Showing 159001 words to 162000 words out of 557259 words

Chapter 54 - πƒπ”ππˆπ˜ATA BOOK1 AND 2 HAUSA NOVEL

HUGUMA   

03 Nov 2025

574

Hularsa tana hannun me sunan malam dake tsaye daga gefe bayan ya karbi news paper din daya kammala dubawa. Ameh ya sallama daya biyoshi da tray din teen da zaitun da kuma jan inibi da bai zauna yaci ba,ya juya yana duban me sunan malam

"Ka shiryamin zama da shugaban gidan jaridu a gobe.....don yau din zamuje abuja.....but zuwa yammaci zamu juyo"

"Okay sir" Me sunan malam ya furta,sai fu'ad din ya sanya hannu ya karbi hular ya juya yana nufar qofa,abinda ya sanya duka guards dinsa tsaiwa don sunsan inda zashi,mutum biyun daya saba tafiya dasu sukabi bayansa.

Dab da zai fice a gate din farko yaji tana qwala kiran sunansa da shagwabar na tata

"Hamma......hamma na". Tun kafin ya waiwayo murmushi ya subuce masa duk da bai shiryawa hakan ba. Yasan zaisha qorafi saboda haduwa da tayi wahala a tsakaninsu a kwanan nan.

Barin hali inji hausawa sai mutuwa,tana isowa taja tunga kuwa tana tura baki gaba

"Hamma.....kace kada na yarda da abinda BB farouq ya fada......kuma ni Allah alamun nake gani". Wani lafiyayyen murmushi da ba kasafai ake katarin ganinsa saman fuskarsa ba ya saki yana juya fuskarsa dama da hagu kafin ya tsaida dubansa saman fuskarta.

"Amneeen hamma amneen anni......zaki yarda magauta su rabamu?" Kai ta girgiza da sauri tana sake fuskarta qasan ranta kuma tana fata inama saddiq yana kusa yaji yadda hamma yake ji da ita.

"Kwana biyun nan school ya saki gaba.....nima duka aikace aikace sun tasomin......ko bakison mu bude company n jewelry sample din farko da zamu fara fiddawa ya zama naki......kinsan sunan da zamu bawa brand din?" Kai ta sake girgizawa cikin tsananin jin dadi

"To sai kin kawo cin hanci zan gaya miki" Yayi maganar yana juyawa tare da ci gaba da tafiya.

Da hanzari ta tattaka ta cimmasa sukaci gaba da tafiya tare

"Please hammana.....ka gayamin cin hancin me kakeso?,kome kakeso hamma zan bayar"

"No....ki canka da kanki kawai ki bada din sai na gaya miki" Shuru tayi tana zurfafa nazarinta na abinda ya dace ta bashin,dab da zasu fice a gidan tace masa

"Yauwa.....hamma........zanyi maka mata ka huta da gorin yaa farouq akan kaqi nemo mata......na baka friend dita nasreen...." Dan rage speed na tafiyanshi yayi ya waiwayo yana jefa mata harara da fararen idanunsa.

Ya yarda autanci da kuma quruciya suna damun amna din da gasken gaske,da alama fa da gaske take,don daga yadda tayi masa maganar tana zumudi tare da jij ta masa bajinta kadai zai gaya maka iya gaskiyarta kenan.

"Wannan ba cin hanci bane......saidai ma ki jawo komawa ta biyu da za'a bawa product din" Hannu ta sanya tana rufe bakinta gami da zaro ido. Sai yanzu ta gane tayi wautar,ta tuna sunanshi da farouq ke gaya masa,ta kuma tuna shi lamarin yin budurwa ko zancan aure abune da bata taba gani ya zauna ya bashi muhimmanci ba.

Kunnenta ta kama daidai sanda suke isa qofar gidan wanda sam bata ma kula da gidan da suke nufa din ba saboda yadda hankalinta ya dauku

"Am sorry hamma.....please,wallahi idan ka fasa yaa saddiq zaiyimin dariya".

"Ki canza wani abun.......but this" Sai ya girgiza mata kai yana maida dubansa ga muhallin malam Sa'adu wanda bai ganshi wajen ba da alama ko ya zaga ne.

Tun daga shigowarsu gidan har takowarsu farfajiyar gidan idanunta yana bisa kansu. A yadda tasan hali da dabi'arsa ya akayi yarinyar ta samu sakewarsa har irin haka?,anya abinda take tunani kowanne dare kuwa bazai afku ba?.


*D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

PAGE 86


Ita kuwa ta yaya zata bari wani abu ya hada zuri'arta data hajiya amina?. Muddin da rai da ruhi da kuma numfashi a gangar jikinta.... Koda zata rasa komai data mallaka.......koda shine abu na qarshe da zata aiwatar cikin rayuwarta ba zata taba bari wannan tunanin ya wanzu a kwanyar kowa bama bare akai ga haifar tunanin a zahiri.

Labulenta ta saki zuciyarta na mata wani irin suya. Kwanaki biyu kenan suna sanyata yin asarar komai data shirya domin su. Yaune cikar kwanakin da bokan ya diba mata,muddin a yau ma nasara ta qwace mata to lallai zancan bokan ya tabbata na cewa aikin aiki ne......muddin a yau bata samu yadda takeso ba batajin gobe warhaka zata kasance a bigiren da take tsaye akai a yanzu......dole ta tafi plan B da zafi zafinta kuwa.

"Zuwaira.......maza leqa ki gaya masa ya qaraso ciki amma shi kadai......bana ko qaunar kallon fuskar yarinyar ballantana gangar jikinta ya shigomin cikin gida".

Sosai zuwaira taji nauyin aiken saboda ba qaramin kwarjini fu'ad din yakeyi mata ba,amma ba zata iya musa umarnin uwar dakin nata ba.

Da bismillah a bakinsa yake shirin sanya qafarsa a step na farko da zai sadaka da qofar falon zuwaira ta fito. Kai ya daga ya kalleta a nutse ganin kamar an jehota,sai tayi qas da kanta cikin tsananin qanqan da kai ba tare data iya hada ido dashi ba tace

"Maamah tace ka qaraso ciki.....amma so samu tanason ganawa da kaine kai kadai". A nutse ya waiwaya ya dubi amna,suka hada ido sai ya zare idonsa daga kanta,ya miqa mata hularsa yana cewa

"Riqemin yanzu zan fito" Bata musa ba ta sanya hannu ta karba,ta koma daga gefe ta zauna kawai jikinta a sanyaye,don inda ya barta gida zata koma,sai yanzu ta tuna gidan waye ta biyoshi?. Matar da totally ita tsoro take bata tun ranar data shigo gidansu ta kuma ga abinda tayi musu.

Bai fasa duka addu'anshi ba kafin ya sanya qafarsa cikin matuqar kula da takatsantsan. Tana zaune saman sofa qafarta daya saman daya tana kadata a hankali. Ciki ciki ta amsa masa sallamar ba tare data masa wani dogon kallo ba. Ya qarasa ya tsugunna cikin girmamawa yana fadin

"Barka da safiya.....kin tashi lpy?"

"Koma ka zauna muhammadu" Ta furta kai tsaye wanda baice komai ba ya miqe din ya koma ya zauna sosai.

"Wacece mahaifiyarka ne muhammadu?" Tayi masa tambayar da wani sauti dake cike da izza da kuma bacin rai. Kanshi ya daga ya kalleta suka hada idanu,ta tsareshi da ido sosai da kuma tarin abubuwa daya gansu kwance cikin idanun nata.

"Kece" Ya amsa mata a gajarce.

"To amma banga alama ba.......banga alamar hakan ba......yanzu ace samuwar farincikina daga gareku sai ya gagara?,yanzu ace samun kulawa da danuwarku a kaina sai ya zamemin aiki?" Ta jefa masa tambayar da ba abinda tayi tasiri a kai sai tuna masa da baya da tayi. Ta tuna masa sanda suke da tsananin buqatarta a daidai wannan lokacin ta tattara hankalinta zuwa ga wani waje daban. Ya tuna tun shekarunsa basu kai ya koyi wasu abubuwa masu yawa harda ma wadanda sukafi qarfinsa saboda rashin samun kulawarta. Ya tuna yadda yake kasa yiwa mahaifinsa dake jiyya abubuwa da yawa saboda bashi da qarfin da zai iya dagashi zuwa toilet da sauransu,saidai su zauna shi kuka shima kuka. Sau tari maganganunta da lafuzzanta sunfi masa kama da na mutanen da idonsu ya rufe......mutanen da buqatar gabansu kawai suka sanya a gaba,mutanen da ba ruwansu da damuwar kowa sai tasu......mutanen da ba wani burbushi na nadama a tare dasu ballantana dana sani.

"Kiya haquri" Ya jefeta da kalmar da yakejin iya ita kadai kawai zai iya furta mata don bashi da wani sauran abun fada.

Sake zube masa idanunta tayi tana sake jaddada zallar miskilanci da taurin fu'ad din. Ba wani alamun sarewa ko saukowa a tare dashi?,tamkar ma an sanya fetur da ashana an qone dukkan wata qauna ta mahaifiya dake zuciyar kowanne d'a. Anya ba zancan hajja harira bane akan hanya da take hasashen hadda farraqu hajiya ameena ta sanya akayi musu?.

"Zanje abuja yau din.....nace bari na sanar miki,sai mun dawo" Ya furta bawai don yana sanya ran zata masa addu'a ko wani abu daya dace ba,don yana kaiwa qarshe ya miqe yana gyara hannun rigarsa.

Dan runtse idonta kadan tayi tana hasashen yau dinma kenan babu nasara?. Da qyar ta iya controlling kanta da fadin

"Sai ka dawo" Duk kuwa da tarin tambayoyin da takeson masa akan me zaije yi abuja?,yaushe zai dawo?.

Binsa tayi da kallo har ya fice daga falon,taja wani mataccen numfashi idanunta na qanqancewa saboda bacin rai.....dole suje plan B bata kuma fatan su isa plan C don zaifi kowanne mataki wahala a gareta dasu gaba daya

"Yaro baisan wuta ba sai ya taka.......yaro man kaza......idan kasan wata bakasan wata ba" Dukka ta furta a sarari tana daukan wayarta gami da kiran hajja harira.

Cikin wani iri ya dawo cikin gidan. Saidai yayi qoqarin daidaita yanayinsa lokacin daya isa parlor din anni.

Can babban dining area din dake parlor din ya samesu saman dining. Anni abba da farouq suna breakfast,yaja kujera kusa da anni ya zauna yana gaida abba da basu samu haduwa ba sai sannan.

"Abba.....nace ya kamata ace tare muka fara hawa jet dinnan". Dan murmushi ya saki yana ciro tissue cikin tissue box.

"Nikam wannan jumaar a kibiya zanyita me babban suna......indai muna da rai ai za'a yita hawa ko don zuwa ibada qasa me tsarki.......yanzu kam ku wuce sabgar gabanku.....saidai kads ku manta da addu'a,Allah yasa a shiga a sa'a,ya kauda dukka abunqi"

"Allah yasa a fara hawa cikin sa'a,ubangiji yasa rai aka yiwa" Anni itama ta furta tana murmushi. Har qasan ranta tana jin dadi gami da jin alfaharin kasancewarta uwar goyo a gareshi. Koda muhammad bai kasance me dukiya da arziqi kaman haka ba.....shi din abun alfahari ne ga dukka uwa me hankali......yana da wasu nagartattu kuma kebantattun halaye na daban da ba kowanne dan adam yake samun baiwar mallakarsu ba.

Da dukka zuciya da idanu ta takawa hasken idaniyar tata har zuwa sashen da kowannensu zai hau mota tana rakasu da addu'o'i na neman kariyar ubangiji da kuma tsarinsa. Abban yau sunyi kibiya shi da musaddiq,wanda dama kusan kowanne qarshen wata ko sati idan ya samu chance acan yake sallar juma'arshi,hakanan yakan tafi musu da tarin alkhairai daga arziqin da Allah ya wadatashi dashi bayan wasu daga cikin 'yan uwan da suke zaune a gidan. Wannan din wata dabi'a tasa ce dake qara masa farinjini da soyayya wajen al'ummar garin,domin kuwa alkhairinsa ba wai iya ga 'yan uwansa kadai ya tsaya ba......ya kewaye kowa da kowa.

A saman idanunta dukka motocinsu suka tashi,sai gidan ya rage daga ma'aikata sai ita sai musaddiq.......sai mutanen dake can boys quarter da ba kasafai suke iya jiyo motsin abinda ke faruwa cikin ainihin gidan ba ko kuma su aji nasu.

Idanunsa lumshe cikin jirgin,sanda yake lulawa dasu sararin subhana daga abujar birnin tarayya zuwa kanon dabo. Abujan da duka duka awa biyar sukayi cikinta suka fito. Acan sukayi sallar jumaa cikin centra mosque abuja,daga nan suka wuce unguwarsu fanna.

Rashin sabo da wannan sabgar ya sanya mintuna talatin kawai yayi gidan ya cewa farouq zan dan kama masauki na wucin gadi da yafi kusa da airport.......zai tura masa location din sai ya sameshi a can su wuce.

Shigarsa masaukin yayi arba da abinda ya sake tsuke tunaninsa ya kuma sake dora masa mamaki me azabar nauyi......ya shiga daidai sanda mashkur ne gangarowa daga sama riqe da wayarsa a mugun gigice yana cigiyar hotonta daya buda cikin wayarsa. Hoton da yakebin duk wanda ya gani da tambayar

"Don Allah kaga wannan?,yanzun nan ta sauko daga dakina fa.......ta yasheni ta kwashemin komai daga accounts dina guda biyun". Da irin wannan bayanan ya tareshi sanda yake yunqurin kiran elevator ya haura dashi zuwa sama bayan yabar guards dinsa guda cikin reception din.

Duba daya tak ya yiwa hoton ya dauke idanunsa a hankali ya maida fuskar mashkur da tayi wani irin hautsinewa.....da alana ta zare masa kudi masu yawan da tsaf zai iya taba rayuwarshi. Wacce irin hatsabibiyar yarinya ce wannan?,fu'ad ya yiwa Kansa da kansa tambaya sanda elevator din ya qaraso ya bude ya soma shiga. Har a sannan yana jin muryar mashkur dake bulayin neman wanda ya ganta.

Lumshe idanunsa yayi yana jin wani mummunan bacin rai yana saukar masa. Yana buqatar qarin information a kanta abinda ya raya kenan a ransa,ya fiddo wayarsa yana neman Jordan,sukayi maganganun da zasuyi,dab da zai ajiye wayar kuma kiran abdus_samad ya shigo masa.

Dukkan wasu bayanai ya karanto masa akan rufai ahmad mu'azzam.

"Caca" Shine alaqar data hadasu da mikail?,ta yaya zai zama mutumin banza yana zaune kudinsa ya tafi ta qazantacciyar hanya irin caca?.

"Thanks for your effort" Ya amsa masa yana gintse kiran. Still yana shiga dakin daya kama din kiran saddiq ya shigo masa

"Hamma......mikail keta neman haduwa dakai......" Idonsa yadan lumshe kadan kana ya bude kaman yadda ya saba a duk sanda ranshi ya baci yake kuma qoqarin hadiyewa

"Ya samawa kansa mafita.....koda bai kawo kanshi ba tabbas zan sanya a kawomin shi.......bani da time na ganinsa yanzu......sai zuwa Monday......ka tuntubi Easter kan investigation da na saka suyi cikin company"

"Itama tayi dropping min massage.....tace in sha Allah zuwa Monday din komai zai kammala"

"Alright" Ya amsa a taqaice kanshi yana sake shiga rudani.

Wannan din shine abinda ya zurfafa tunaninsa cikin jirgin,har sai da farouq ya magantu

"Wani abu ya sake faruwa ne?" Idanunshin da suka sauya launi ya bude a hankali sannan ya girgiza kai

"Nothing.....kawai dai kaman akwai abubuwan da nake ganin ba haka ya kamata su tafi ba.....but everything will be fine". Kai farouq ya kada masa yana dubansa da kyau

"Whenever you need assistance........kada ka manta farouq na side dinka.....am ready to be a good partner". Dan qaramin murmushi ya sakar masa yana gyada kai

"Na sani tuntuni".

Tun kafin sabreen tayi nisa da gida ta zura hijabinta zuwa gurin daya gaya mata ta duba zaya ajjiye mata sabuwar waya torch. Yadda ya kwatanta matan haka ta sameta a wajen,ta dauketa cike da murnar zataji muryar da tayi kewa qwarai ta wuce zuwa gida.

Murmushi ya saki bayan informers dinsa dake wajen ba dare ba rana sun shaida masa abinda ya faru

"Yadda zaki bare sabuwar wayar nan yarinya haka zan bareki nan da kwanaki uku kacal masu zuwa" Yayi maganar cikin shauqi da wassafa ta yadda a ranar zaici karensa babu babbaka,ya dauki tiyo dake maqale da bututun tukunyar shisha ya zuqi hayaqin har cikinsa ya fesar,sannan ya kalli matashin dake gefansa.

"Aikinka na yau tunda ta dauki wayar zai fara da tura mata zazzafan saqo da zai nuna asalin kewa da shiga rudani da rashin jin muryarta"

"An gama oga" Ya fada yana bude wayar ya fara abinda aka umarceshi,shine kuma kwangilar daya dauko takanas zai yiwa naseer din.

Jikinta har rawa yake sanda ta kunna wayar saqon ya shigo. Tana gama karantawa taji idanunta sun cika da qwalla,tausayinsa ya cikata.

"Allah sarki bassam.....bazan sake yarda adda sabreen tayi silar yin nesa dani ba" Tayi maganar yana yunqurin kiransa saiga nasa kiran ya shigo.

A yadda ya marabceta a yau din sai da zuciyarta tayi narkewa da qwalla ta fita.

"Tun daga ranar bani da lafiya huda.....fargabata na mutu ba tare dana cika muradan zuciyarmu ba....baqincikina kuma sai na jima a kushewata qilan kafin labarin mutuwata ya riskeki....."

"Allah ya kiyaye.....in sha Allah ba zaka mutu ba" Ta fada muryarta tana rawa tana tuna yadda ta rasa abbanta da umminta,yanzu kuma sai ace shi?.

"Ganinki ne kawai zai sanya na warke huda.....ki taimkeni muddin kinaso na farfado naci gaba da rayuwa kizo na ganki"

"Bansan gidanku ba.....bansan inda zan ganka ba"

"Indai zakizo din huda zan tura miki da adress....ki taimakeni kizo......amma karki takura kanki daga nan har zuwa litinin,har sai kin gamsu da kanki na cancanci kizo din na ganki.....".

Ko kusa ko alama bata ji saukar damuwa saman zuciyarta akan mashur ba,wanda ta tabbatar ta masa gagarumar barnar da zaiyi wahala ya maida gurbinta.

Wani tabbataccen labari data samu a daren jiya akan mashkur shi daya ya qara mata qwarin gwiwa da jin cewa ya cancanci ta rabashi da komai da yake sanya shi jin xai iya shiga ko bata rayuwar dukka diya macen da yaso a sanda yaso.

Da confidence dinta take takowa zuwa cikin gidan nasu. Kamar ko yaushe bata damu d kallon me kallo ba......bata damu da hasashen me hasashe ba......hakanan bata damu da zunden me zunde ba,ta keta

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login