Showing 495001 words to 498000 words out of 557259 words
sauke ajiyar zuciya tana fadin
"Alhamdulillah alhamdulillah.....please hamma"
"Bani hug daya kawai ya isa tukucin yi miki albishir......tausar dare kuma itace tukucin kaiki wajenta"
"Zanyi hamma zanyi wallahi" Ta fada tana dan qaramin tsalle. Riqeta yayi da kyau yana duban tsakiyar idanunta,da wata muryarsa can qasan maqoshi yace.
"Bi a hankali.....yarana" Ya qarasa fada yana dora hannunsa saman cikinta. Kunya ta kamata,ta kuma sanyata janye idanunta da sauri,daidai sanda kira ya shigo masa.
Bai fasa sakata a jikinsa ya matseta ba sannan ya amsa wayar da cp ne ya.kirashi.
"Thank you.....gani nan fitowa" Sai ya katse wayar yana dubanta.
"Zanga baqi my world.....zan dawo shortly in sha Allah....ki kulamin da kanki" Ya fada yana kissing kuncinta duka biyun ya juya yana fita farfajiyar gidan.
Daki ne yalwatacce da aka shimfideshi da lallausan carpet milk color kaman kalan labulayen dakin.
Daga damansa bibo ce ita da zuwaira,sake maida dubansa yayi ga gabansa,mashkur ne shi da dan uwan tasa ta'asar.....mashkur din da gaba daya ya fita a hayyacinsa,tsufa sosai ya kamashi,wani irin tsufa na qarfi da yaji wanda wawulonsa ya sake tsananta munin abun.
Sauran duka ya bisu da kallo,amma kowannensu munin fuskar mashkur ta zarta munin da yake gani a fuskokinsu,bawai muni na fuska kawai ba.....aaah muni na zuciya.
Ma'aikatan gidan jaridar ya fara nunawa.
"Wadannan na gama da case dinsu......aje a hadasu da diyar ambassador......ranar shiga kotu a hadosu tare qarqashin shari'a guda daya,lawyer na zaiji da komai".
"Wayyo Allah.....mun shiga uku,don Allah sir kayi mana afuwa ka yafe mana,wallahi bamusan a kanka tace a buga labarin nan ba". Wani banzan kallo yayi masa.
" Okay,idan wanine bani ba kenan zaku iya tozarta masa iyali,idan wani ne bani ba kenan zaku iya wulaqantashi ku wulaqanta aurensa da shaidar zur.....CP.....bana son sake jin muryarsa a nan wajen" Ya fada yana takawa ya jawo wata kujera.
Kiiiii ya ajiyeta gaban bibo wadda jikinta ketsa tsuma,ya koma ya zauna sosai yana dora qafarsa daya kan daya.
"Nutsu sosai.....labari zan baki sannan na sallameki".
"To....to Allah yayi albarka".
" Ameenatu ahmad sabreen takai budurcinta gidan mijinta,wanda ni Muhammed fuad jadda na karbeshi da kaina....kuma mutanen dake rayuwa damu suka shaida hakan a lokacin". Dif wuta ta daukewa bibo duk yadda takeji da tsageranci sai taji maganar ta girmeta.
"Ke din uwace ko?,a kamatance bai dace na gaya miki haka ba ko?,saidai kash.....nidin bana yafiya bana kuma ragayya ga duk wanda yace zai taba rayuwar duniyata.....sabreen,a inda kuma aka samu akasi shine.....tuntuni kika sanya qafa kika take wannan girman daya kamata ki samu......to ina me!miki albishir.....sabreen takai bantenta......ba wani matsiyaci ko lusarin daya samu damar tsallake wannan shingen......yadda kika dinga yada jita jitan mutuniyar banza ce......na baki dama na biyu kisan yadda zaki wanke wannan sunan daga kanta....ki maida gurbinsa da kyakkyawar shaida,idan hakan bata kasance ba kuwa,a karo na biyu idan na daukoki batar dake zanyi bat.....a bude mata ta tafi gida". Bata tsaya tunani ko waiwayen tazarar nisar tafiyar da zatayi a qasa,ba tare da abun hawa ko kudin mota ba ta fice,tunda har ta samu nasarar shaqar iskar 'yanci kuwa......bataga abinda zai hanata hada lecture din wayar da kan al'ummarta kan muhimmancin mutuncin da sabreen ke dashi ba.
Idanunsa ya ware akan mutum uku.....mutum ukun da yakejin laifinsu yafi na kowa girma,ya sake aza idanunsa akan zuwaira wadda daga ita har bibo sunyi wani zuzzurmawa. Duk da ajiya ce kawai akayi musu irin ajiyar da take daidai da aljannar kare.
"Kamata yayi kema a hadaki da wadancan.....sashen manyan laifuka ko?..." Kuka ta fashe dashi tana hurwa tana neman agajinsa.
"Ki rufen baki,don duk yadda raina yakai ga baci bazan iya zabgawa fuskar dakeda furfura mari ba,koda furfurar ta banza ce" Gum ta koma tayi sannna ya bude idonsa yana sake dubanta.
"Kina gidana kina qarqashin inuwata amma kina neman hanyar da zaa shigo a keta haddin iyalina?!.....abu guda ya rage miki ki gayamin......waye ya sanyaki boyesu a dakinki kika fiddosu da dare zuwa sassan matata!!!". Wata bahaguwar tsawa daya sauke mata sai data tattara gudawa me yawa a cikin mashkur,ya rasa wanne.ibtila'i da bala'i ne yake hanashi furta masa sunan.matar kowa ma ya huta?,fatansa daya wannan tsohuwar ta kira sunanta,wataqila ko kwatance da ka yayi akan shima ita ta dauki.nauyinsa duk da akwai nasa shirin.
"Mmm.......maamah ce" Sunan ya saukar masa cikin ba zata. Fuska ya yamutsa yana dubanta.
"Wacce kenan?"
"Hajiya maamah.....mariya mahaifiyarka" Komai ya tsaya masa na wasu daqiqu,sai daya koma daidai kuma kwanyarsa ta cika da wasi wasi.
"Cp.....janye matar nan,a hadata da wadancan mutanen". Kallo daya ya yiwa mummunar fuskar mashkur,wadda ta jima da tashi daga kyakkyawa zuwa asalin mummuna.
"Mariya ce nima!.....maamah ake ce mata" Ya fada da sarqaqqiyar muryarsa da bata fita yanzu tartar saboda fitar haqora sha biyar daga bakinsa.
Kaman ya dauki takobi ya jefeshi dashi haka yaji,duk wani jini dake jikinsa yaji yana neman daskarewa,kwanyarsa kuma tana shirin yi masa formatting da karan kanta irin na kota kwana,saidai kiran wayarsa yaso maida komai muhallinsa,ya daga kiran bawai don yana gane waye ke kiran nasa ba yana komawa kaman wani shashasha.
"Jordan ne sir.......sir an jona musu na'urar fidda bayanai cikin sauqi,sun kuma yi bayanin komai...."
"Me aka samu?" Ya tambaya cikin sarewa da jin komai.
"Am sir.....kayi haquri.....gaskiya bayanansu na qarshe kaman na'urar ta samu matsala.....sunce zaa sake bincikawa"
"Jordan please tell me.....ka gayamin ko waye ya sanyasu.....bana buqatar jinkiri a daidai wannan lokacin".
"Sir....sir" Sai ya kama inda inda.
"Tell me nace!" Ya fada a tsawace.
"Mariya......mariya ce maamah". Iya abinda fuad yaji kenan wayar ta sulale daga hannunsa ta fadi qasa.
Bai sani ba......jijiyoyin hannunsa ne suka daina aiki yadda ya kamata ko kuma qwaqwalwarsa ce?!.
Tashin hankali!
Allah ka rabamu dashi!
Me karatu sai ince muje
mu qarasa
Hugumanku ce
Na gode
*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
π π π π π π π π
_Zafafabiyar_
ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2
β±§Ιβ²Ιβ₯β³
ππΌππ 149
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
149
Kowacce gaba ta jikinsa sai yaji tayi wani irin sanyi,sai ya dinga jin kaman bashi da wani sauran damar ya motsa ko ya sakeyin kuzari a daidai wannan lokacin.
"Mariya ce.....maaamah ce......itace" Sautukan suka dinga haduwa suna masa amsa kuwa a tsakiyar kansa.
"Are you okay sir?" Muryar cp tayi kutse cikin tunaninsa,wanda yaga lokaci daya fu'ad din yanayinsa ya sauya,wuta kuma ta dauke masa. Da qyar ya iya daga idanunsa ya kalli cp saboda wani dan banzan ciwon kai daya saukar masa lokaci guda.
"Yes.....am okay,akwai wadanda sukayi kidnapping 'yar alhaji hamza kibiya......za'a canzasu daga can inda suke a kawosu nan a hadesu......duk yadda ta kama ayi musu hukunci".
" Ma sha Allah....sunzo.hannu kenan?" Kai ya jinjina masa kawai. Bayason doguwar magana sam sam,don shi kadai yasan yadda kansa yake masa wani irin bala'e'en ciwo,yana jin yadda zuciyarsa ke tafasa da wani irin mahaukacin fushi da yake tsoron kada ya illatashi shi a karan kansa. Da zafi zafi ya fita a gurin,ya samu abdulgaffar suna tsaye suna dakon fitowarsa. Hannu kawai ya miqa masa
"Bani key" Ya fada ba tare daya dubu abdulgaffar ba. Baki ya saki yana kallon boss din nashi,baisan meye haka da zafi ya tunzurashi ba ko kuma ya sauyashi.
"Sir.....muje na kaika duk inda zaka je.....like kaman baka cikin mode din da za'a barka kayi driving".
"Just give me the keys abdulgaffar.......ko mutuwa zanyi a hanya kana da asara?........wanda ya kawoni duniya ma bashi da asara ballantana kai!" Ya fada da wata irin tsawa data bashi matuqar mamaki. Salin alin ya miqa masa key din,saidai kuma ya yiwa sauran team nashi alama da ido,don haka fu'ad din yana tada motar yana fita suka bishi a baya cikin salon da bazai gane shi suke ba. Suna matuqar qaunarsa da kula da dukka abinda zai cutar dashi,suna matuqar jinsa a jiki irin kusa kusannan,suna jinsa tamkar wani babban yayansu da yake da ruwa da tsaki a rayuwarsu,inda suna da hali tabbas ba zasu bari ba ko quda me cutarwa ya sauka a kansa ba.
Wani mahaukacin gudu yake zubawa wanda ya sake tabbatar musu da ba lafiya ba,hankalin abdulgaffar akan motar yana duban wanda ya bawa yayi driving.
"Ka kula sosai,kada ka matsi bayansa da yawa kada kuma ka bari ya kufce mana" Ya fada yana gyara zaman Bluetooth din kunnensa yana magana da na motar baya.
Shi kansa yasan gudun da yakeyi ya wuce qa'ida.......amma a irin zafi da bugun da tasa zuciyar takeyi sai yakejin ba wani gudu yake ba shi din. Idanunsa fes bisa kwalta amma tunaninsa yayi nesa sa gangar jikinsa. Baisan kuka yakeyi ba saida yaji iska na fifita hawayen daya silmiyo masa,karon farko tun bayan tafiyarta ta barsu.....karon farko tun bayan wasu shekaru masu yawan gaske da ya share wani abu bai sakashi kuka ba......a yau a zagaye na biyu ta sake zama silar kukanshi. Hannunsa daya ya saki dava steering din,ya shafo hawayen yana kallon su,a wannan lokaci yana jin ta gama sanyashi kuka......yayi kuka qarshe a rayuwarsa saboda ita. Tsananin kunyar anni da abba yakeji,da wanne idanu zai kallesu ya shaida musu mahaifiyarsa ce ta aikata ma diyar cikinsu autarsu haka?,da wanne bakin zai musu bayani?,wanne shine kalar sakayyar da suka cancanci su samu makwafin alkhairin da sukayi mata?.
Wani birkitaccen parking yayi qofar gidan,parking din da ya tada qura,ya kuma ja hankalin malam sa'adu dake zaune daga cikin gidan a bakin qofa yana jan tasbaha.
Da sassarfa yake takun nasa,kaman me gaggawar cimma wani abun. Security na farko ne ya hangoshi,ya kuma taso ya bude masa da sauri kafin yakai ga qarasowa.
Kusan ba sosai yake gani ba,fatansa kawai ya cimmata......fatansa kawai ya isa gareta......ya kuma tambayeta dukka akan me?,me yasa?.
Da sauri me aikinta dake saukowa daga samanta taja baya tana zubewa sanda taga shigowarsa.
"Barka da warhaka yallabai?" Sam ba gaisuwarta bace damuwarsa,bai kuma damu ya amsa ba
"Tana ina?" Ya tambayeta kai tsaye yana jin jikinsa ko ina yana rawa.
"Tana sama" Ta amsa masa tana rabewa ganin yadda ya nufo saman da sauri bata ko dire statement dinta ba.
Matakala bibbiyu ya dinga hadawa har Allah ya kaishi saman. Dab da matakalar qarshe sautin muryarta ya sauka a kunnensa.
"Ta yaya akayi saken da har wani yasan inda suka boyeta.....wanne irin hauka ne wannan?,baisan muhimmancin yarinyar nan a hannuna ba?,subucewarta da kuma kamasun da akayi yasan irin asarar da zai jawomin?.....bani da haufi akan zasu iya fadar sunana......duk da boka baiyi aiki a kansu ba amma kudin dana musu alqawari da alqawarin dana musu akan koda tsautsayi ta gifta zan fiddasu....iya wannan bazai bari su fadi sunana ba" Ta furta cikin bawa kanta tabbaci da yaqini da gaibu da qaryar daka iya fidda bawa daga ainihin imaninsa.
Wani abune ya fusgeshi sosai,da sassarfar data jawo hankalinta daga wayar da takeyi. Wani irin duba take masa me cike da tsoro da kokwanton ya jita ko bai jita ba?,zuciyarta gaba daya ta kasa bata nutsuwar bai jita din ba saboda wani irin kallo dake fita daga idanuwan da suka sauya launi suka jirkice,daga fararen qwayar idanuwa zuwa kalar makuba kaman an diga jini.
"Why maamah.....why amna?!" Ya furta da wani irin sauti me cike da razani mamaki dake cakude da karyewa yana wara hannuwansa da kuma watsasu kaman wanda yake dakon kama wani abu.
Wani irin shock taji,wanda ya kusa sanya numfashinta dakatawa na wucin gadi.
"Me yasa maamah?.....me yasa?,idan ni kinyimin.......d'anki ne.....idan kin yiwa musaddiq.......d'anki ne......amma amnah fa?!" Ya fada da wata irin murya dake neman fara rawa saboda tsananin sarewa da dukkan komai,ya kuma qarasa maganar yana nuna waje da yatsarsa.
"Me amna ta aikata maamah.....meye laifinta?" Ya kuma fada da yanayin mutumin da ya soma zarewa.
"Idan kika bada kai bori zai hau.....idan kuma baka iya kama barawo ba saishi ya kamaka" Wani sashe na rubabbiyar zuciyarta ya sake bijiro mata da wannan shawarar,shawarar data qarfafi dukkan gabbanta,ta soma qoqarin tattaro kowacce nutsuwa tata,sannan kuma ta hana kanta shiga d'imuwa.
"Kai fu'ad.....kalleni nan da kyau,idan kana cin qasa ka kiyayi ta shuru....ni dinnan nice uwarka,baka da sama dani.....ohhhh,wato kaje an karanto maka abinda zakacemin da kalar rashin kunyar da zaka yimin.....dukka ameenatu ta yo maka katunsa shine zakazo ka saukemin?!"
"Ameenatu ameenatu dai?,ameenatun da batayi miki komai ba face alkhairi?,ameenatun da ta rungumi yaran da kikaji cewa baki buqatarsu?,ameenatun data yarda ta zauna ta kashe tata rayuwar saboda ta 'ya'yan da kika watsarwa duniya?,akwai wani alkhairi sama da wannan?,akwaishi......wata can daban tayi abinda uwa ta gaza yi?,wata can daban tayi abinda uwa take ganin ya zame mata babban aiki?" Ya qarasa fada yana zuba mata ido,qirjinsa yana sama da qasa yana jin kamar ciwon zuciya ne yake shirin kamashi.
"Kin dawo kin sake kashemu a karo na biyu bayan wancan kisan da kika yiwa rayuwarmu.......me mukayi miki haka?,laifinmu ne da kika haifemu alhalin baki buqatarmu?" Ya fada a tausashe da wani irin rauni daya sanya idanunsa fitar hawaye
"Daga kowanne bangare......cikin binciken kowanne laifi Maamah dai mahaifiyar fu'ad?,mahaifiyarsa?.....maamah dai?,wadda tayi silar zuwansa duniya?,maamahn ita ta dauke amna?,amna diya ga hamza kibiya?,mutumin daya zame musu uba......bango madafarsu?,ya tallafesu a sanda duniya tayi watsi dasu,ya rungumesu,a sanda ita da take Mazaunin uwar data kawosu duniya ta sanya qafa tayi wancakali dasu?.....ya rungumi farincikinsu da baqincikinsu?,ya rabu da duk wanda zaice baya sonsu?,ya qara zafin nemansa saboda su.......yayi musu riga yayi musu wando?,yayi kawar da dauda da duhun jahilci daga qwaqwalensu?,ya daga darajarsu a idanun duniya ta hanyar haskasu da hasken ilimi?,ya maidasu mutane ta hanyar basu ilimin addinin islama?,ya karbesu a matsayin 'ya'yan da shine yayi silar zuwansu duniya bawai uban riqo ba?,yayi musu gatan da ko 'ya'yan cikinsa bai musu ba?.....amnan dai itace d'iya ga ameenatu......ameenatun data dawowa auren hamza saboda yaran?,ameenatun data sadaukar da duk wata kulawa da lokacinta akan yaran?,ameenatun da bata yarda da wani abu me cutarwa ya rabesu ba?,ameenatun da idan kanaso kaga farincikinta.....ko kaga kirkinta ka yabi musaddiq.......ka yabi fu'ad......idan kanaso ku bata alaqarku taja baya ka zagesu ko ka kushesu.....ameenatun da ta sadaukar da lafiyarta saboda su su rayu cikin aminci?,taqi kwanciya ta huta sabodasu?,taqi ci saboda saboda basuci ba?,taqi sha saboda basu sha ba?......" Ya sake tsayawa saboda yadda numfashi ke masa wahalar shaqa.
"Laifin ameenatu rainon 'ya'yanki da tayi......laifin ameenatu inganta rayuwar 'ya'yanki.....idan duka haka ne ita kuma SABREEEN FA?!". Wannan tambayar daya jefa mata tafi kowacce gigitata. Sabreen?,ya tabbata ta qarasa bude mata aiki kenan kaman yadda taci alwashi?.
"Ni na kawota rayuwarka.....kuma a yanzu bani da buqatar kasancewarku......na nuna maka ta dukka hanyar data kamata amma saboda banda kima da martaba a idanunka ka gagara fahimta".
"Sai hakan yanzama license ya zama halaccin da zaki tura wani d'a namiji gidan aurenta.......dakin da d'anki ya gina saboda matarsa ta sunnah?.....yaje ya keta hurumin ubangiji?,.......kin auramin sabreen saboda ki.mallaki fu'ad......fu'ad din da bai mallaki wuta ko aljanna ba......fu'ad din da bai mallaki rayuwa ko mutuwa ba.......bai mallaki komai ba face wata aba da ake kira DUKIYA wadda ka iya zama fitina da jarrabawa ga bawa.......". Yana kaiwa qarshe ya jawo littafi da abun rubutun daya gani ajiye a gefe,ya jawo side table ya ajiye a tsakaninsu ya daga idonsa yana kallonta duba na kai tsaye.
*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
π π π π π π π π
_Zafafabiyar_
ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2
β±§Ιβ²Ιβ₯β³
ππΌππ 150
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
150
"Na baki dama......daga farkon littafin nan har bangonsa ki rubuta adadin kudin da kikeso......na baki dama ki rubuta adadin alatun rayuwar da kikeso......na baki dama ki rubuta tsarin rayuwarki na shekaru dari nan gaba idan har zaki kai sannan......ni kuma zan tabbatar miki da wannan mafarkin,muddin zaki zare kanki daga rayuwarmu.......muddin zaki fita salin alin daga rayuwarmu......muddin zakiyi nesa da rayuwarmu......indai kin amince zaki bar iyalin ameenatu su rayu cikin salama su kuma zauna lafiya........ina fada miki hakanne cikin harshe na girmamawa.......ina gaya miki hakanne saboda har yanzu sunanki MAHAIFIYARMU.......Duk da girman abubuwan da kika aikatawa mutanen da basuji ba basu gani ba......ina gaya miki wannan zabinne saboda shine zaifi mana sauqi mu dake" Ya qarasa maganar yana jin wani mulmulallen dutsen wuta yana tsaya masa tsakanin wuyansa da qirjinsa yana qoqarin turashi da qyar. Fata yakeyi inama ace wani ko wata ce can daban suka aikata musu wannan abun ba maamah ba?......inama ace wasu mutanen ne daban keda alhakin dukka wadannan abubuwan ba maamah ba?,ya rantse da Allah da sai ya ganar dashi kuskuren bari da yayi uwarsa ta haifesa zuwa gidan duniyar ma gaba daya.
"Fu'ad!.....ni kake gayawa wannan maganar?,ni kake cewa zaka rabu dani saboda ameenatu?" Ta tambaya tana jin wani irin tashin hankalin jahiltar matsayin ameenatu da tayi a baya. Ashe har zai iya katse alaqar uwa tsakaninsu saboda ameenatun dai?.
"Fu'ad!.....ka saurareni da kyau!......."
"Jaffal qalam" Ya fada yana miqewa daga gabanta. Zuciya da shaidan dukka suna kusa,duk sanda zai kalli fuskarta fuskar mahaifinsa yake kalla a tayi watsi dashi cikin tsananin ciwo bayan ta gama illatawa luguiguita lafiyarsa cikin mugunta.......duk sanda zai kalleta saiya