Showing 471001 words to 474000 words out of 557259 words

Chapter 158 - πƒπ”ππˆπ˜ATA BOOK1 AND 2 HAUSA NOVEL

HUGUMA   

03 Nov 2025

439

ya tambaya tana tsayawa cak.

"Am okay dude"

"Ma sha Allah.....ka karba envelope"

"Na karba"

"Ka bude?"

"Na bude dude.....but I'm.....I'm speechless dude.......rubutun jikin invitation card dina da ruwan gold na ainihi?" Murmushi ya subucewa fu'ad.

"Kafi qarfin wannan dude......kada ka sake magana akai.....akwai sadakin fannah a daga envelope din....have you seen it?"

"What?,dowry fa kake magana dude?......wannan gold din ya ninka abinda suke karba a matsayin sadaki......babanta malami ne,kada yaga mun zura da yawa fa".

"Fannah tafi qarfin haka a gurinmu....tunda takeson wannan tsohon tuzurun namu,ta kuma amince zata zauna mana dashi da zuciya daya.....sadakin mace baya yawa a musulunce,ko nawa aka bata yayi,saidai ma yayi kadan,yadda kace babanta malami ne nasan yasan da hakan,sayyadina umar yaso qayyadewa a zamaninsa,wata mata ta tunasar dashi annabi baiyi hakan ba, sai ya qyale shima.... Ka fahimta?"

"Ya ilahi dude.....am speechless seriously"

"Zamuyi fada dakai......ina fata ka riqe data din....kwana hudu......saura kwana hudu dude dina ya angwance" Sautin murmushinsa ya riski fu'ad,hakan kuma ya masa dadi a haka sukayi sallama. A duniya bayajin yana da wani abu da zai iya sakawa farouq dashi koda meye yayi masa.

Musaddiq ya kira wannan karon,shima dai kaman yana kusa da wayar ya daga. Muryarsa da mugun sanyi ya amsa sallamar,still shima tambayarsa yayi lafiya yake?.

"I'm fine hamma"

"Maamah ko?" Shuru musaddiq yayi yana mamakin yadda ya gano haka ta farat daya. Shurunsa ya bawa fu'ad tabbaci,ya sauke numfashi.

"Idan ka dorama kanka daukan damuwoyinta ba inda zakaje a rayuwa,zakayita zamane kamar a inda ta tafi ta barka ba tare da damuwan yadda rayuwa zata kasance maka ba.....na kiraka na gaya maka,kayi magana da musaddiq kai dashi ku duba gidajen nan dana bashi details dinsu ku zaba,za'a hade bikinka sana farouq in sha Allah,so ka ajiye damuwan da bata cancanci damuwarka ba.....ka fuskanci rayuwa da reality dinka.....but kada ka sake ka manta da wannan......ka riqe mana amna sai mutuwa ce zata raba". Mutuwar daya fada ta saukar masa da wani irin matsanancin faduwar gaba......ta kuma tuna masa da maganarsu ta dazu da maamah.

"Mutuwa hamma?".

"Yes.....mutuwa,saboda ita kadaice ta isa ta raba Soyayyar masoya" Shuru ne ya wanzu tsakaninsa da shi,har sai da fu'ad din yace.

"Kana layi?"

"Inaji hamma"

"Good......komai da amna zata buqata ka rubuta ka turamin.....bance ko sisinka ka saka a bikinka ba" Baima jira ya masa godiya ba ya katse,saboda baya buqatarta,yanajin wani wajibinsa ne ya saukeshi.

Anni ce ta qarshe daya kira,amna na kusa da ita ta miqa mata wayar.

Ban gajiya suka yiwa junansu,sannan itama ya buqaci ta bada duk wani abu da take buqata.

"Muhammadu kabar 'yan uwanka suyi wani abun mana?" Murmushi yayi

"Anni sai idan bana raye.....ki fadawa amna ta rubuta komai da take buqata na lefe.....idanma ba zata iya ba tazo nan gidan su hadu ita da duniyat....." Saurin katsewa yayi bai qarasa ba,kunya ta kamashi ya aza hannunsa aka yana sosa sumarsa. Murmushi me sauti ya qwacewa anni

"Ita da duniyarka ameenatu" Murmushi shima ya saki.

"Su rubuta komai,bance ta dauke masa komai ba". Kaman sauran bai jira ta masa wata godiya ba ya katse wayar,ya zubawa sabreen ido wani abu yana yawo cikin ranshi.

Da alama baccin ya mata dadi sosai,amma dole ya tasheta don akwai magana me muhimmanci da zasuyi da bata buqatar takai safiya,yana ganin kaman tayi nisa.

Wayar anni ta ajjiye gefanta,tana jin wani abu yana sauka a ranta. Tabbas fu'ad din wani kyautar Allah ne a garesu,bawai don dukiyar da yake da ita ba.....aah....ta jima da sanin haka tun yana fu'ad dinsa dan makaranta secondary school,fu'ad dan bautar qasa. Wata irin zuciya ce shimfide a qirjinsa,wani irin dattako daya girmi shekarunsa......wani irin halin girma me dumbin yawa.

"Tabbas mariya inda kinsan irin kyauta da alkhairin da Allah yayi miki a rayuwa da baki gudu kin bar muhammad ba.....da baki gudu kinbar musaddiq ba". A tattare dasu gaba daya tana ganin wata irin nagarta ta musamman.

"Hammanki yace ki rubuta ko kije gurin addarki ki.masa list na kayan lefe duka" Anni ta fada tana nazarin amna data fahimci ta yawaita shuru shuru tun daga yammacin yau din.

"Lefe ann?" Amna ta tambaya da wata sassanyar murya

"Wani abun daban kikaji na fada?" Anni ta fada tana nazarinta. Kai amna ta girgiza,haka kawai taji hawaye sun cika idanunta,sai anni ta kasa jurewa.

"Meya kuma?"

"Tsoro nakeji anni......gabana yanata faduwa" Sai hawayen da take maqalewa ya gangaro mata.

"Tsoro?" Anni ta maimaita,kai amna ta gyada mata. Yankewa gaban anni yayi ya fadi,ta sauke numfashi tana ambaton sunan Allah.

"Tashi kije kiyi alawala,ki karanta hasbunallahu wa ni'imal wakil qafa dubu kafin ki kwanta". Kai amna ta gyada sannan ta miqe a sabule tana fita a dakin zuwa nata.

"Addanmu" Fu'ad dake tsugune gaban sabreen da bacci yaketa danneta ya fada yana leqa fuskarta. Da qyar ta sake bude idon nata a karo na uku.

"Adda sabreen.....tashi don Allah" A cikin baccin taketa mamakin kiranta da adda din da yaketa yi,saita miqe tana daquna fuska.

"Hamma.....bacci"

"Zakiyi,na miki alqawari,amma kafin sannan jeki wanki fuskarki ki dawo". A daddafe ta miqe saboda nauyin bacci,ta lalubi toilet din ta shige.

Ba jimawa ta fito,fuskarta tayi fresh da digo digon ruwa,idanunta sun dan tashi kadan alamun bacci,ta zauna saman sofa tana dubansa.

Ajiye abinda yakeyi yayi ya taso,ya iso gabanta ya tsugunna a hankali. Hannuwansa yakai ya kamo tafukan hannayenta a tausashe.

"Adda sabreen" Ya maimaita fadi yana murmushi. Idanu tadan ware tana dubansa wani malalacin murmushi yana qwace mata. Kai ya jinjina mata.

"Kin bamu daman neman auren sister huda?.....kin bamu izini mu nemawa musaddiq auren sister huda?".




*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862



𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀
_Zafafabiyar_

ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2

β±§Ι„β‚²Ι„β‚₯β‚³

π™‹π˜Όπ™‚π™€ 136


*_Bgawo's KITCHEN AND APHRODISIAC_*


*_WATA KILLATACCIYAR MASARAUTA CE,WADDA KE QUNSHE DA DUKKAN NAU'IKAN ABINDA KUKESO_*


*_GIRKE GIRKE NA ZAMANI_*

*_KAYAN MAQULASHE DA NAU'IKAN DRINKS KALA KALA_*

*_INGANTATTUN TSUMAMMUN MAGUNGUNAN GYARAN MUTUNCIN 'YA MACE......GYARA IRIN NA IYAYE DA KAKANNI DA INGANTATTUN MAGUNGUNAN DA BABU DUNGUSHE KO KOKWANTO A KANSU_*

*_KALAR MAGUNGUNAN DA SAO WAJEN IYAYENMU NA DAURI.....INGANTATTUN SAUWOYI DA SAQE SAQI DA AKA SARRAFASU ZUWA MAGANIN GYARAN DIYA MACE_*

*_BIKI KUKE DASHI KO SUNA?_*

*_SAUKAR KARATUN QUR'ANI?_*

*_KO KUMA WALIMAR AURE QARIN MATSAYI A GURIN AIKI KO KUMA WANI QWAR QWARYAN TARO?_*

*_KO YAU DIN BAKIJIN SHIGA KITCHEN?,TSAFTATACCE KUMA INGANTACCEN ABINCI KIKE BUQATA A CIKIN WARMERS DINKI KO FOOD FLASK?_*

*_HAIHUWA KIKAYI?_*

*_KO GYARA ZAKIYI KAWAI A MATSAYINKI MA CIKAKKIYAR MACE?_*

*_BGAWO'S KITCHEN SHINE MUHALLIN DAYA DACE DA DUKKA WADANNAN BUQATUN NAKU_*

_Maza garzaya ki tuntubesu ta wannan number wayar_

08104553105
08127084190

*_zaki godemin qwarai da haduwa da BGAWO'S KITCHEN_*


*_BGAWO'S KITCHEN_*
*MATATTARAR BIYAN BUQATUNKU*




136


Wani saukar ba zata zancen yayi mata,wani irin zuwa ya yiwa kunnuwanta.

"Saddiq kuma?,saddiq dai hamma?" Ta fadi da sautin muryar bacci da har yanzu bata gama warwarewa ba,banda ta zuba ruwa saman fuskarta da sai tace cikin jerin gwanon mafarki kawai wannan maganar take dibanta. Murmushi ya saki me sanyi yana jinjina mata kai.

"Eh......saddiq dinmu addanmu......inaso ya zama mijin huda nan da kwana hudu,kaman yadda farouq zai zama mijin fannah in sha Allah" A hankali ta daga ido tana sake duban fu'ad din,sai takeji kaman wasa yake mata da hankali kawai ko tsokana,saidai kuma ko daya bataga wannan a cikin idanunsa ba.

"Hamma.....huda fa?.....ka manta mudin ba kowa bane hamma.... Mu din ba wasu madaukaka bane,ni din kawai a cikin family dinku ya isa,basai huda ta shigo ba...."

"Shshshsh" Ya fada yana dora yatsantsa akan lips dinsa. Bayason wannan karayar da take nunawa,bayason wannan raunin da yadda har yanzu ta kasa jinta kaman kowa.....bayason yadda ta kasa daina tuna wacece ita a baya

"Damu daku dukkaninmu abu daya ne yayimu.....jirgi daya ne ya kwaso mu.....ki manta akwai wani lokaci da abinci da sutura suke gagarar muhammad fu'ad?....ki manta akwai wani lokaci daya shude da yunwa take saka musaddiq kwana yana kukan yunwa?,kin manta wani lokaci daya shude fu'ad dan jari bola ne?......kin manta sanda saddiq ke kwana da yunwa saboda ba gatan uwa a gefansa?,duka damu daku ki gayamin meye banbanci a ciki?" Shuru tayi tana tuna komai kaman yadda yake tunasar da ita yanzu.

"Hamma.....amma huda batayi qanqanta ba?.....yanzu zata gama secondary school fa......a haka an sanyata a makaranta da wuri kaman yadda abbanmu yake mana....." Murmushi ya saki yana dan jan kumatunta.

"Qanqanta?.....ke din kanki duka duka shekara nawa kika bata?,banajin yakai biyar,ba gashi muna zaune ba?".

"Hamma karatunta fa?" Hannu ya sanya yana dungure mata kai da sauri

"Lallai dai sai an ja mana aji kafin a bamu auren sister huda.....lallai ko yaya wai sai an wajiga mu?.....me huda zatayi da karatu duniyata?,ba huda ba.....ko wanda ke rayuwa qarqashin inuwar jadda banajin zai buqaci karatu saboda ainihin buqata ta lalura.....saidai duk me sha'awa yayi karatun don dai sunansa ilimi.....ba abinda huda zatayi da takardu.....saidai.idan har tanason karatu saddiq bazai hanata ba.....za'a dauko mata duk kalar malamin da takeso ya koyar da ita matakin ilimi daga na college har zuwa university har PhD ma.......idan kuma makaranta takeso......ta zabi duk makarantar da takeso a fadin duniya cikin jerin qasashe da muke dasu a duniya 195 zuwa 200....kowacce take so zataje in sha Allah......sai me kuma......a shirye muke mu karba duka qorafinki" Ya qarasa fada yana tsareta da ido tare da jiran abinda zata sake fadi.

A hankali ta jinjina kai

"Na amince hamma.....na bada izini bisa sharadi da alqawarin zai bata dukkan wata kulawa data dace koda bayan raina". Wani zazzaro idanu wajen fu'ad yayi yana dubanta.

"Kul.....karki sake zancan bayan ranki my world......waye ya gaya miki fu'ad yana da sauran rayuwa bayan babu taki?". Idonta ta maida ta lumshe a hankali tana murmushi.

" Zamu rayu tar in sha Allah......zamu kula da yaranmu mu kuma basu tarbiyya tare" Ya fada yana sumbatar hannunta a tausashe.

"Na gode sosai duniyata.....na gode sosai da sadaukarmana da daya daga cikin abubuwan da kike matuqar so a duniya.....kika yarda ta zama abokiyar rayuwar saddiq"

"Kafi qarfin komai a wajena duniyata.....kafi gaban haka muffin". Ta fada itama harshenta da sautinta cike da qauna da soyayya.

" Bayan gidan malam......sai ina da ina kike kai taimako?" Ya sake soko Mata tambayar da bata taba kawota ba. Fararen idanunta ta daga ta kalleshi,sai kuma ta sauke idanun nata qasa tana jin nauyinsa. Batason abinda zai sanya ya dauko mata wannan zancan na abinda ya wuce a tsakaninsu.

"Ki bani dama.....inaso ki dore da aikin ladan da kikayi niyya in a halal ways.......inaso na miqar dake kici gaba da abinda kika fara a baya". Sake kallonsa tayi a karo na biyu......tana jin yana sake shiga rayuwarta yadda ya kamata. Soyayyarsa tana sake hudata,wani mafarki ne wannan nata,dasu take kwana dasu take tashi.....hayewar su huda kawai bai sanya zuciyarta ta kwanta d'ari bisa dari ba.....bai sanya zuciyarta ta samu nutsuwar da take yunwar samu ba. A yanzun a kuma wannan lokacin sai gashi ya gama qarasa karanta tunaninta kafffff yana son xike mata ragowar gibin da ya rage.

"Me yasa a kowacce rana kake sake karantar zuciyata?,me yasa a kowacce rana kake abubuwan da suke sake haukatani a kanka muffin?". Idonsa ya lumshe yana budesu duka a lokaci guda. Yanason irin wannan yanayin.....yana son irin wannan lokacin da zaiyi zaune kawai a gabanta yana tana tona masa asirin zuciyarta.

"Sabrrrrr" Ya sake kiranta a tausashe.

"Haqqina ne.....kuma cikar kamalar kowanne d'a namiji kenan,ya karanci wace matarsa.....me tafi so?,me tafi buqata?,me zaiyi ya mallaketa?". Mallakar daya fada ta sakata fashewa da dariya tana zaro ido.

" Hamma.....mallakata kakeso kayi?"

"Nama mallakeki duniyata.....na mallakeki....kedin tawa ce ni kadai har abada" Ya fada yana daga yatsunsa guda biyu.

"Gidan marayu.....gidan gajiyayyu.....yaran da iyayensu suka mutu suka barsu kuma babu me tallafa musu irinmu" Takai qarshen maganar muryarta tana karyewa.

"Ki zauna ki tsara dukkanin burinki akan wadannan gidajen". Ya fadi yana miqewa tsaye. Wani irin sanyi taji yana sauka saman zuciyarta

"Ina fata ubangiji ya lullubeka da dukka rahamarsa......ya yaye maka damuwarka.....ya kyautata qarshenka.....na gode da karamcinka karimin mijina.....na gode da wannan halin dattako naka uban 'ya'yana". Murmushi me sanyi ya kubce masa,yanajin alfahari da wannan addu'ar tata.

"Allahumma ameen matata 'yar aljanna.....amma saura abu daya da baki roqamin ba". Idanunta ta juya,abinda ya sake tafiya sosai dashi

" Me kenan muffin?"

"Baki roqi Allah ya qarawa wannan ameenatun so na ba.....so nake ameenatu ta soni fiye da yadda takeson kanta,don kuwa ta samu wanda zai kula mata da kan nata" . Kunya ta sakata sanya tafin hannunta ta rufe fuskarta kafin tace.

"Inda ana iya bude zuciya ko qirji a nunawa wani.....tabbas da na bude maka tawa zuciyar kaga abinda yake ciki a kanka,wataqila zakafi gasgatani.....don maganar fatar baki tayi kadan" Rasa me zaya ce mata yayi,sai kawai ya tsugunna yana kissinh forehead dinta a tausashi.

Yana dauke labbansa tana daga idanunta da sauri,sai ta soma rarraba idanun nata tana a narke.

"Kai.......ina doughnuts dina?" . Dubanta yayi

"Wanne doughnut?". Ya tambaya yana tunanin ko mafarki tayi a dazun kafin ya tashera. Tambayar tata da yayi sai taji kaman zata saki kuka

"Doughnuts dina mana da ma'u ta bani......a nan fa na ajjiye naci kadan na ajiye sauran". Qaramin murmushi yayi.

"Kin cinye madam....ni na tattara kwalin na zuba a dustbin". Idanu ta waro waje tana dubansa sosai da salon rigima a muryarta.

"Ka sakamin a shara?,wallahi ban cinye abuna ba,akwai saura" Ta fadi tana miqewa zumbur gami da nufar dutsbin din. Da mamaki yake binta da kallo ganin yadda ta bude dustbin din tana ciro kwalayen.

"Kai?,ka cinyemin?" Ta fada cikin sanyin jiki hawaye yana taruwa cikin oily eyes dinta. Dariya ma abun ya bashi,ya daga hannunsa alamun surrender yana dubanta.

"Innalillahi,Allah ba ruwana,sanda nazo ba komai a ciki sai boxes din da leda". Dariyar tasa ta qular da ita,sai kawai ta fashe da kuka tana sakin boxes din.

"Wallahi kaine.....kaine ka cinyemin kuma bazan yarda ba" Mamaki sosai ya kamashi ganin yadda ta zube tana kuka bilhaqqi,hawaye shabe shabe ta dage wai shine ya cinye mata. Da sauri ya isa inda take yana miqa mata hannu.

"Yi haquri ki tashi.....eh na yarda nine na ci". Ya fadi hakan don ya lura qaryata ba shine yaci din bama qular da ita yakeyi.

"Dama kai dinne ko?" Ta fada tana watsa masa harara da jiqaqqun idanunta,sai ta sake fashewa da kuka sosai kaman wadda aka yiwa dukan tsiya harda shashsheqa.

Ya rude sosai don ta maida abun serious matter. Ya sulale ya tsugunna a gabanta yana cewa.

"Am really sorry my world......taso muje ki gayamin a inda aka siyo a sake nemo wani". Sai data galla masa harara sannan tace.

"Kaduna.....kaduna ne wajen maman ummi".

"Kaduna?" Ya maimaita.

"Eh" Ta fada cikin son jiran mutum yayi wani abun ta sake barke masa. Kansa ya daga ya kalli agogo yana duba lokaci. Qarfe goma na dare,wa zaya tasa zuwa kaduna yanzu. Idonsa ya mayar kanta,saiya taras ta zuba masa ido tana kallonsa,dukkan alamu kuma sun nuna rigima ce a kwance idan ya musa.

"Is alright.....bani details na masu abun".


"0803 049 9555,wallahi tunda ummee ta haifeni ban taba cin doughnuts me dadin nata ba" Ta fada bilhaqqi da gaske har zuciyarta tana jin tun kafin ya kawl ma yawunta ya tsinke. Idanu warwaje yake kallonta. Tashin hankali!,ya fadi saboda yadda yaga tsaf ta haddace number,yaushe hakan ta faru oho shima bai sani ba.

"Ina zuwa" Yace mata yana takawa a hankali yana sauka qasan. Shi kam yasam yanzu ba lallai a bawa jadda wings daman tashi ba,kafin ma su nemo umarni,pilot din ya isa su tashi ai asuba yayi,saidai duk da haka bai fasa kiran number din ba.

Ainihin sunan daya fito ameena sai yaji kimar me number ya qaru a idonsa tun ba'a daga kiran ba. Bugu na uku aka dauka da cikakkiyar sallama ya amsa shima.

"Am sorry,na kira late at night......i don't know ko matar aurece.....am sorry idan hakanne"

"Ba komai" Matar me kirki ta fada. Bayanin dalilin kiran yayi sannan ya dora.

"If possible goben zan aiko a taho dake,kizo kiyi mata sai a maidaki.....kiyi naming price dinki,kada ki damu ko nawa ne ki zaba i will pay it". Murmushi tayi.

"Ba matsala.....ko goben da safen ma ana iya samun ko pieces nawa takeso.....akai akai sai a dinga zuwa ana karba mata,Allah ya raba lafiya,kowanne ciki da yadda yake zuwa ma mace,sai haquri". Yaji dadin magananta sosai,don daga yanayinta ya fahimci ba yarinya qarama bace,yayi godiya sannan ya kashe ya kira farouq.

Bugu daya ya samu farouq,da alama bacci ya fara daukansa ma.

"Farouq akwai matsala fa" Maganan da ta saka farouq miqewa ya zauna

"Me ya faru?" Ya tambaya. Ajiyar zuciya ya saki ya masa bayani a nutse.

"I don't know ina zan samu doughnuts?.....kune masu zuwa irin guraren nan".

"Ba damuwa......bari na duba wani guri kusa damu......sun iya sosai zataji dadinsa".

"Thank you dude.....you save me" Ya fada yana dan dafe goshinsa sannan suka yanke kiran.

Lallabata ya dinga yi har aka gaya masa ga saqo daga bakin gate. Sanda yaje har farouq din ya aje saqon ya juya,ya yaba masa sosai irin saurin da yayi don duka duka mintuna talatin ya iso,ya tabbatar wannan gudun nasa ya zuba.

"Ga doughnuts din" Ya fada da murmushi yana aje box din a gabanta. Da zumudi ta jawo ledar ta bude. Tun a yanayin packaging din ta tabbatar akwai matsala,banbamce babance take gani iri iri da wancan,ta danne tana bude doughnuts din.

Kanta ta daga ta kalleshi,ya dage mata gira yana qoqarin lallabata,can qasan ransa yana fatan kada ta ballo rigima kuma.

Kanta ta mayar kai,ta gutsira tana kaiwa bakinta. Taunawa daya biyu ta furzar,muryarta tana rawa ta kalleshi

"Wannan bashi bane.....Allah bashi bane".

" I know

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login