Showing 303001 words to 306000 words out of 557259 words
da wuturi_
_Sannan akwai hidisi me zaman kansa abdullahi bin umar ya rawaito,manzan Allah S A W yace ALLAH KA YIWA BAYAN DAKE SALLAH RAKA'A HUDU KAFIN SALLAR LA'ASAR RAHAMA_
*_IBADA DUK IBADA CE,AMMA MAFI SOYUWAR AIKI A WAJEN ALLAH DUK QANQANTARSA SHINE WANDA ZAKA DAWWAMA KANA YI,SAIKA DAUKI WANDA KASAN ZAKA IYA DOREWA_*
Tana kallonsa ta cikin madubin yana ci gaba da kusanto inda take,saidai gaba daya ta kasa motsa koda yatsanta ne ballantana tayi tunanin abu na gaba daya kamata ace ta aiwatar.
Shu'umin murmushinsa da kallon da yake dubanta dashi duka ba wanda ya fasa,yaci gaba da kusantota kowacce gaba ta jikinsa tana jin wani shauqi tare da dokanta ta sadar da kanshi gareta. Irin yadda ya fitinu da ita ba abu bane me sauqin fassarawa ba......sai kuma gashi a bagas zaice ko a banza wata hanya ta samun isa gareta ta riskeshi cikin sauqi,wanda zai iya kiran hakan da qatotuwar sa'a cikin rayuwarsa.
"Mashkur!" Ta fusgi sunan da hanzari ta kirashi a tsawace bayan ta maimaita la'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimeen har batasan adadi ba.
Tsaiwar da yayi ita ta bata damar waiwayowa da wani irin hanzari kamar wadda aka fusga. Idanu ta zuba masa kaman yadda shima idanun ya zuba mata yake kallonta da dukka iyakacin kallonsa.
"Me ya kawoka gidan mutane?......har dakin matar aure?" Ta fadi da wata irin birkitacciyar murya data cika da razani da tsoro.
Wata irin dariya ya qyaqyace da ita,harda komawa ya fada saman gadon nata,sannan ya tashi ya miqe yana fuskantarta. Ya bude baki zaiyi magana a hankali sautin saukar ruwan saman farko ya baqunci kunnensu,shatin ruwan ya fara sauka ta glass din windown dakin sai ya saki murmushi yana dawo da dubansa kanta.
"Kin gani ko?,.....ko Allah ma yana sona......ko Allah ma yasan kin cuceni....kuma ko Allah yasan kedin azzaluma ce,wannan zubar ruwan shi zai sake toshe kunnen duk wani da kike tunanin zai ceceki ko zai kawo miki dauki,duk da kuwa wannan ginin gidan naku dama kaman anyishi ne domin ni,yana riqe sirrin kowanne motsi yadda ya kamata". Ya fada yana kallon yanayin roofing na dakin yana sakin murmushi.
"Nayi mamaki wai da kike tambayata abinda ya kawoni,bayan akwai basussuka na da yawa a kanki?".
"Mashkur ka haukacene?,kasan gidan waye ka shigo?,gidan matar aure har tsakiyar dakin aurenta..... " Fara takowa yayi yana sake nufota yana dariya
"Ina cikin gidan muhammad fu'ad jadda,the owner of jadda diamondchore resources.......sannan ke din sabreena ce,mata a wajensa.....bayanin yayi daidai?" Ya jefa mata tambayar yana dage mata dukka girarsa biyun bayan ya tsaya daga takowar da yakeyi.
"Ko kina buqatar wani qarin bayanin?......kinaso ne na gaya miki da license dina na shigo gidan nan?,da license daga hannun wata mace mafi kusanci da me gidan?". Daukan tunaninta yayi ya luluqa wajen lalubar ma'anar abinda yake fada,da license daga hannun wata mace mafi kusa da me gidan?,wace kenan?.
Kaman yasan abinda take tunani a kai yace
"No dear......kada ki wahal da kanki wajen tunanin wace..... Ki bari na gama kashe qishirwata sosai sannan mu zauna mu tattauna..... I need you.....na azabtu da yadda asara biyu ta fadamin......babu ke ba kudina......come please" Ya furta yana kawo mata cafka.
Batasan tana da tsananin zafin nama har haka ba sai data kufce masa ya kama iska. Sukabi hannunsa da kallo dukka su biyun shi da ita. Shi dariya ya saki yana jijjiga kai
"Kada ki dauka kedin me sa'a ce ko da yaushe.......idan a wancan karon kin kubcemin...... Na rantse wannan karon baki isa ki kubuta ba,koda kuwa a gaban mijinki ne a yau sai na kashe qishirwar dake raina" Ya furta yana daga rigarsa,take ta hangi hancin bindiga daga aljihun trouser dinsa. Kaman an debo bulo an jibga mata haka taji wani matsanancin tashin hankali ya keto mata,bata gama sauke abinda ya taso mata ba ta ganshi ya taso mata yayo kanta gadan gadan. Wani irin qarfi ne yazo mata,ta tattara hijabin jikinta da batakai ga cireshi ba da kyau ta haura sofa bed din dake gabanta ta wuce tsakiyar gadon
"Ka fita min a gida.... Ka fita tun ban tada security din gidan nan ba" Ta fada tana duban sashen da wayar girke take a dakin wadda zata baka daman kiran kowanne sashe na gidan. Ta shiga shock sosai sanda ta lura ya gutsire wayar gaba daya ya fasa kan,duka yaushe yayi hakan da ko alama bataji ba.
Dariya ya saki yana cewa
"Kinga abinda ya samu telephone din ko?....." Bata bari ya qarasa ba ta tattara dukkanin qarfinta ta kwarara ihu tana fadin
"Wani ya taimakeni" Abinda ta dinga maimaitawa kenan har sai da taji maqoshinta yana wani suya da radadi. Dakatawa tayi hawaye suna cika idanunta,tana duban mashkur dake qyaqyata dariya.
"Zan iya qara miki lokaci kici gaba da ihu......kiyita ihu har iya yadda kikeso".
"Fuad!. ....fuad!!!!" Ta sake qwalawa kiran sunansa. Karo na farko da ta fara ambatar sunan nasa kenan.
"Yana can yana bacci" Ya fada yana juyi kaman zai taka rawa
"Na sakashi bacci,kuma bazai tashi yanzu ba,sai na gama hutawa da matarsa" Ya sake maimaitawa cikin yanayin nishadin da kana kallonsa zakayi imani yakai masa har qasan zuciyarsa nishadin da yake ciki.
"Mashkur,........ka saurara haka,ya kamata kasan kuskure kake tafkawa ba qarami ba.......ketawa matar aure haddi mashkur?!" Ta furta a tsawace. Dariyar nishadi ya saki yana kallonta,ya kama button din rigarsa ta saman ya fara ballewa yana zareta ya yar.
"Kada kiyi kaman bakisan komai ba.......kina tunanin yaune na farko dana fara kwanciya da matan aure?,na kwanta dasu har bansan adadi ba......kawai ke dince ta daban,kin kasa fita a raina......bazan miki qarya ba,koda na dandana yadda kike banajin zan iya ci gaba da rayuwa ba tare da ke ba......shawara daya kawai zan baki,kada kiyimin gaddama.......ki bani kawai salin alin don na tabbatar kinsan komai,ba wani abu baqo a wajenki"
Sasai kalamansa sukayi mata nauyi a qirji,ta tabbatar inda za'a tsaga jikinta ba za'a taras da jini ko digo ba saboda tsananin tsoro da fargici. Ranta yakai maqurar baci sanda taga yana yunqurin haurowa gadon
"Har ka mutu mashkur ba zaka taba samun komai daga gareni ba.... Ko gawata tafi qarfinka mashkur bare gangar jikina a sanda numfashi yake busawa".
"Well.....tunda kin zabi muje ta haka dake!" Da furucin da haurowarsa saman gadon duka lokaci guda suka faru. Wani tsalle tayi da zummar barin gadon,saidai kuma ya samu nasarar take qasan hijabinta da qafarsa ganin zata kufce masa,abinda ya sanyata data dira din bata sauka a daidai ba,hannunta ya daki side bed ya bada wani irin qum.
Qara ta saki cikin tsananin azaba......azabar da bata hanata ci gaba da qoqarin qwatar kanta ba,cikin sa'a santsin bedsheets din dana hijabinta suka sanyashi ya zame zaman lallausar katifar,saita miqe itama,amma ta kuma zamewa take fuskarta ta bugi gefan bedside din still.
Bata damu da radadin daya sake ratsata ba.....sake miqewa tayi tana harin qofa,abinda ya lura dashi kenan shima ya miqe da azama,tana isa qofar shima yana qarasawa sanda take kici kicin bude key din,ta finciketa ya watsar ya saka key ya kulle qofar. A zafafe yabar bakin qofar yana nufar qofar toilet yana cewa.
"Yau zaki gane waye mashkur.....tunda baki zabi komai ya kasance ta hanyar maslaha ba" Key din jikin qofar toilet din shima ya murza ya kulle,tana kallonsa sanda take qoqarin sake tashi saboda buguwar da tayi a hannu da fuska,yadan bude window din waje ya watsa Keys din sannan ya sake waiwayota.
"Kaji tsoron Allah mashkur......kada ka keta haddin aure.......da auren wani a kaina.......ba bazawara ko budurwa bace!"
"Allah yasa tattabara ce ke" Ya fada cikin rashin damuwa yana durfafota da sassarfa kaman me wasan motsa jiki.
Cafka ya sake kawo.mata ta sake samun nasarar gocewa abinda ya sake qona masa rai,sai kawai ya zabi ya galabaitar da ita.....don duka alamu sun nuna masa cewa gwana ce wajen iya zilliya,kada ta bata masa time ta kuma bata masa plan,don haka yakai mata naushi.
Ya sameta ta kafadarta ne yayin da nashi hannun ya wuce ya daki bango,abinda ya sanya wata azaba me tsanani ratsa kwanyarsa.
"Ouch!" Ya fada cikin tsananin jin zafi,yayin da zuciyarsa ta sake tunzura
"Ni xaki sanya naji rauni?". Yana kaiwa nan ya shammaceta yakai mata qafa ya kwasheta,take ta fadi ta bugu da qasa.
"Wayyo Allah na" Ta fada cikin tsananin radadi tana riqe qugunta gami da runtse idanunta. Wannan shine abinda ya bashi daman isowa gareta,ya kama bayan kanta inda ta tattare gashinta tayi gammo dashi ya riqe gam. Wata azaba ta ziyarci tsakiyar kanta zuwa qwaqwalwarta,ba shiri ta sake qwalla qarar da zuwa yanzu ta yanke tsammani akwai me cetonta.
Yana riqe da kan nata ya turata har saman dressing table dinta,baiyi wata wata ba ya buga goshinta samanshi,take goshin nata ya fashe,saidai kuma tana dagowa ta dago da bedside lamp da akayi ado da ita saman mirror din ta kwatsa mata ita tsakiyar kanta,abinda ya sanyashi sakinta ba shiri yana dafe da wajen.
Duk da wajen bai shafe ba amma take yayi wani malulu azaba ta shiga ratsashi tako ina.
Ya kalleta sanda jini ya fara diga jikin sky blue din hijabinta yana jin wani fushi mara misali yana saukar masa. Bai taba tunanin zaiyi minti biyar ba daga sanda ya shigo dakin ba tare daya samu galaba a kanta ba,sai gashi yanzu wankin hula yana neman kaishi dare...
π π π π π π π π
_Zafafabiyar_
ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2
β±§Ιβ²Ιβ₯β³
ππΌππ 57
57
_Daga abu hurairah RA yace,manzon Allah S A W yace "mafi falalar sallah bayan sallar farilla itace sallar dare_
*_ga falala ga kaifi,biyan buqata kaman yankan wuqaπ,Allah ya bada ikon jurewa_*
Ga mamakinta sai taga ya samu waje ya zauna yana mulmula wajen. Tsahon mintuna tana tsaye tana kallonsa tana dafe da inda jinin keci gaba da diga bata da abun tareshi. Ko na minti guda taqi yarda ta dauke kallonsa a kanta gudun kada ya mamayeta bata shirya ba. Hannun nasa ya sauke,ya fidda kwalin wiwi,ya zari guda biyu ya kunna musu ashana sannan ya sanya duka biyun a bakinsa ya soma zuqa cikin gwanancewa. Yadda ya tsara zaiyi da ita sai yaji me yasa bai taho da kayan mayensa ba?,ko banza yafi samun kalan nishadin da yakeso?,ya yanke ya fara zama yasha wiwi dinne don yadan huce kadan ta yadda zaifijin gardin abun.
Tunda ya kunna wiwi din hankalinta yayi mummunan tashi. Ta san tabbas zata shiga wani mummunan yanayi ne da idan batayi wasa ba xai galabaitar da ita. Asthma dinta,ba kalar hayaqin dake saurin tayar da ita irin hayaqin wiwi taba da shisha. Matsawa baya ta dinga yi tana duban yadda hayaqin ya fara gauraye dakin,yana canxa yanayinsa daga ainihin qamshi xuwa gurbataccen warinta maras dadin shaqa.
Dukka hijabin ta cukuikuyeshi tana rufe hancinta dashi,a hankali tana jin yanayinta yana son ya fara sauyawa.
"Zaki fahimci abinda ake nufi yau da asalin fyade" Kamar mugun dawa haka ya miqe zumbur ya kuma nufota,ta juya itama da nata hanzarin da nufin barin gurin,saidai tuni ya miqa hannu ya danqo hijabinta ya dawo da ita gabansa tana fuskantarsa. Yadda take qoqarin toshe hancinta a nasa tunanin ya karanci batason warin wiwin ne,don haka ya zuqeta sosai ya kuma soma fesa mata ita saman fuskarta. Kauda kanta tayi sosai tana dauke numfashin da zuwa sannan tana jin kamar ya fara daina isarta
"Ba wannan hijabin ba?" Ya fada yan yamutsa hijabin cikin hannunsa,abinda ya sanya ta takurewa gaba daya guri guda tana qoqarin neman hanyar da zata samu iska me kyau gudun gushewar hankalinta,wanda wannan na daya daga cikin damar da zai samu cikakkiya kan ya aikata komai hankalinsa kwance.
Wata wawiyar zuqa ya yiwa wiwi din ya sake fesa mata kan fuska,sannan ta birkitota gaba daya yana kici kicin fincike hijabin daga jikin ta.
Dole ta daga fuskarta,duk da yamutsewar hazon dakin dole ta bude kafofin shan iskarta ta fara masa magana a rarrabe
"Kada ka ketamin haddi na,kada ka lalatamin mutuncina" Tayi.maganar sanda ya samu nasarar salube kan hijabin daga kanta. Bayyanar sassalkar sumarta ya sanyashi sake gigicewa,bai taba tunanin ta mallaki suma har haka ba.
"Wow" Ya fada yana qoqarin samun wuyan hijabin don itace hanya mafi sauqi da zata bashi damar tsarge hijabin cikin sauqi daga jikinta. Ta fahimci abinda yake shirin yi,saita tattara dukka dan qarfinta ta cukuikuyeshi da kyau tana kiran sunansa cikin qaraji gami da fadin
"Kada ka aikata!.....ka qyaleni mashkurrrr!!!!".
A hankali ya bude idanunsa wadanda basu sauka akan komai ba sai agogon dake gefan gadon nashi. Idanu ya zuba mishi kafin ya miqa hannu a hankali yana jawoshi yana duba time da weather na gari. A nan yaga alamun saukar ruwan sama,sai ya maidashi sannan a hankali ya furta addu'a yayin saukar ruwan sama
'ALLAHUMMA SAYYIBAN NAFI'AN'.
A nutse ya tashi daga kwanciyar,ya motsa kadan yana sauke qafafunsa daga qasan gadon wanda suka sauka daidai bedroom slippers dinsa yana jin yadda gaba daya ciwon kan da yakeji din ya sauka. A yanzun tsabar ta'ammali da home remedies ya sanya ba kasafai ya fiya afawa kansa qwayoyin bature ba yayin zazzabi da ciwon kai ba.
Miqewa yayi ya fara takawa zuwa qofa yana mamakin yawan baccin da yayi,yadan shafi cikinsa yana jin yadda yunwa ta fara yamutsa hanjinsa,don haka ya yanke shawarar ya sauka qasa kawai yaci abinci,yadan duba ayyukansa koda na awa biyu ne kafin ya sake kwanciya.
A parlor ya tsaya ya duba wayarsa,ya samu tarin miscal amma ciki na farouq yafi yawa,ya samu saqonsa da yake masa mita akan bai bada komai na tafiyarsu ba bayan saura sati guda. Qasan zuciyarsa kawai yayi murmushi yana sauka daga duba saqonnin. Har ya aje wayar wani tunani ya fado masa,sai ya tsaya ya zubawa qofa idanu.
Yana tuna tahowarta ne jiya daga bedroom dinta zuwa qofan falo. Tabbas idan idanunsa ba qarya sukayi masa ba kallo yaga tanayi.
"A ina ta samu waya?,waye ya bata waya?" Ya yiwa kansa tambayar a bayyane yana zurfafa nazarin ta inda zata samu waya tana cikin gida.
Kaman yadda ya sanya doka ya sani ba wanda ke shiga gidan,sai amna da tazo baifi sau biyu ba. Amna kuwa yayi imanin ba zata taba bata waya ba musamman idan ta gaya mata shi ya karbe. Duk abinda yayi ko ya aikata amna tasan yana da dalili,ta fita saninsa,so ba zata karya dokarsa ba.
Kai ya jinjina yana tuna fitar da tayi ba tare da sani ko izininsa ba rannan,tabbas wayar tana da alaqa da wannan fitar duk da ya bincika babu wani abu da yayi kama da gurin wani taje.....amma how and when ta samu waya?.
Tambayar data masa susa kenan a qirji. Yanaji kaman ya kamata ya maida hankali a saka CCTV din. Company din yazo har sau biyu shi yace su bari ya zama free ya kirasu,yana jin kamar gamsuwa daya fara bawa kansa don tana karatun addini sosai a yanzu ta hannun jikar malam.....kaman bai kamata ya bata amanna har haka ba.
Da wannan tunanin ya bude smart door dinsa,ya kuma fara sauka zuwa qasa.
Abinda ya soma bashi mamaki shine jin gaurayar wani qamshi qamshi me kama da wari wari da gauraye stairs din. Koda ya kawo qarshenta sai yaji warin yana dada qarfi,ya tsaya cak yana buda hancinsa sosai,a nan yaji daga inda warin yafi qarfi.
Mamaki ya kamashi sosai,yana da wani irin experience na iya hasashen abu da gano sauyawar motsi ko yanayi kaman wanda ya karanci aikin binciken tsaro na sirri. Fara takawa yayi zuwa cikin hallway din a hankali,yana sake shiga ciki xarginsa kuma na sake qarfafa saboda daduwar warin da sai a sannan ya fahimci warin wiwi ne.
"Wiwi?" Ta maimaita sunanta can qasan maqoshinsa sanda ya iso bakin qofar dakin.
Tsaiwar da yayi duka baifi ta minti guda ba,amma sai yaji jikinsa bai aminta da dakin ba,baya buqatar yayi knocking don ba qa'idar bincike bace akan abinda kakeson ganin gaskiyarsa quru quru,juyawa yayi da sassarfa yana tuna inda yaga an tanada a dakin nasa saboda ajiye kowanne key na kowacce qofa ta gidan a matsayinsa na mamallakin Master bedroom.
Dubawa daya ya hango master key,sai ya daukoshi yana juyawa gami da saukowa kai tsaye yana nufar hallway din.
Ta riqe ya riqr,yaja taja,har