Showing 327001 words to 330000 words out of 382072 words
gefe daya a cikin damu suna kallon abindake wakana a wurin har kowa ya manta da suna wajen ma lokacin.
Maganganun su mama kudidi yasa jin zuciyana ya dan sassauta min a lokacin har na dago ina kokatin sauka daga gadon inda nake kwance.
Kowa ya bini da ido ana kallon kome zanyi a lokacin gyalena dake saman gado na dauka na yafa kafin na taka zuwa inda kafan baffah hamza yake na tsunguna tare da fadin uncle ka yafe min insha Allahu zan yi maku biyayya kamar yadda al,adan ku yake na gida.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ANA DARA GA , , , , , , , ,
9️⃣9️⃣BY, , , , , , , , , , , ,
ZAINAB IDRIS MAKAWA, , , , , , , , , , ,
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM MALIK AL MULK , , , , , , , , , , ,
ONLINE PAID NOVEL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA BA TARE DA HAKKIN KOWA BA DON BIYA KI TURA DARI BIYAR 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK 08036959257
ALLAH SARKI AI RAINA BAYA BACI YANZU DON KIN FITAR DON NASAN AKWAI RANAN HADUWA SEE U U👋👋
Ba yadda na iya don abu biyu zuwa uku na farko yin biyayya gun uwata sai nabiyu zanyi biyayya gun magabatana kamar yadda umma tace dani haka al,adasu yake gada na yarda na karya ga hakan sai kuma don ita mahaifiyar shi mukhatar din da sukace ta roki hakan kada in nuna bata isa ba a gareni.
Gashi abu kadan zakaji tana faman yabon mahaifin mu ta mashi adduan samun rahama a wurin ubangiji duk muka hadu da fatan muyi koyi da irin halin mahaifin namu.
Nima zan nuna mata yace kamar kowa zan nuna masu na gado mahaifin namu a wani fanni na rayuwa saidai kwakwalata da zuciyana ta kasa daina shi mukhatar din a wurin yaya nake ke nan ?
Na gyara kwanciya badon naji dadin shi ba lokacin ina tuna irin alkawarin dana gama daukarwa iyayyena a yanzu suna saka min albarka.
Akan wanan auren shina tuna na lumshe idona cikin takaici da kunan zuci ban taba kawowa kaina wani laluran aure ba a yanzu kusa.
Asalima ban taba kallon wani da namiji naji ina son shi ba da sunan aure amma sai gashi kaddara ta a yanzu tazo min da abinda ban shirya mashi ba a lokacin.
Hawayene masu zafi n
aji suna bin fuskana a lokaci guda daidai lokacin da wayana sako ya shigo min ke nan ban yi yunkurin dubawa don yanayina daba dadi a lokacin.
Jin sako na biyu ya kara shigowa lokaci guda yasa na dan juya ina kallon wayan nawa sunan ya Abubakar nagani rubuce ya turo min sakon.
Nakai hannu na dauki wayan na bude gaisuwane tare ban hakkuri yana tausan zuciya na yarda da kaddara duk yadda yazo mi n shine cikan musulmi mutum na gari a wurin ubangiji yana da tabbacin mukhatar zai rikeni amana da mutunci kuma kada in yarda a samu matsala a bangarene har ya daukeni mara tarbiya.
Baki na dan mere don jin kalamin shi na karshe don kaman yasan na shirya yiwa wanan mutumin daya biyo ta baya don kawai ya hadani fada da iyayyena a yanzu.
Don haka na shirya rashin zaman lafiya ko kwanciyan hankali a bangarene da wanan mutumin da ya wuce sa,an aurena a yadda na dauka.
Idan ma aurene sir Sha,aban nake iya aure a yanzu koda yin hakan ya taso min a yanzu idan banda zancen Alaja da ya bata min rai da dukkan su a yanzu.
A rayuwa naki jinin kai min gori kan abin hannun ka ko wani abu daya shafi dai ka nuna abinka yasa nake tare dakai shiyasa ban shiga mutane don nasan mu ba masu shi bane sosai don haka daga aiki sai gida saiko wani wuri na musanman.
Idan nace nayi barci a ranan karyane don haka ko da asuba da zasu tafi sallah ban bisu ba ganin haka itama fatima tace su tafi kawai ba zata tafi ba.
Faiza da tafito ban daki ta samu fatima kwance take tambaya sai cewa tayi bazanje nabar anty sahiba a cikin wanan halin ba haka ku tafi kawai.
Ita kuma sai tace a,a ku dai tafi nina zauna da ita zaifi zaman kike tace ba zan iya wuce na barku ba gaskiya gara dai mu zauba din dukkan mu a nan hankalina zaifi kwanciya.
Duk sai sukaki fita karshe sai mama kudidine ta shigo tana fadin mufa ake jira a waje sukace su tafi kawai yau ba zamu tafi ba.
Duk abinda sukeyi ina jin su amma ko motsawa alaman najisu banyi ba har mama ta fita daga dakin suma suka koma suka kwanta suna jiran lokacin sallah suyi a daki.
Felix ne ya kira Sir Shaaban yana fada mashi abinda dake faruwa zaune yake tare da mahaifiyar shi da duk kwanakin suna dan sama sama da junan sune da shi da ita.
Nan ya fara maimaita Sahiba fa kace tayi aure a madina yace kwarai Abdulne yake fadawa oga jimoh jiya da dare.
Kuma ya turo mai photunan daurin auren a yau ya gani shike nan yanzu shike nan abinda ya fara fada lokaci guda.
Wanda ba wani abu bane illa dabian su na yarbawa daya tsaya mashi a rai kuma ya rikeshi a gaskiya.
Cewan da malamin shi yayi mai arzikin mu yana hade dashi idan muna tare zaiga arzikin shi yana bunkasa zaiga komai yasa a gaba zai sameshi a saukake zai zama mai albarka.
Da farko bai dauki hakan gaskiya ba sai zuwan mu kaduna yin wanan aikin da kuma irin cigaban da yaga yana samu a yan shekarun nan .
Sai ya dauki wanan zancen da gaskiya ya rikeshi a rai saidai bai taba fadawa kowa wanan zancen ba har ranan da ya samu labarin barina aiki dasu a lokacin hankalinshi ya fara tashi yazo kuma ya samu wai bana kasan tun lokacin hankalin shi ya fara tashi.
Yanzu kuma ga felix yazo mai da wanan zancen yasan na salwanta daga gareshi ke nan na fita hannun shi haka yasa yana kashe wayan ya mike ya bar abincin dake gaban shi.
Alaja da tadan fara saukowa ta bishi da kallo don ganin yadda lokaci daya ya shiga cikin rudani kuma gashi ya ambaci sunana a wayan.
A lokacin ta dan mere bakin ta tana gyara zama sai kuma taga ya mike rai bace yabar falon Aisha ce tace dashi a, a brother why are you living now ?
Tana fadi tana kallon abincin daya tashi ya bari a wurin ga mamakinta ko juyowa baiyi ba a lokacin balle tasa ran samun amsa a wurin shi dukko da hakan ba halin shi bane.
Sai hakan bai kwanta mata a raiba mikewa tayi tabi bayan shi har dakin kwanan shi zaune ta hangoshi a bakin gado ya dukar da kai kasa kamar yana tunane mai zurfi hankalishi a tashe.
Takowa tayi har zuwa bakin gadon ta samu wuri ta zauna a kusa dashi na tsawon dan lokaci kafin ta dauki hannunta ta dora a nasa tana fadin .
Meke faruwane dakaine haka brother ta tambaya tana kallon fuskan shi hannun nata ya dan rike da karfi kafin ya dago kai yana kallonta da idanuwan shi da suka rine sukai ja don tashin hankali.
Da sauri tace subbanallahi brother tell me please what is going on ko sahiba din ce ta kara jefa mai tambaya cikin tambaya.
Murmushin dole ya dan kakaro a fuskanshi kafin yace sahiba ta tafi ta tafi daga gareni yanzu har abada Alaja taji dadi yanzu shike nan Aisha .
Nasan daba don wanan matsalan nata da Alaja ba ba abinda zaisa sahiba aure a yanzu at dis time tayi surprise din mutane haka lokaci guda.
Wai da gaske kakeyi miss Sahiba tayi aure at dis time da kafi kowa bukatan ta tare dakai kuma tayi ma hakan lokaci guda ?
Idanuwan shi ya runtse yana fadin you can live now bana bukatan dogon magana a yanzu zata kara magana yace please Aisha live me alone.
Jin hakan yasa ta mike tsam ta bar mashi dakin ko kallon Alaja dake zaune saman kujera mai zaman mutum ukku ta mimike tana waya tazo ta wuce ta.
A zuwa lokacin yar nata laifin ta tagani don gani take itace taja komai a lokacin har hakan ya faru da dan uwanta ya rasani.
Bin bayan yar tayi don tasan hakan sukan hade mata kai idan ta taba mutum dayan su sai dayan shima ya nuna bacin ranshi ga hakan shiyasa bata son wani matsala irin haka a tsakanin su.
Bata san meyasa ba Sun kasa fahintar gata take son masu ko yaushe akan me zata yarda ya auro mata yar tallakawa a zuri,an ta.
Sam bata yarda da hankalinta ta rabi talauci talakka banda wahala meke cikin hada halaka dashi banda tsiya don ko yayane dole dashi zasuti amfani su tofo suma.
Da ace yarinyar dan wani hamshakine ko mahaifinta baida mukami zata iya yarda danta ya auri yarinyar don sahiba ba inda take da matsala banda na rashin background.
Gwaggo harice zaune gefen daddy ranta a bace daddy din yai shiru yana kallon ta kafin ya furta kai yaran nan sun girma amma basu san sun girma ba su.
Yanzu kema din ga irin abinda suka aikatawa jinan su na bace bace kina son ki aikata hakan a gabana da alama goyon bayan danki kike son nuna min don dole akwai abinda yasa modibbo ya fada mai hakan shima.
Dama nasan haka zaka fada a karshe ba zaka dauki maganan da muhinmanci ba ai amma dama ai sai kuma tayi shiru.
Kallonta yadan yi kafin ya mayar da jikinshi saman kujera ya dan shafo goshin shi yana murzawa kafin ya mika hannu ya dauki waya.
Danshi ya kira yace a takaice kazo yanzu kome kakeyi ka barshi kazo yanzun nan daga bangaren modibbo din yake tambaya lafiya dai daddy ?
Lafiya ke nan kazo yanzun nan da sauri ya mike don cika umurnin mahaifin nasa cikin yan mintuna ya isa gidan saidai tun daga nisa ya hango motan gwaggo hari a waje alaman tana gidan itama a lokacin.
Tambayan kanshi yayi meke faruwa hakane wai ko a kan zancen auren sahiba din ne sukaji hankalinsu suma ya tashi da hakan.
Da sallama ya turo kofan falon ya kai kallon shi ga iyayyen nasa biyu dake zaune a lokacin yanayin su ya kalla ya gano ba lafiya a wani bangare.
Daddy lafiya ya fada tunkan ya zauna samu wuri ka zauna ya fada yana nuna mashi da hannun shi ya kalli wurin yakai zaune a hankali ya kara maimaita tambayan shi wanan karon gun gwaggon nasa.
Dake zaune tana cika tana batsewa don yadda take jin kanta lokacin jin tambayan daya jefo mata yasa ta dan harareshi tana fadin.
Kaji mun mara kunya sakon daka bayar ne ya sameni yasa nazo gun mahaufin ka tunda nika rainani a yanzu har zaka iya fadawa boy wanan maganan ido da ido.
A, a gwaggo Allah ya baki hakkuri amma shi mustapha din ai ya fada maki dalilin fadin hakan danayi ko ?
Me zai fada min bayan wanda kake ganin yanzun wuyan ka yayi kauri kai ka isa zagin mu a yanzu akan Sahiban banza wace , , , ,
A, a hari me kuma ya kawo zacen sahiba a yanzu nan don Allah ku bar yarinyar nan da abinda ya isheta daddy ya fada rai bace.
Kafin ya juya wurin dan nasa yana fadin kai meya hadaka da dan uwanka har yakai ga batanci ga iyayyen ku ?
Shiru modibbo din ya danyi kafin yace wai fa daddy samuna yayi har gidana dacin mutunci aai akan zancen aure sahiba nine duk na kullashi.
Nan dai ya kwashe yadda sukayi tiryan tiryan ya labarta masu saiga gwaggo hari tayi shiru kafin tace shi boy din ya fada ma hakan ?
Gqaggo zan maku karyane naci riban me a hakan idan na fadi ba daidai ba daddy ya kalleta yace kinji ke ku dinga bincike kafin ku auwatar da abu don Allah.
Yanzu waya fara zagi a nan daga zancen baki kawai kuma ya koma ya fada maki kekin hau haka ni ai na dauka duk daya suke a wajen ki ashe ba haka zancen yake ba.
Wallahi yaya rainane ya baci idona ya rufe wai ace modibbone ya fadi hakan garemu ashe shidin mara kunya ya fara fada bai nuna ba.
Ba zai nuna ba yanzu dai kun girma kusan ya kamata ku kun fadi hakan kamar yara me wasu zasu fada kuji zafin sa ?
Kai daya fadama meyasa ka biye masa kuka kai ga hakan wanan ai fada mata ko yarane su aka sansu dashi haka baku maza haka magidanta ba.
Ayi hakkuri munyi kuskure gwaggo kuyi hakkuri don Allah ranmune ya baci har muka kai ga hakan ya fada yana dukar da kanshi kasa cikin ladabi.
Toh yanzu dai in zaku daina ku daina don mu ba tabbata zamuyi tare daku ba a nan in kun rike zumuncin kun kyautawa diyan ku nan gaba idan kuma kunci gaba da hakan kundaiga yadda abubuwa suke a yanzu.
Bayan fitan shi gwaggo hari ta shiga wurin mommy sun dan jima a tare suna tatauna wanan matsalan na diyan su kafin danta ya isheta da kira ta bar gidan.
Kwana biyu cur bamu fita dan gara su sun dan fita zuwa wurin sayayya ni dai kan ko kofa ban leka ba ina dakin kwance sai faman tunane dake cin zuciyana.
Ba komai bane ya tsaya min a raina lokacin sai yadda rayuwana a yanzu zai kasance min da kuma yadda zan barsu umma na tafi wani uwar duniya da sunan aure kai ina nace a raina.
A daidai lokacin da akai nockig din kofan tare da turo kofan lokaci guda jin hakan baisa na dago don ganin mai nocking din kofan da zai shigo ba.
Wani kamshin ne ya daki hancina lokaci guda wanda yasani dago kai ina kallon kofan shine a tsaye kaina ya zuba min idanu kamar ranan ya fara ganina na farko.
Da sauri na lalubi hijabin da nayi sallah dake gefena na rufa a saman dan rigan dake jikina dogo ya matse min jiki har zaka iya ganin suran jikina a fili.
Wani dan guntun murmushi ya sake wanda har ina iya jiyoshi a lokacin Sahiba meke damun ki haka kinbi kin sukurkuce kamar ba Sahiban mommy ba dana sani mai kwazo.
Ko duk a kan cikan alkawarin ubangiji akan mu yasa kike kokarin nuna butunlcewan ki a hakan ?
Wani kallo na jefamai mekama da tsana do your wish kayi amfani da daman da kake zaton kana dashi a yanzu a kaina.
Kada kayi tsamanin a yanzu kayi nasara ke nan ko ka dauka wanan damane da zakayi amfani dashi a kan mu kan wani manufa naka don ka cin ma nasaran abinda kake nufi.
Hannaye ya ware kafin yace Allah ne kadai shedana banda wani manufa ko daya akan family din mutumin da yayi silan zamana wani abu rayuwa na.
Bani da komai a kanku sai alheri fatana mu rayuwa tare mu kara kafa kan mu a karkashin innuwa daya daku haka kawai zan maku nasan na taimakawa kaina daku farin ciki yakai ga mahaifin ku.
Stop dat jork kana tsamanin ban san abinda kake kokarin yi bane a kan mu din sai yayi murmushi yana gyara tsayin shi yace idan ma har kin yaudari kanki a hankan zato zunubine .
Allah yaga manufata a kan ku yanzu kuma kada zuciyarki ya yaudari wani ko zato akan shi Allah ya gani ban nuna kudi ko karfin iko akan kowa ba naki illa zallah gaskiya danazo masu dashi kuma suka gamsu da hakan gareni.
Don haka ina rokon ki da ki cire komai a zuciyar ki yanzu ki natsu ki fahinci waye mukhatar a wajen ki da mahaifin ki .
Ranan da naga natsuwa zan sanar dake koni waye nan gaba na barki lafiya dama nazo naga fuskan kyakkyawan amaryatane nakuma yi maki sannu da jiki duk da nasan ba abinda ke damun ki sai fargaban gamayya dani a yanzu.
Karkiji komai ni nidin mutum ne mai saukin kai da sanin ya kamata ga duk wanda ke karkashin innuwa na a zaune har sai idan maishi ya fito da nasa manufan a kaina muke raba hanya dashi .
Saidai ki sani ni da sahiba auren mu na mutu ka rabane insha Allahu da sannu zaki fahinci koni waye nan gaba.
Ki kula da kanki don Allah kada wani abu yazo nan gaba yafaru dake please take care yaran ki sunce a gaida ke idan na ganki.
Yara na dago kai ina sake kallon shi da mamaki yaranshi fa ke nan yana da mata kila ma mata don hausawa irin wanan a yanzu ba zancen mata guda a