Showing 426001 words to 429000 words out of 557259 words

Chapter 143 - πƒπ”ππˆπ˜ATA BOOK1 AND 2 HAUSA NOVEL

HUGUMA   

03 Nov 2025

421

bakinsa ke iyayi banda furta sunanta a jejjere da bada zazzafan kiss da karbar martani daga gareta.

"Ki soni sabbrrrrr......na rantse da Allah ni kadai nasan me nakeji a kanki......ki soni,zan miki komai....zan zame miki komai.....zan mallaka miki komai". Fuskarsa ta riqe sosai cikin hannuwanta tana dubansa,gaba daya kamanninsa sun sauya ya birkice sosai.

"Muhammad" Ta kirashi

"Fu'ad" Ta maimaita

"Muhammad jadda......ameenatu ta yarda ta soka......ameenatu ta yarda ta mallaka maka kanta da rayuwar ta,ameenatu ta zama taka har gaban abada....dakai da ameenatu yanxu duka abu daya ne.......ka gayawa kowa wannan cikin alfahari taqama isa da samun tabbaci"

Ya riga ya sallama,gaba daya ta gama susuta qwaqwalwarshi......yasan a yau kam duk wanda yayi kusa da yawa da dakinsa zai iya jin motsin da xai saka zargi a ransa,baisan me yake yi ba kaman yadda ya manta wayeshi. A lokaci ji ya dinga yi inama akwai wata duniyar ta daban da zai iya maidasu shi da ita?,duniyar da babu kowa saisu kadai?,wannan albishir daya samu daga bakinta......daga gari me tsarki yafi komai masa dadi da zame masa tarihi cikin rayuwarsa.

Wani irin dare suka raya,daren data sakar masa dukka ragamarta,ta cika masa mafarkinsa ta hanyar bashi kowacce gudunmawa da cikakken hadin kai,saiga muhammad fu'ad din yana mata kuka sosai kaman qaramin yaro. Kukan daya sake susutata itama,banda abune da ubangiji ya sanyashi ya zama sirri tsakanin ma'aurata......tabbas duniya data cika da mamaki idan akaga matashin zaki gwarzo irin muhammad jadda yau a gaban mace yana mata kuka har haka.

Ita kanta a rikice take,ta kuma aikatu sosai a hannunsa duk da controlling din kansa daya dinga qoqarin yi,kafin wani lokaci zazzafan zazzabi ya sake rafketa bayan amai data yi a jere har sau uku.

Abinda ya daga hankalinsa kenan,ya tsaftacesu shi da ita,ya kuma shiryata cikin abayarta me sulbi shima ya sanya jallabiiyyarsa,ya duba asibiti mafi kusa ya kirasu donsu dauketa aje a duba masa ita,don bayajin zai iya jure wannan zazzabin yaci gaba da taba masa ita.

Cikin mintuna qalilan motar al_ansar hospital ta iso suka wuce da ita. Baiko samu tsaiwa gaya musu ba,don kiran sallar farko kawai akayi,sai ya rubuta saqo kawai ya turawa Farooq.


*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862




𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀
_Zafafabiyar_

ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2

β±§Ι„β‚²Ι„β‚₯β‚³

π™‹π˜Όπ™‚π™€ 114


114



Ko na second daya bai barta ta matsa daga jikinsa ba,tana kwance cikin jikinsa da wani irin yanayi. Cikin kowanne numfashi da zai sauke ko zai fitar jinsa takeyi da wani irin maqalallen yanayi a cikin zuciyarta,duk bayan minti kadan sai ya tambayeta

"Ina ne kuma yake miki ciwo?,menene yake damunki?,me kikeso?" Ido kawai take lumshewa,don ita kadai tasan me takeji cikin qasusuwanta,saidai tana qoqarin nuna masa all is well saboda ta fahimci a gigice yake,amma duk da haka bataga nutsuwa a tattare dashi ba,kaman me gani har hanji,ya fahimci duk wani motsinta.

Yanayin zazzabin ya sanya suka fara bata taimakon gaggawa a daki na musamman,kafin daga bisani su fara gudanar mata da test har kusan kala biyar suka tafi kan zasu dawo da result din.

Sanda tayi farkawa na biyu bayan tayi sallar asuba gari ya waye sosai,kusan goma saura na safe. Shine mutum na farko data fara gani,fuskarsa ta fito fes yana zaune daga gaban gadonta yana jan tasbaharsa,lokaci lokaci yana duba saqonni a wayarsa.

"Sabahal khair muffin" Cikin ba zata muryarta ta sauka a kunnensa. A nutse ya daga kansa ya sauke mata idanunsa. Itama shi take take kallo da fararen idanunta murmushi na fita daga fuskarta.

"Muffin?......thanks ny world" Ya fadi sunan data bashin yana masa wani mugun dadi.

"Sabahannur......khaifa asbahti?" Ya fada da tataccen larabcin da kana ji zakasan yasan qa'idar kowanne harafi a cikinsa yana nutsa tafin hannunsa cikin nata.

"Asbahatu bikhair walhamdulillah" Ta maida masa da murmushin nan nata data tsinceshi saman fuskarta.

Kansa ya langabe gefe guda kaman wani qaramin yaro,fuskarsa a narke yace mata.

"I'm scared that am going to loose you,i know it's stupid,but i just can't stop thinking about it" Murmushi ta saki tana danjin nauyinsa kadan

"Ka wahalar dani ne kawai......you won't lose me,am not going anywhere in sha Allah". Riqe hannunta yayi sosai cikin nasa.

"That's my wish in sha Allah,you're the most important thing in my life" Sosai maganganunsa suke sake samun mazauni a zuciyarta,maganar amna data taba fada mata ta dawo mata fes akai.

"You're the luckiest woman da kika samu hamma na" A yanzun take sake tabbatar da maganganun amnan,duk da a baya ta qaryata hakan.

"Have your breakfast and then brush your teeth" Idanu tadan bude kadan tana kallonshi kafin ta sauke dubanta kan jerin kayan breakfast din daya jawo gabanta saman dan wani gado.

"Ehnnnn" Ya fada yana dage mata girarsa,ya fahimci akwai abinda takeson fadi.

"Brush din xai zama first ko?" Kai ya girgiza

"No.....Brushing teeth after breakfast helps remove food particles and maintain oral hygiene" Shuru tayi murmushi na qwace mata,ba a banza ba takejin su musaddiq na gulmarsa. Komai nasa yasha banban dana kowa,tsare tsarensa ba irin na mutane bane.

A jikinsa ya ajiyeta,ya dinga qoqarin bata breakfast din amma ta kasa cin komai a ciki. Iya black tea kawai ta dinga kurba,tana sha yana kallon fuskarta yana qarfafa mata gwiwa,a haka tasha rabi da qyar. Saidai tana kammalawa ya dawo duka,ta wankesu tsaf da aman shi da ita.

Hankalinsa tashe ya danna wani guri,qasa da second sha biyar wata nurse ta iso. Zata karbi gyaran wajen ya dakatar da ita da harshen turanci.

"Barmin zan gyara,aman nan da takeyi ne banaso,inaso shima ya tsaya ko ya tafi,ya kamata abinci ya tsaya a cikinta hakanan".

"Likita yana dab da shigowa da dukka result na gwajin da akyi mata,sai a sannan zaa san abinda ya kamata ayi mata,amma yanzun xan sake saka mata ruwa don kada jikinta yayi rauni da yawa".

Yana tsaye a gefe ranshi a jagule ta gama mata komai sannan ta fice,koda ya matso sai ya samu har bacci yayi awon gaba da ita. Ajiyar zuciya ya sauke,yana jin kamar ya dawo da ciwon jikinsa,agogo ya kalla.....yau din juma'a ce,yanason samun sahun gaba gaba a masallacin ma'aiki,duk da zuwa yanzun ma yasan ya makara,baya ga haka akwai wani al'amari me muhimmanci da zai aiwatar a can din,wanda bayajin akwai abinda zai sanyashi jinkirtawa ko dakatawa a wannan ranar ta juma'a. Rana ce mafi dacewa daya aiwatar da al'amarin. Idan yace zai koma gida ya shirya ma ya bata lokaci,don haka ya daga waya kawai ya kira farouq.

"Ka turo saddiq ko musaddiq......ina buqatan Friday attire please".

" Ina kusa da hospital dinma......but bari na koma na duba maka kayan...."

"Thanks dude"

"Don't mention it....ya jikin nata?" Dubansa ya mayar kanta sannan yace

"Alhmdlh....she's sleeping,inaso naje mosque ne na dawo kafin ta farka"

"Zaa kula maka da ita dude....kada ka damu,dukansu na barsu suna shiryawa zasu taho nan"

"Alright" Ya fada a taqaice yana ajiye wayar.

Ba jimawa farouq ya qaraso,dauke da wata leda me kauri. A nan parlor din dakin ya zauna,shi kuma ya wuce ciki inda gadon sabreen din yake.

Cikin qanqanin lokaci ya shirya,Moroccan jallabiyya ce fara tas me asalin tsada me adon gold din zare,sai zagayayyar hular nan irin ta larabawa wadda set ce tare sukazo da hular da loafers din dake ciki iri daya. Wani irin sassanyan kyau ya aje,saika dauka balaraben Morocco dinne,ya matsa inda take kwance tana baccinta kaman ba abinda ke damunta,ya sunkuya yayi kissing dinta sannan ya fara takowa yana fitowa.

Tun bai qaraso parlor din ba yaji muryar farouq dana likitan,yana tsaye sanye da farar lab coat dinsa suna hira sama sama da farouq din. Fuskarsa sake ya miqawa fuad hannu cikin sanin darajar dan adam da iya aiki,shima ya bashi suka gaisa,sannan ya fara bude takardun hannunsa.

"After conducting the necessary tests,I'm pleased to inform you that your wife is pregnant...." Likitan ya fada da murmushi a fuskarsa.

Karon farko da yaji ya koma kaman dan koyo a fannin turanci,kaman ma baya gane komai. Ya zubawa likitan idanu yana buqatar qarin bayani,muryar farouq ta dawo dashi hayyacinsa.

"Alhamdulillah......ya rabb lakalhamd.....alhamdulillah......muna godiya sosai likita" Farouq daya kasa zama ya fada yana kama hannun likitan da kyau ya riqe cikin nasa.

"Allah ya inganta......ya bata lafiya me dorewa.....ina tayaku murna" Abinda likitan ya fada kenan yana murmushi,sannan ya miqawa farouq takardan gwajin yana masa bayani.

"Idan ta tashi a bacci za'a qarasa bata duk wani treatment daya kamata"

"Mun gode" Farouq ya sake maimaitawa yana karbar takardan likitan ya juya ya fice.

Ganin gaba daya fuad din ya zama wani statue ya sanya farouq kai masa duka

"Dude......kayi nasara.....ka jefa qwallonka a raga daidai" Sai a sannan ya tattaro kalaman bakinsa da qyar

"Am going to be a father?" Ya tambayi farouq cikin neman bayani gamsashe.

"Yes dude.....bakai kadai ba,harda ni,anni zata zama grandma for the first time......zamuyi yaro ko yarinya dukanmu......" Bai jira farouq ya kammala ba yayi masa wata wawiyar runguma hawaye suna kubce masa.

"Ya rabba.....antal kareemul lazi ya yaraddu sa'eelan,la'ilaha llla antar rahmanir raheem......shukran ya Allah,shukran" Sai muryarsa ta karye,ya dora fuskarsa saman kafadar farouq kuka nason qwace masa.

"Bansan wannan jarumin muhammadun da saurin kuka ba.....duk da na lura sabreen ta maidashi baby da gaske" Farouq ya fada shima zuciyarsa tana raunana amma yana qoqarin bawa kansa qwarin gwiwa. Kansa y a daga yana riqe farouq da kyau,yanata qoqarin masa magana amma ya kasa,sai kawai ya jijjigashi yana kada kai sannan ya taka da sassarfa yana komawa dakin.

Baccinta take kaman yadda ya fita ya barta,ya sake sumbatarta a goshi da labbanta,a hankali ya furta

"Kece duniyata.....na gode,na gode" Sai ya rufe mata qofar yana komawa parlor din da sauri.

"Zanje nayi sallah masallaci......zan kuma aiwatar da wani abu,idan zakaje mu hadu a hanya" Ya fada yana saka hannu ya kwashe takardun ya zubasu a aljihunsa sannan ya fita da sassarfa bayan ya sanar musu su aika me kula da ita zaije juma'a ya dawo.

Ba inda yakejin ya kamata yaje ya juye farincikinsa da godiyarsa ga Allah irin cikin rauda.....ya godewa Allah daya samu wannan labarin a irin wannan wajen,banda haka ya tabbatar sai yayi qaramin hauka saboda farincikin yayi masa girman da zuciya ba zata iya daukarsa ba ita kadai.


*_BAYAN AWA DAYA DA RABI_*


*_B A Z A T A_*


Anni,amna,musaddiq,saddiq dukkaninsu suna zaune a parlor din dakin asibitin bayan sun shiga sun dubata tana bacci sun fito.

Huda haneefa nadra da kuma momma bahijja sune kadai daga cikin dakin,suna taba tasu hirar kadan kadan wadda ke cike da farincki da qaunar juna.

Maamah dake zaune kallon kowa takeyi kawai daya bayan daya,yanayin yadda taga sabreen a yanzu ya soma sauke mata duk wani qwarin gwiwa da takejin tana dashi akan ba ciki bane a marar sabreen din. A shigarsu ta dazu ta gama qare mata kallo da kyau,ba abinda idanunta suka hango mata kuma banda dashewa irin ta me yaron ciki.

Iya wannan abun kawai data gani ya sanya gumi ya fara yanko mata,duk da yadda zuciyarta keta qarfafata tana mata romon bakan cewa ba ciki bane.

A yau din batajin zata matsa daga asibitin nan ba tare da an gwada yarinyar nan ba anga uban abinda yake damunta ba.

Sake jan qaramin tsaki tayi jan qasa qasa tana gyara zamanta. Gaba daya zaman wajen takeji ya gundireta,daidai lokacin fu'ad ya turo qofar dakin da sallama a bakinsa ya shigo.

Sannu da zuwa dukkaninsu suka fara masa banda maamah dake jifansa da wani irin kallo. Saddiq musaddiq da amna dukka suka gaidashi da tambayar me jiki,ya amsa musu cikin kulawa kafin ya qarasa gabansu anni yana gaidasu.

Da qyar maamah ta amsa,ta bishi da kallo sanda yake miqewa zai wuce ciki

"Zo nan muhammadu" Ta kirashi,sai ya dawo ya samu waje yana zama kujerar dake fuskantarta.

"Wannan ciwon da yaqici yaqi cinyewa ina ganin ya kamata a auna yarinyar nan asan me yake damunta,kada mutane suna zamansu lafiya taje tana yawo da ciwo tana yada ma mutane tunda gata ga yadda take a baya". Sosai maganar maamah ta sokeshi,ya kuma fahimci inda ta sanya gaba,anni kuwa sai da tayi da gaske ta iya controlling kanta.

Idonsa ya lumshe kana ya budesu ya gyara zamansa.

"Ba wani ciwo da ameenatu take dauke dashi a jikinta......tunda nine mutum na farko dana fara karbar mutuncinta na 'ya mace......ciwonta na yanzun kuma nine silarsa.....ga bayanin nan a rubuce" Ya fada yana zaro takardar,sai kuma ya dakata yana dubansu.

"Naji dadin ganinku a tare gaba daya" Ya fadi yana sake zura hannunsa a aljihun rigarsa.

Dollars dubu biyu ya fiddo sabbi kar a miqe,ya miqawa maamah takardar ya kuma miqawa anni kudin.

"Abba......alhaji hamza kibiya ta hannuna ya karbawa musaddiq mahmud jadda auren amna......bisa sadakin dala biyu biyu lakadan ba ajalan ba......ta hannun wakilinsa abokinsa alhaji muhyidden kibiya da tarin shaidu cikin masallacin annabi muhammad SAW,bisa yarjewar waliyyansu ni muhammad fu'ad jadda da kuma abba wato alhaji hamza kibiya"......


TURQASHI!......FU'AD.....NACE ME JADDA?,WANNE IRIN MATCH KA TARO HAKA?,KO TAKARDAR DA MAAMAH TA WARWARE BAKA BARI TA GAMA DUBAWA BA?.

TO NIDAI JAMAA WANNAN FADAN YAFI QARFINA
NAYI NANπŸ˜‚πŸ˜‚πŸƒπŸ½β€β™€οΈπŸƒπŸ½β€β™€οΈπŸƒπŸ½β€β™€οΈπŸƒπŸ½β€β™€οΈπŸƒπŸ½β€β™€οΈ



*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862


𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀
_Zafafabiyar_

ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2

β±§Ι„β‚²Ι„β‚₯β‚³

π™‹π˜Όπ™‚π™€ 115
_____________________________
_kin dade kina cizon yatsa kan yadda ake kacalcala suturun yaranki da dinkuna marasa ma'ana?_

_HUGUMA na miki albishir da wajen zazzafan dinki na MS KIDDIES WEARS,irin dinkunan yaran da kike gani a Instagram TikTok suna burgeki kuma bakisan inda zakikai ayi miki ba ko kina tsoron tsada_

_Zafafan dinki na gayu da ado kiga yaranki sun fita dagwas dagwas_
_ready

_MS KIDDIES na nan kano gwammaja_

*TRUSTED AND TRUSTED mun gwada mun gani*

_Maza tuntubeta a nan_

+234 708 865 2858

Ko Instagram account dinta

https://www.instagram.com/ms_kiddies_wers_by_nafs?igsh=MTljZWQwM2FsaXlxaA==
______________________________


115



Dukkanin wani da yake numfashi a wajen saida jinin jikinsa ya daskare na wucin gadi,qwaqwale da yawa suka dakata da aiki na wasu mintuna,yayin da idanuwa sukayi warwaje a kansa. Kowa dubansa yake d wani irin madaukakin mamaki da tarin ba zata,dukkaninsu kowa kwanyarsa ta kasa fahimta ko sarrafa maganarsa.

"Mem.....me kake cewa fu'ad?" Anni mutum qwaya daya da tayi qarfin halin sake tambayarsa tana jin yadda jinin jikinta uske tsinkewa. A nutse ya dubi annin nashi,yana da qwarin gwiwa da zato me yawa a kanta,don haka kansa tsaye yace.

"Na aurar da amna ga musaddiq cikin masjid nabawi bisa shaidu da wakilai da sadaki dala dubu biyu" Sai a sannan kwanyar wasu daga ciki ta harba ta kuma dawo da aiki,ciki harda amna.

Wani tsananin tsoro taji yana shigarta,ta shige jikin anni tana buya a bayanta gami da cukuikuyeta,idanunta kuma suna sauka kan fuskar maamah. Wannan fuskar da take bata wani tsoro haka kawai,fuskar da batason kallonta saboda duk wani yanayi da alamu na rashin wanzuwar alkhairi tattare da ita tana ganinsu......a yau mamallakiyar wannan fuskar itace a mazaunin surukarta?.

Shi kuwa musaddiq kama hannun saddiq yayi ya riqe da kyau yana qoqarin tuna maganganunsa da hamman masa mintuna ashirin baya da suka wuce kafin ya shigo cikin asibitin. Abubuwa biyu ke masa kai kawo suna gwarabkiya cikin zuciyarsa,farinciki da kuma fargaba da wani sofane na tsoro dan kadan. Kalaman bakin maamah wani irin daci da dafi ne dasu wanda ya kasa sabawa da jinsu,baya qaunar komai ya hadashi da ita alkhairi ko sharri,dadi ko akasinsa.

Idanu kawai anni ta zuba ma fu'ad tana jin tsigar jikinta na tashi. Wanne irin tashin hankali ne haka fu'ad din ya rakito mata tana zaman zamanta tana lallaba tsufanta?. Wacce masifar ce ke shirin wanzuwa?,meye kuma zai afku gaba ga amnanta?.

"Allah ya sanya alkhairi......yasa anyi a sa'a" Lafuzzan suka fita daga bakin maamah da tayi qoqarin ware idanunta daga qanqancesu da tayi.

Ba wanda kalamanta basu bawa mamaki ba.......kaman yadda suka janyo hankalinsu ga fuskarta wadda ta maida idanunta kan takardar hannunta tana qoqarin hana zuciyarta tsananin bugun da takeyi,tare da fatan gumin dake yanko mata ya tsane jikin atamfar jikinta ba tare da kowa ya gani

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login