran nan dama ?
Da sauri Nabila tace a, a mommy nima ji nayi ana fada wallahi cikin dangi yasa nazo ranan ina fada masu abinda naji din amma bani na kawo zancen ba.
Kasa magana tayi a lokacin din bata san me zata fada ba ga yaran nata sai mikewa tayi ta shiga dakin nata ta barsu a wurin zaune.
Nabila ta kalli faiza cikin dan kwantar da murya ta kada mommy tajisu tana fadin na fi karfin sahiba kema kin sani duk kika kara hadani da yar matsiyata din nan mai kama da yar wanke wanke wallahi saina balbala ki a gidan nan ranan don ta dan sayo maku gwajon lagos ta aiko maku kike wani rawan jiki akansu haka.
Nayi shirina ranan monday na fita wurin aiki tunda na tsayar da motana udanuwa suka dawo akaina na mutanen dake ma,aikatan .
Sam ban damu da irin kallon da suke min ba don inda sabo a yanzu na saba hakan a wurin su.
Ban yarda na shiga office din da muka saba zama don yin aikin muba aranan don haka na zaro wayana na fada masu zamuyi aikin yau a cikin office din babban accounter din ma aikatane.
Don haka nasan a nan zan samesu na fito yadda na saba ina saye da wandon jeans na yayi sai yar riga fara mai dan ado daga gaban riga daya tsaya min iya gwiwana kaina yana saye da hula baki kalan wandon dake jikina zakace tare akayi su.
Na wuce naji wasu na fadin kai ga mace dai kan har mace amma kuma kafira bata sallah ina wayana na wuce su ina mamakin dan adam da daukarwa kanshi fitina yake.
A daidai shiga na hadu da oga bala da sauri zai fito yana waya yana ganina yadan razana ya daburce don gani din da yayi a bazata.
Gaisawa ya tsaya mukayi dashi sama sama kafin don ban tsaya ba ina tafiya muka gaisa din da dan murmushi gefe a fuskana na wuce zuwa ciki.
Suna zaune ina tsaye ina karanto masu abinda nayi nazari a file din farko dana bude tare da bayanin abubuwan da na gano a cikin sa.
Kafin na dauko computer na daga inda nake tsaye din ina tura bayanan da muka gani acikin sa aka turo kofan office din.
Oga bala ne tare da manager suka shigo a dan rude duk muka dago muna kallon su a cikin mamaki kallo daya nayi masu na mayar da hankalina wurin computer da nake tura sako ciki.
Bayani yakeyi a rude yana fadin sunzo don Allah akwai wani files a ciki da basu dabganci wanan zaman naku ba zamu dubasu cikin nan.
Ba tare dana fago kaiba na fadi a cikin yarbanci su basu su duba din naci gaba da aikin da nakeyi ban dago kaina ba.
Ban dago kai ba still ganin suna damuna nace dasu wanan kuke nema ku dauka ai mun gama dashi zaku iya tafiya dashi yanzu.
Lokaci daya suka dago kai suna kallona kafin su juya su kalli junan su kuma suna mamakin hakan.
Manager ne dan fara ja baya kafin ya juya ya fita daga office din oga bala yabi bayan shi ba tare da sun tsaya amsan file din ba don sun san komai yagama tonuwa a cikin shi ke nan.
Kallon su nayi ina fadin zamu shiga kano gobe idan Allah ya kaimu da safe Adnan zamu tafiya da motar kane dana Abdul zuwa can don haka ku sha mai da wuri da zaikaimu ya dawo damu a yau din nan.
Sai mun hadu goben na fada daga haka na fita don ban iya tsayawa hira a rayuwana har yanzu sabo da rayuwan ujula dana tashi a cikin sa har banda lokacin da zan tsaya yin dogon hira da mutane.
Basai mun tambaya ba don da ganin wurin hankali a tashe yake nikan ban tsaya ba wurin motana na hara direct na bude zan shiga.
Da sauri Bello ya karaso inda nake ya tsayar dani yana fadin wallahi madam akwai matsala don suna son su hada kan mutanem wajem nan ai muna bore a koremu.
Nothing will happen insha Allah na fada na bode motana na aje kayan dake hannuna tare da juyowa gareshi ina masa godiya.
Na shiga na tayar da motar na halba aguje nabar haraban wajen suma suka shiga muka fice zuwa inda masaukin mu yake.
Haka yasa suka dawo da hankalin su wurina har na bace kowa na fadin albarkacin bakin shi a kan mu yarinya yar firit kara sai bakin wayau da fitinan tsiya haka.
Wasu suce da ganin wanan yar ta karantu sosai tayi ilimi tun tana karama irin tashin turai din nam ne kana ganin ta kasan ba tashin kasan nan bane ita.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ANA DARA GA , , , , , , , ,
6️⃣0️⃣BY, , , , , , , , , , , ,
ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , , , , , ,
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AL WADU,D, , , , , , , , , ,
ONLINE PAID NOVEL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA BA TARE DA HAKKIN KOWA BA DON BIYA KI TURA DARI BIYAR 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK 08036959257
ALLAH SARKI AI RAINA BAYA BACI YANZU DON KIN FITAR DON NASAN AKWAI RANAN HADUWA SEE U👋👋👋👋
Zaune suke sun kura mai ido sai harkan gaban shi yakeyi kamar baisan dasu a wurin ba zaune ga lokacin da suka bata a waje kafin su samu shigowa wurin shi falon.
Saida ya gaji daja masu rai suna zaune shiru don zakace ba wani mahaluki bayan shi a falon.
Gyaran murya yayi ya dago yana fadin kai yanzu manaja har akwai wani hallita da zaizo garin nan ya tayar maka da hankali irin haka ?
Kuma kace mace ce yar karama ke maku wanan karanbanin barazanan da rayuwan ku yaya akai sake kabari har haka ya faru dakai kamar ba namiji ba ?
Zama manaja ya gyara ya dan shafo fuskan shi kafin yace wallahi Alh yarinyar