Showing 105001 words to 108000 words out of 557259 words
yana daya daga cikin abubuwan da suka sanya yake janye jiki da rayuwarsa sosai daga gidan. Duk da komai na fasalin gidan ya canza,ba wani abu da yayi saura dangane da ainihin ginin gidan na baya,to amma dai wannan filin....wannan gurbin da wannan muhallin da aka aza tubalin ginin gidan har yanzu dai shine a wajen. Har yau har kwanan gobe idanunsa basa mantawa da tsarin gininsu na asali,wannan ya sanya idan ya kalli wasu guraren sai ya tuna da JADDA sai kuma ya tuna da ABBANSA,duk da guraren a yanzun sun sauya sun koma wasu abubuwan na daban,amma tambarinsu yana nan kafe qasan ransa da zuciyarsa.
Cike da girmamawa,martabawa tare da kallon Cikakkiyar kima da darjtawa malam sa'idu yake miqewa sanda ya fuskanci dosowarshi gidan.
"Barka da zuwa yallabai.....sannu da zuwa" Malam sa'idu yake fadi cikin mutuntawa.
"Barkanmu da warhaka baba.....mun sameku lafiya?" Fuad din ya furta shima cikin tsananin bada girma. Malam sa'idu bawai me gadi bane kadai a gareshi,yana da wani role da yake takawa da kuma wani ajiyayyen matsayi da fuad din ya bashi ba tare da sanin kowa ba.
Malam sa'idun da asalinsa me saida kayan marmari ne a bakin titin tsohon layinsu,wanda a yanzun layin ya koma tacan katangun gidansu yake,qofofin sun dawo bayan gidansu na asali,inda kusan gaba daya fuad din ya siye layin sai tsirarun gidajen da suke mazauna ciki suna da buqatar zama a ciki. Tun asali bayan layin nasu suna kiransa ne dama da layin 'yan gayu,don kusan manyan gidaje ne ata wajen,kamar yadda kusan mafi rinjayen unguwar tasu layinsu ne kadai keda qananun gidaje jifa jifa. To a yanzun layin duka ya zama qarqashin kulawar fuad da wani irin kwalta da aka zuba,gate a farkonsa da qarshensa da manyan fitilu jere reras.....cctv cameras da masu gadin layin saboda tsaron dukiyar mazauna layin da rayukansu.
Bayajin malam sa'idu zai iya ficewa daga tarihin rayuwarsa ko zuciyarsa. Yadda mahaifinsa baya iya cin komai haka malam sa'idu zai hada fruit ya bashi daidai qarfinsa lokaci bayan lokaci duk sanda Allah yakai wucewar fuad ta wajen,ana tsaka da haka malam sa'idu yaje ganin gida,bai kuma dawo ba har sai bayan wasu shekaru. Bai manta da yadda malam sa'idu ya nuna jin ciwon rasuwar abbansa ba,wannan ya sanya ko da rayuwa ta kawosu inda suke a yanzun ya nema malam sa'idu. Kyautata rayuwarsa yayi da gasken gaske ba tare da mutane sunsan da hakan ba......amma sai ya ajeshi a mazaunin me gadi bisa shawararsu da amintarsu shi da malam sa'idu din,kuma hakan bai hana ya bashi albashi ba duk wata,saidai ba irin albashin da ake jifan gamagarin masu gadi ba. Malam sa'idu baisan wace maamah ba bare anni,tun a baya wajen sana'arsa yake lazimtar zama,bai tara jama'a bare gulma dayi da gidajen alumma ya shigo ciki har yasan abinda gidan wani ke ciki,abu daya ne dai da har yau bai fahimta ba,jaddada gadin gidan da kula da shige da ficen matar gidan daya kasa tantance matsayinta a wajensa. Da yake bame damuwa da abinda bai shafeshi bane bai taba tambaya ba,yana dai aikinsa yadda akace,duk kuma abinda muhammad din yake da buqatar sani yana sanar masa.
"Mu zauna daga nan" Fuad ya fada yana neman wajen zama saman bencin da malam sa'idun kan dan kashingide akai wani lokaci.
"Aa haba yallabai.......ai sai ka bata kayanka kuma......bari a dauko maka kujera daga cikin gida kafin mutanen gidan su qaraso"
"Yi zamanka" Ya fada cikin ko in kula. Mamaki ya sake kashe malam sa'idu. Duk uwar dukiyar daya mallaka,kyau....ilimi duk basu sanyashi jin ya bambamta da sauran jama'a ba.
"Ita kadai ta fita?" Fuad din ya tambayeshi yana zaro wayarsa
"A'ah....su biyu ne" Ya amsa masa kai tsaye,don ba tambayar da zaiyi masa da zai boye masa wani abu. Kai ya daga yana duban malam sa'idu din jin ya ambaci ita da wata.....Allah yasa abinda yaketa qoqarin kaucewa da fatan kada ya faru ba shine ya soma faruwa ba
"Sun jima da fita?"
"Eh ya kusa awa biyu zuwa uku haka" Ya sake amsa masa. Idanu yadan zubawa malam sa'idu din kamar yanason fahimtar wani abu daga gareshi,sai kuma ya janye idon yana fesar da iska daga bakinsa,sai ya samu kanshi da Maida wayar aljihunsa kawai ya miqe daga zaman da yayi niyyar yi da,ya dawo gaban gidan ya tsaya sosai jikin realer da aka yiwa gaban gidan adon flowers da ita,idanunshi bisa hanya zuciyarsa na karanta masa abubuwa iri daban daban.
Tun dazun tunani da hankalin maamah yana kan hajja,har zuwa lokacin da mintuna kadan suka rage musu su isa ga unguwar
"Yarinyar can fa hajja kin kaita wata unguwar tana jira". Murmushi hajja ta saki da qaramin tsaki a hade
"Bari ki gani" Ta fada tana daukan wayarta daga saman cinyarta.
A hands free ta saka wayar,bugu daya ta daga. Akwai qaguwa sosai cikin muryartata,amma kuma bata isa ta nuna hakan ba koda da wasa kuwa
"Hajja na qaraso"
"To yayi.....na bar wajen,zan turo miki address na inda zaki sameni,na gaji gida nakeso na wuce,kada ki wuce minti biyar baki iso ba"
"To hajja" Ta amsa mata a sanyaye. Katse kiran tayi,murmushi na subuce mata ta kalli maamah
"Yanzu nan zata zo cikin minti biyar?" Maamah ta tambaya cikin mamaki
"Kuma mijinta shi zai maidani gidanma a gabanta ba....da kai da kaya ai duka mallakar wuya ne". A gajarce ta tura mata adress din,sannan ta fara qoqarin kiran yahaya daidai sanda suke karyo kwanar da zata sadasu da shimfidadden jadda street din dake rubuce jikin wani qaramin allo dake kafe a farkon layin.
Tunda ya hangi motar ya ganeta kafin takai ga isowa. Yaci gaba da bin motar da idanu har ta qaraso qofar gidan,tayi kuma yi tsaiwar bawa malam sa'idu umarnin bude mata hanyar shigewa,sai a sannan ya sauke hannayensa yana duban tayoyin motar da sukayi bududu abinda zai shaida maka ba qaramar tafiya akayi da motar ba,tafiya me tsaho kuma cikin guraren da basu da shimfidadden titi ya saka kai yana wucewa ciki kafin malam sa'idu ya kammala bude musu gate din.
Kansa a qasa yake takawa cikin gidan,haka kawai zuciyarsa yakejin bai gamsu da yanayin fita da kuma shigowar motansu a yanzu ba. Cikin falon ya yiwa kansa gurin zama. Ba kowa a ciki,don dama muddin idan bata nan din bata aminta da masu aikin nata su kusanci falon har sai ta dawo.
Tun tsaiwarsu bakin gate din ta ganshi,wannan ya sanya driver yana aje motar qasan rumfar aje motocin ta bude ta fito
"Ya da sauri haka ko duk gajiyar ce?" Hajja ta tambayeta sanda take tattaro jakarta
"Yaroncan Muhammadu na gani,yana ciki yana jira,bansan tun yaushe ya shigo gidan ba.....banyi zaton jirgin safe zasu biyo ba" Ta fadi hankalinta yana yin cikin gidan. Da kallo hajja tabi maamah din ganin yadda duka hankalinta yayi cikin gidan,sai kawai ta jinjina kai ta soma yunqurin fita a motar itama tabi bayanta.
Qafafunsa na harde cikin juna yayin daya jingina bayansa da makarin kujerar,ya zube idanunsa duka a bakin qofa yana jiran ganin shigowarta. A wannan yanayin ta murda qofar ta shigo,tanata qoqarin azawa fuskarta rashin sukuni da gasken gaske. A wannan karon batajin zatayi masa da wasa akan dukka buqatun da zata bijiro masa dasu.....dole yayi yadda takeso wanda shine zai zama cikamakin burin MALLAKAR 'YA'YANTA.
Duk yadda taso tayi diban watsin tsiya dashi amma sai kwarjininsa yakeson bugar da ita. Hausawa sukace kuma wanda yayi me kyau ya sani haka wanda yayi maras kyau. Idanun da yake binta dashi sai ta dinga jin kamar yanason karantar daga ina take?,me kuma taje yi?.
"Sannu da zuwa" Ya fada a nutse yana zare qafafunsa daga cikin na juna daidai sanda take aje mayafinta da jakarta
"Ai kaine da sannu" Ta fada a taqaice tana ta tattalin fushinta da bacewar fara'a daga fuskarta,saidai kuma wani bangaren na zuciyarta yanata saka mata tsarguwa da kuma shakku.
Hada ido sukayi a karo na uku,sai ta kasa jurar kallon da yake binta dashi din
"Kana mamakin na baka umarni baka bi ba kazo na sameni a raye ban mutu ba ko?" Ta fake da wannan,don batasan da abinda zata iya qalubalantar kallon nasa dake mata wani irin nauyi da kwarjini ba. Idanun nasa ya sauke a qasa yana girgiza kansa,baikai ga cewa komai ba ta sanyo kai da tata sallamar.
Ita dinma dashi suka fara hada idanu,saidai nata kallon yafi na maamah tsini a nata idanun da zuciyar. Kwarjininsa ya cikata fal,hakanan alfaharin ganin farko wa mamallakin jadda diamondchore resources ya cikata.
Sunansa ya jima da shiga kundin nata lissafin,saidai a dukka hasashenta bata taba tunani ko zaton samunsa a nan kurkusa ba.....bata taba kawowa cewa yana da wata alaqa ta jini me kusanci irin haka da tsohuwar qawa kuma aminiyarta mariya ba.....bata taba hasashen mariyan tana da nasibin haifar babban mutum har kamar Muhammad jadda ba.
"A'ah.....yaron namu ya iso kenan......maraba" Ta fada tana sauya reaction na fuskarta cikin qasa da second biyar tare da takowa cikin falon a hankali. Akaikaice yake dubanta da wani irin kallo,sam baisan fuskarsa ba......bai kuma tuna ko yaya a inda ya santa ba,ta yaya ita din akayi tasan wayeshi?,yaya akayi tasan daga tafiya ya dawo?.
"Bana jin zaka iya shaidani.....shi ya sanya banyi mamakin musaddiq daya kasa ganeni ba.....ga yayansa ma ya gaza shaidani?" Ta fadi tana sakin fara'ar da bata kai ga qarasawa ainihin zuciyarta ba,yayin da kwarjininsa ke barazanar hanata samun abun fadi. Still dai baice komai ba yana ci gaba da dubanta. Ko dis baiji matar tayi masa ba,bai hangi dattako ko kamala da sukayi daidai da shekarunta ba a tattare da ita,sai kawai ya dauke kallonsa daga kanta don baiga amfanin maida hankali tare da son qoqarij fahimtar abinda ya tabbatar daga qarshe bame amfani bane,amma ina suka fita har na tsahon awannin ita da maamah din?. Tambayar data maqale masa kenan,bashi kuma da amsa.
Qafarsa kawai ya miqa ya zira takalmansa ya miqe
"Lokacin sallah ya kusa,zanyi salla na dawo" Ya fadi yana juyawa a nutse yana fita a falon.
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
PAGE 57
_________________________
https://chat.whatsapp.com/D4mOQ8gmKb7EXZ2sNcmLdy
Assalamualaikum
Yar uwa kinason kiga kitchen dinki a cike da kayan amfani masu kyau da inganci amma Kuma kina tunanin chake kudi kisaya a dunkule??
Koda yarinyace Dake da takusa aure kinason kifara Tara mata kayan kitchen??
To damuwarki tazo karshe Yar uwa kinzo inda za'a share Miki hawayenki *ALFAT KITCHENUTENSILS* (Adashen Yar gata), sun shirya tsaf dan ganin sun sama Miki ingantattu Kuma masu kargo Yan zamanin kayan kitchen.
Zaki dinga tura kudinki idan yakai wani minzali saiki karba duk abunda kikeso daide kudinki.
Ba iya nan muka tsayaba, farashin kayanmu daban yake a ko ina.
Dannan link dinnan domin kisamu damar shiga group dinmu don zabar kayanda kikeso da Kuma ganin yadda abubuwan suke kasancewa. Nagode
https://chat.whatsapp.com/D4mOQ8gmKb7EXZ2sNcmLdy
____________________________
"Yaa huda.....yaa huda?" Muryar haneefa ta ratsa kunnuwanta dai dai sanda take kwance qudundune cikin bargonta. Kusan idan bawai dare ne yayi ba hakan ba dabi'arta bace,amma a yanzun yana neman ya zame mata dabi'ar da sabreen ta fara karantar hakan.
Batakai ga ce mata komai ba,don ba abinda ta gani behind kwanciya din da take yawan yi,sai ta barshi kawai a zuwan yanayi ne da yakan sauyawa kowanne dan adam. A yanzu ma gaba daya hankalinta yana kan ayshatu.....ciwonta gaba yake qara yi,ga mika'il a gefe,ga mashkur shima daya sanya wuta da yawa a kanta. Ya'aqoub ne kawai me dan sauqi saboda bai cika zafafawa ba. Dukkansu batason kowa ya subuce mata a daidai wannan lokacin da shirinta ke qara zurfi a kansu,kuma tafi hangen samun nasara da wuri akan mika'il da mashkur,don shi ya'aqoub a yanzu tunaninsa yafi karkata kan yadda zai shawo hankalinta ta aminta ta aureshi,abinda kuma bataga ranar yiwuwarsa ba. Wai mema zata tsinta ne a auren?,bayan tana ganin yadda su mazan suke?,tana ganin kuma yadda matan ke komawa?,ko hanyan aure yanzu mutum yayi mata ai bai qaunarta ballantana ace mata tayi. Duka tsari da halayyar mazan baiyi mata ba ballantana ta cusa kanta a sabgarsu da nufin zama tsakaninta da waninsu zama na din din din?.
Miqewa tayi a dole tana duban haneefa,sai haneefa din ta miqo mata takarda tana cewa
"Wani ne wai a waje yace a baki...." Da sauri ta fiddo mata idanunta waje sanda muryar sabreen wadda ke amsa waya take dosowa cikin dakin. Yadda suka daga kai suka kalleta duka su biyun ya sanyata janye wayar daga kunnenta tana kallonsu
"Lafiya?" Tayi tambayar tana sauya yanayin fuskarta. Wani faduwa gabanta yayi,cikin tsoro tsoro ta girgiza kanta tana qaqalo murmushi tace
"Ba komai.....ina kwance haneefa ta tsoratani,na dauka wani abune da naji tanata tashina". Idanu ta sake zuba mata na daqiqu sannan ta amsata tana zama gefan nata gadon
" Ko bata tsorataki ba dama ai yaci ace kin tashi,an kusa kiran sallah.....uniform dinku nadra ta wanke tunda kin koyi laziness......kije kiyi alwala ki dawo ki kwashe abincin tukunya a flask a wanke sauran abinda ya rage".
"Tom" Ta fadi tana matse takardar a tsakiyar hannunta tare da tunanin yadda zata miqe da takardar ba tare data lura da ita ba,to amma kuma ci gaba da zama dinma tunanin mafita tamkar tana bata damar dora ayar tambaya ne a kanta.
Aljihun skirt dinta ta tuna dashi,cikin dabara ta cusa a ciki,sannan ta zame ta sauko tana gyara inda ta kwanta din,ta daura dankwali saman doguwar sumarta ta juya tana fita a dakin. Dauke idonta tayi daga kan tab dinta ta bita da kallo. Haka kawai ta gagara samun nutsuwa kwanaki biyun nan,duk motsinsu a kan idanunta yake,kuma da gaske tana ganin dan sirkawar wani abu kadan tattare da huda din.
Bandaki kawai ta wuce kai tsaye tana fata da zumudin budewa taga meye a takardar?.
Sai data samu guri cikin toilet din ta zauna sannan ta ciro takardar ta kuma warwareta.
Kaman yadda ta zata shi dinne,sunansa kawai data gani sai bugun zuciyarta ya qaru da kaso hamsin cikin dari.
Yau kwanaki uku kenan,ya rakota daga hanyar makaranta har dab da gidansu kamar yadda ya saba a kowacce rana......tun tana gocewa har ya fara zame mata sabo ba tare da sanin nadra ko haneefa ba wadda yanxun aka banbanta musu lokutan tashi qarfi da yaji ba tare da kowa yasan dalili ba. Ya zame mata kamar abokin rakiya a yanzun.....tun tana dari dari da tsoro har hakan ya fara gushewa daga zuciyarta.
A ranar alhamis tayi matuqar mamaki yadda ya tsaya suna tsaka da tafiya,ya kuma kafeta da idanu
"Lafiya kake?" Ta tambayeshi da mamaki
"Ke kyakkyawa ce" Ya fadi yana jin wutar sha'awarta na ruruwa a ransa tamkar yadda ya dinga jin ta 'yar uwarta. Yana jin kamar ya dauketa a yanzun ya wuce da ita ya aikata abinda ya tanadi aikatawa,saidai kuma bazaiyi haka ba,yanason komai ya kasance a daidai sanda zatafi jin ciwo da radadin da zai iya zama ajalinta,ya kuma tarwatsa farincikin da take musu tattali. Yanason idan ya tashi ya tarwatsata tarwatsewar da ba zata taba dawowa ta gyaru ba ballantans ta koma yadda take.
Idanu ta waro tana dubansa,yadda yake yawan kambata da kurantata ya sanya kusan kullum sai ta kalli madubi......kusan kullum sai ta kalli kanta da kanta taga wannan kyan da yake magana a kai......wannan budurwar da yake yawan kiranta dashi. Tun bata ganin abinda yake fada din har ta fara ganin,amma tana ganin kaman bata ca canci kowacce rayuwa ba a yanzun......karatu shine yafi da cewa dasu kamar yadda yaa sabreen ke gaya musu
"Ina sonki huda.......ina tsananin qaunarki tun daga ranar dana fara ganinki.......zuciyata tana miki wani mahaukacin so da bansan iya adadinsa ba......wallahi inaji a zuciyata tamkar zanyi hauka saboda ke huda......ki soni don Allah......ko baki sona ni zan koya miki yadda zaki soni din". Kalaman da suka tsoratata suka kuma razanata kenan. Kalaman kuma da Naseer din ya shiryasu ne kawai don ya soma wasa da tunaninta da qwaqwalwarta,plan na biyu kenan daga cikin tsarikansa.
Baya taja tana girgiza kai,tana jin tsoro yana shigarta. Wacce irin soyayya a shekarunta?,duka duka nawa take?,koda yaa sabreen bataga ta kawo kowa tace shi zata aura ba,bataga wani yazo qofar gidan da sunan zance wajenta ba.....koda abinda ake maganarshi a kanta da nasu idanun basu taba ganinta cikin motar wani ko tsaye da wani ba har zuwa yanzun da take tsaye a gabansa. Ko rakota da yakeyi kullum kwanan duniya a tsorace take......wani lokaci zuciyarta tana raya mata idan sukayi kacibus da yaa sabreen fa?,sai kuma zaqin bakinsa da daddadar hirarsa ta yaudare tunaninta