Showing 435001 words to 438000 words out of 557259 words

Chapter 146 - πƒπ”ππˆπ˜ATA BOOK1 AND 2 HAUSA NOVEL

HUGUMA   

03 Nov 2025

555

ya riga ya saba mata,wata kasala take fama da ita,bata iya cikakken zama ba'a jikinsa.

Tunda jirginsu ya tashi take jin gabanta yana faduwa lokaci lokaci,tadan rufe idanunta kadan tana jan sunan Allah,ko shima sabuwar faduwar gaban tana cikin laulayin ta yiwa kanta da kanta tambaya.

Idonta ta rufe tana fatan bacci yayi awon gaba da ita wai ko zata samu sassaucin abinda takeji,tana iya jin sanda ya sanya blanket ya lullubeta,sannan ya sake rufeta da faffadan qirjinsa yana rufeta tsam cikin jikinsa,ajiyar zuciya me sanyi ta subuce masa ya dora habarsa saman kanta a tausashe.

Cikin zuciyarta take roqon Allah......kada ya bata ikon butulcewa wannan bawa ko juya masa baya.......ita kanta wani lokaci irin yadda yayi nisa a soyayyarta tana jin kamar tata zuciyar zata narke a kansa. Tsakanin ita dashi batasan waye yafi wani yin nisa ba,waye yafi wani yin zurfi bs,fatanta kawai shine kada su zama masu butulcewa juna a tsakaninsu.

Tafiyar awanni biyu jirginsu ya sauka a filin sauka da tashin jiragen sama na malam aminu kano dake kano. Sai takejin farinciki yana ratsata duk da ta baro wani guri mai muhimmancin gaske a rayuwar duk wani musulmi.

Abu guda daya da yaci gaba da farautarta shine faduwar gaban dake qara tsanantar mata,duk sai take jinta a rikice har zuwa sanda suka qaraso inda jerin gwanon motocin jadda diamond suke jiran qarasowarsu.

Kusan dukkanin guards dinsa sun zo tararsa cike da girmamawa da kuma kewarsa da sukayi na tsahon lokaci.

Sabule hannunsa yayi daga cikin nata,abinda ya sanyata daga kai ta kalleshi kenan.

Murmushi ya sakar mata me taushi yana dubanta.

"Zaku fara yin gaba saboda ki samu zama dasu huda kuyi sallama......zan qaraso yanzun......nasan a gajiye kike amma ma'u ta tanadar miki komai.....kada kice zaki jirani,kiyi wanka kici abinci kiyi bacci sosai......yau akwai biyan bashi" Ya furta maganan qarshen qasa qasa yadda ba wanda zaiji musu sirrinsu.

Duk da yadda gabanta ke tsananta faduwa,duk da yadda takejin kaman zaini wani wawan nisa da ita......irin nisan da takejin tazararshi tayi yawa amma saida murmushi ya subuce mata. A tausashe yayi kissing goshinta yana dubanta. Raunin da yake ganin cikin idanunta shi kansa baisan na meye ba,ya saka hannu da kansa ya bude mata qofar motar dasu huda ke jiranta,ta shiga,ya tsugunna ya tattare mata abayarta data fito waje ya maida ciki.

"Kada ka dade" Ta samu kanta da fadi masa a karye sanda yake shirin rufe mata qofar

"In sha Allah" Ya bata amsa yana jin dadin kulawa da damuwa dashi din data nuna,ya rufe qofar a tausashe sannan yaja baya ya kira abdulgafar sukayi magana,ya kira abdulbasit shima sannan ya sallamesu suka tashi motocin da zasu kaisu gida,ya rage sauran wadanda zaiyi amfani dasu ne kawai.

Ta cikin side mirror din motar tasu ta zuba masa idanu,suna sakeyin gaba yana nisa da madubin har ya bacewa ganinta,saita lumshe idonta tana sauke nannauyar ajiyar zuciya.

Tana jin karadin su huda sanda suke fita daga airport din amma ta gaza saka baki a hirarsu,kawai tana sauraren yadda zuciyarta take bugawa ne.......har zuwa sanda qarar harbin bindiga har sau biyu ya sauka a kunnenta.

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un,hasbiyallahu la'ilaha illa huwa alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azeem" Ta fada da wata irin zabura tana ware idanunta gami da miqewa ta zauna sosai faduwar gabanta yana ninkuwa.

Salatin da taja shi ya sanya kowa a motar ya dauke wuta,momma dake seat din gaba ta waiwayo da hanzari tana kallon fuskar sabreen din. Huda ce tayi qarfin halin fara tambaya

"Lafiya adda?".

" Qarar harbin bindiga huda......bakuji ba?" Ta tambayesu a rude tana raba idanunta akan fuskarsu.

"Nidai banji ba" Huda ta fada tana girgixa kai

"Naji....harbi ne,amma kamar nesa da nan" Momma ta fadi tana dubansu daga inda take

"Nima naji momma" Nadra itama ta fada tana dubansu. Kan hanya hankalinta yakai,sai taga kaman driver din nasu ya qara gudun motar fiye da yadda suka fara tafiyar,hankalinta taji yana neman dagawa sosai,sai ta kalli su momma din tanajin kaman haki yanason kamata saboda tsananin bugawar da zuciyarta takeyi.


*_Tabdijan.......meke shirin faruwa ne?,me kuke hasashe?,me karatu mu hadu gobe idan me duka ya kaimu_*

*_akwai yaqi kenan_*



*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862




𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀
_Zafafabiyar_

ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2

β±§Ι„β‚²Ι„β‚₯β‚³ 118


118



"Momma ba'a nesa harbin nan yake ba......koda a nesa dinne bawai ness can damu ba......mun baro su hamma a ciki momma.....bamusan me yake faruwa ba.....driver!" Ta ambata da qarfi kaman numfashinta yana son qwace mata.

"Yes madam" Ya fada da dan qarfi shima yadda zata iya jiyoshi.

"Mu koma mu duba boss......qarar harbi nakeji".

" Am sorry maaa.......nima naji,kuma umarni ne na boss din shi ya horemu,duk sanda mukaji abu irin wannan kada mu sake mu koma da baya......kuma ko a tsarin tsaro ma hakan ganganci ne.....kiyi haquri mu qarasa gida.....we are safe in sha Allah". Yana kaiwa qarshen maganarsa qarar wani harbin a jejjere har guda biyu ya sauka a kunnensu. Qarasa gigicewa tayi gaba daya,jikinta da muryarta gaba daya suka dauki rawa.

"Ta cikin airport dinnan ne momma.....idan safe nake hamma fu'ad fa?" Ta jefawa momma tambayar cikin rauni hawaye na gangaro mata.

Girgixa kai momma tayi wadda ke qoqarin boye nata tashin hankalin.

"Bazaiyiwu a koma ba kaman yadda kika ce.....hasalima baki da tabbacin a inda suke abun yake faruwa ko wani shiyyar ne na daban.....koda a inda suke ne ma shima bazaiso ace koma meye ya hada dake ba....." Momma take fadi cikin son lallashinta. Sam hankalinta ba'a jikinta yake ba,bata ma kama maganar momma ba saita jawo jakarta jikinta dukka yana rawa ta fiddo wayarta tana cewa.

"Gabana yanata faduwa ne momma,tabbacin akwai wani abu da ba daidai ba" Tayi maganar tana zaro wayarta da zummar kiran number fu'ad din.

Abun takacin abinda kuma ya sanya a karan farko tayi Allah wadai da halinta shine. Ba number wata number da tayi kama da tasa cikin contact dinta,sai a sannan ta tuna,waccan tafiyar da yayi ya kirata sau daya,batayi saving number nasa bama,kuma koda ta duba call log babu number a wajen.

Kuka ne ya qwace mata ganin yadda suke qara nisa da airport din ba tare da tasan halin da yake ciki ba.....don gaba daya jikinta yana gaya mata akwai gagarumar matsala.

"Ni ku saukeni......xan koma na dubashi,zan tabbatar da lafiyarsa saimu taho tare dashi" Ta fada muryarta na rawa.

"Kiyi haquri madam......aikina bazai cika ba saina kaiki gida lafiya.....aikata hakan zai zama zunubi mafi girma a wajen boss,har gwara na kaiku gida na miki alqawarin dawowa na duba miki lafiyanshi". Abdul rauf ya bata amsa shima yana jin damuwa sosai da fargabar kada wani abu me muni ya faru da ogansu.

Sam bata gane abinda momma ke fadi mata ma,ta rarumo wayar ta soma lalubar number anni ko amna. Number amna ta fara gani saita kira kawai tana fatan ta samu su daga don su suna motar gabansu. Bugu daya aka daga,anni ce ba amna ba,kai tsaye ta fara magana.

"Anni harbi akeyi cikin airport anni.....kice musu mu juya mu koma,munbar hamma a can,dukkanmu mun taho saura shi kadai". Asalin damuwa anni tana ciki,amma ta danne don kada ta kashe mata qwarin gwiwa.

"Kiyi haquri sabreena......in sha Allah yana lafiya,don bamusan me yake faruwa ba,da mutane da yawa a ciki bamusan akan meye harbin ya kasance ba....."

"Anni jikina yana bani wani abu.....anni don Allah ku barni na koma"

"Ameenatu" Anni ta kirata da asalin sunanta.

"Na'am anni".

" Kita karanta lahaula walaquwwata illa billah.......bari mu qarasa gida saimu laluba abinda ya faru kinji?". Ba yadda zata iya ci gaba da musu da annin,don haka tace mata to kawai tana sauke wayar daga kunnenta ba tare data kashe ba.

Hannu momma ta miqa ta dauki wayar suka fara magana da anni.

"Ta shiga damuwa,don Allah bahijja ki bata baki,kinga ba ita daya bace,a irin wannan yanayin bata buqatar tashin hankali".

" In sha Allah anni" Daga haka ta ajiye wayar ta kamo hannun sabreen din.

Duk wani kalar bada baki da bada haquri momma ta yiwa sabreen din,saidai kawai tana jin momma dinne bawai don ta gamsu da dukka abinda suke fada ba,tana ji a jikinta akwai wani abu maras kyau daya taba hammanta,a cikin zuciyarta da ruhinta takejin hakan.

Yadda anni taji muryarta ya sanya tayi ma abdur ra'uf magana dukansu suka wuce zuwa mansion House din alhaji hamza kibiya.

A babban parking lot na gidan motocin dukka suka tsaya. Abdulgafar ya qaraso ya bude mata side dinta,su huda da momma suka fita ta daya side din.

Da qyar ta miqe bayan ta zuro qafafunta waje,jikinta idanunta dama zuciyarta gaba daya takejin sun mata wani irin nauyi. Duba daya zakayi mata ka fahimci hankalinta baya jikinta,daga airport din zuwa gidan kuwa idanunta sun fara tasawa saboda kukan data matsawa kanta dashi. A hankali da wani irin sanyi ta zube idanunta akansu anni wadda ke tsaye ita da musaddiq da saddiq,dukkansu su biyun waya sukeyi,amna kuma da alama tanata qoqarin samun wata number ne amma kiran yaqi shiga.

"Anni na kasa samun wayarsa,a kashe take" Muryar amna kenan data sakata jin wani jiri yana niyyar kayar da ita. Baya ta koma kawai ta jingina da motar data fito a cikinta,tana jin momma sama sama tana riqe hannunta.

"Na samu Jordan" Muryar saddiq kenan daya fada da wani irin kuzari,abinda ya sanya anni da su amna duka dawowa gabansa suka tsaya.

Dif sukayi suna jiran joradan ya daga,amma harta qaraci ringing dinta ta katse bai daga ba. Idanu sabreen ta mayar ta lumshe,tana jin yadda bayan wucewar kowanne daqiqa zuciyarta ke ninka gudu kaman zata tsaga qirjinta ta fito,tana jin wata sallamawa tana ratsata,tana jin cewa da gaske wani abu ya taba mata hammanta......da gaske wani abu ya faru dashi cikin airport din,sai qafafunta suka fara rauni tana jin suna fara gazawa wajen dauke nauyinta.

A kunnenta kira na uku ya yanke ba tare da jordan ya daga ba.

"Wallahi shine.....Allah wani abun ya faru dashi.....naji a jikina fa" Ta fadi da qarfin muryar da har na nesa saida suka jiyota,wanda kafin su huda sukai ga riqeta ta sulale a wajen tana sakin wani tsumammen kuka tana jin mararta na riqewa gam.

Da wani irin sukunannen gudu anni ta qaraso,suka dagata ita da momma Hankalin annin yana tsananin tashi.

"Karkiyi mana haka sabreen......ba abinda ya faru dashi mana.....ga jordan nan an samu wayarsa dagawa ne baiyi ba". Idanunta fal da kuka wadanda zuwa yanzu sun canza launi zuwa red ta kalli anni.

" Indai da gaske lafiya qalau ne ya daga wayar yayi bayani mana?,ya daga wayar yace ba abinda ya faru mana anni?,me ya hana wayar hamma shiga bayan sanda muka fito a jirgi ma ya amsa kira?". Rudata kawai tambayayoyin sabreen sukayi gami da sage mata gwiwa,saita rasa amsar bata. Duk da haka ta rungumota jikinta tana cewa.

"Amma kamar fatan alkhairi ya kamata kiyi ko sabreen da hasashen alkhairi?"

"Na kasa anni.....zuciyata ce taketa gayamin akwai abinda ya faru dashi,ba laifi na bane......DANGANTAKAR ZUCIYA ce tsakanina dashi.....ko meye ya sameshi zuciyata zata gayamin saboda alaqar dake tsakaninmu" . Sosai anni ta lura kaman hankalinta yana neman gushewa ne,don haka ta sake riqeta da kyau tana cewa.

"Shikenan,mu shiga ciki,zan tabbatar miki lafiya qalau yake.....zan kiramiki shi kuyi magana". Tamkar raguwar ciwo ko zugi daga kasu daya cikin dari shine kawai d'an abinda furucin anni ya yiwa sabreen cikin zuciyarta. Anni da momma suka riqeta da kyau kowa cike da fargaba duba da abinda yake jikinta tattali yake buqata kaman yadda tun a madina likita ya gaya musu suka wuce da ita zuwa ainihin babban falon gidan.

Baya kadan anni ta dawo tayi magana da saddiq kan yayi duk yadda zaiyi ya samo ainihin abinda ya faru sannan ta kira musaddiq suka wuce akan yazo ya zauna yayita kiran fu'ad har sai an sameshi ya daga suyi magana ko hankalinta zai kwanta.

Kaman yadda hawaye yaqi tsaiwa a idanunta haka ma kuka yaqi dakatawa. Ruwa me sanyi sanyi anni ta saka aka kawo Mata,ta tsiyaya mata ta miqa mata tana fadin.

"Karbi kisha tukunna ko zuciyarki zatayi sanyi" Kai ta girgiza kawai fuskarta shabe shabe da hawaye,abinda yake taba zukatan su huda kenan har sai da anni ta sanya ma'u ta janyesu zuwa wani falon na daban.

"Ko nasha anni bazai iya wucewa ta wuyana ba.....inaso nasan halin da yake ciki ne kawai". A sanyaye musaddiq daya gaji da kira ana ce masa a kashe take ya dubeta,sai kawai ya ajiye wayar ya miqe tsam.yana duban anni

"Ina zuwa" Ya fada yana fita da sassarfa daga dakin. Kiransa anni takeyi saboda jikinta ya bata abinda zai aikata daga yanayin tashin nasa,amma baiko waiwayo ba bare ya dakata.

"Innalillahi wa inna ilahi raji'un" Anni ta fada tana sadda kanta qasa. Awa guda kenan amma ko daga security dinsa da guards dinsa ba wanda ya samu labarin abinda ya faru. Sun koma airport din amma tun daga tafiya me nisa ma an hana shiga gurin bare su binciki abinda ya faru.....ina yake?,wanne hali yake ciki?. Duk da sun bayyana kansu a mazaunin masu tsaron lafiyarsa amma an dakatar dasu an kuma basu haquri ance su jira,ko meye ake ciki daga baya zasuji.

Zamewa tayi sosai a nan inda tayi sallah tana kukan zuci,tana jin kamar zata hadiye zuciyarta. Batasan ta inda zata fara rayuwa ba idan wani abun ya samu Muhammad........batasan ta yadda zata iya karbar wannnan qaddarar ba.

Me yasa rayuwa zatayi mata haka ne?,me yasa rayuwa zata zo mata da irin wannan yanayin ne?,me yasa rayuwa take wasan kura da ita?,take nesantata da wadanda ta sanya rai da fata me tsanani a kansu?,take nesantata da duk mutumin da zai jibanci lamarinta?,duk mutumin data dora rayuwarta da burinta a kansa?.

A nan tayi la'asar ba tare data ko motsa ba,anni tasa aka shigo mata da abinci amma ko sha'awa baya bata ballantana tayi tunanin ci.

Xuwa qarfe biyar ta koma tamkar ruwa saman abun sallar,zuciyarta na sake yayyankewa da tsananin tsoro da tashin hankali.

Biyar da mintuna anni ta sake shigowa. Duba daya zaka mata itama kasan hankalinta ba'a kwance yake ba. Musaddiq da saddiq da baisan fitarsa ba har yanzu bai dawo ba,hakanan tasa wayar still tana kashe shima tunda ya fita yabar gidan.

A sanyaye ta qaraso gabanta tana qoqarin tattaro dukka dauriyarta waje daya,ta zauna a qasa daidai saitin qafarta tana kallonta.

"Tashi ameenatu" Anni ta fadi cikin jarumta. Kaman ba zata iya tashi ba ta daddafa ta tashi. Amanta uku ba wanda ya sani,abinda ta dauka tayi adabo dashi tunda ta samu kulawa a madeena sai gashi tashin hankali ya sanya ya dawo. A cikin aman nan guda uku ba kalar azabar da 'yan hanjinta basu gani ba,don babu komai a cikin nata.

"Kinyi imani da Allah da ranar lahira?" Kai sabreen ta gyada mata hawaye na fara taruwan mata.

"Kinyi imani da Allah shine me rayawa shine me kashewa?,shike bada kariyarsa akan kowanne abun halitta?". Kai ta sake gyada mata hawayen data riqe suna sauko mata.



*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862


𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀
_Zafafabiyar_

ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2

β±§Ι„β‚²Ι„β‚₯β‚³

π™‹π˜Όπ™‚π™€ 119


119


" To inaso ki yarda da Allah ki kama ambatonsa....kibar masa kuma lamarinsa.....karki dauki haqqin abinda ke kwance a mararki ta hanyar hana kanki abinci.....don cin abincinki ko rashin cin ba abinda zai canza saima cutar da yaronki,ki samu wani abu ko ba yawa ki sakawa cikin naki". Hawaye sosai take tana kada kai.

"Ba hanya anni.....bana jin abinci xai samu hanyar wuce kwata kwata".

"To ai akwai abu me ruwa ruwa a ciki,ki duba ko yaya kisha" Ta fada tana buda kwanukan gabanta.

Lafiyayyen kunun gyada ne da

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login