Showing 120001 words to 123000 words out of 557259 words

Chapter 41 - πƒπ”ππˆπ˜ATA BOOK1 AND 2 HAUSA NOVEL

HUGUMA   

03 Nov 2025

415

Moroccan abaya ne sulbi ya wuce zuwa sallar magariba.

Kafin ya isa masallacin suna hanya shi da farouq musaddiq da saddiq suka biyo bayansu. Wannan din wata kyakkyawar al'adarsu ce da anni ta renesu a kai. Muddin suna garin ko suna qasar,hakanan ba wani babban uzuri ko aiki bane ya riqesu a kamfani,to zaka samesu a gida duk inda magariba tayi. Kwata kwata basusan yawon dare ba,farouq ne ma medan sha'awar fitan daren,to sukan fita jifa jifa su zaga a mota su dawo. A nan zasuyi sallar magariba suyi ishai,suyi dinner tare me uzuru ya wuce nasa uzurin.

Sanda yake sabule tattausan flip flops din qafarsa yace da musaddiq ba tare daya waiwayo ba

"Bayan ishai ku shirya kaida saddiq zamu shiga wajen maamah" Dan kallon yayan nasa kadan yayi,kaman zai magana sai kuma ya fasa ya amsa da to.

Tun bayan magariba ta sallami kowa tare da kafawa kowa sharadi da dokar bataso kowa ya sake tako mata parlor sai gobe idan Allah ya kaimu.

Ta duba doormat din bakin qofar falon yafi sau goma daga zamanta,ta kuma tabbatar komai yana nan intact kamar yadda ya kamata ace ya kasance din,sai ta koma ta zauna tana sauya tashar Tv din zuwa mbc Bollywood bawai don tana jin dadin kallon ko yana burgeta ba,dukkan hankalinta yanzu da nutsuwarta shine takowarsu cikin falon,su zauna kuma su cika cikin su da abinci da abin shan da ta tsumashi ta kuma tanadashi musamman saboda su.


*D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

PAGE 64


Saddiq da musaddiq dinne a gaba shi kuma yana biye dasu a hankali a hankali,hakan ya sanya suka dan masa tazara kadan. Wayar Mika'il yake amsawa,wanda yakeso ya tabbatar komai ya zama daidai zuwa ranar Monday da zai koma office. Yanason ya gabatar masa da dukkan wasu mu'amala na kudi da banking ya samu bayan tafiyar tasa,komai na shige da ficen kudi.

Yana wayar ne amma hankalinsa yana kan saddiq da musaddiq,tamkar 'yan biyu kamar yadda kowa yake musu kallo hatta da makarantun da sukayi. Suna hira abinsu ne cikin wani irin shaquwa da jituwar jini. Malam saidu ne ya bude musu qofan da kanshi,ya rusuna kuma yana miqa masa gaisuwa sai ya gyada masa kai hadi da daga masa hannu saboda wayar da yakeyi din,ya taka a nutse yana bin bayansu.

Dab da zasu isa steps din da zasu sadasu da ainihin falon yaji gabansa yayi wani mummunar faduwa

"Zamu qarasa anjima" Yace da Mika'il a gaggauce yana katse wayar ba tare daya jira amsarsa ba

"Kai saddiq" Ya furta da muryar da taja hankalin maamah dake falon,wadda dama dukkan tunaninta yana fa farfajiyar gidan tana sauraren kowanne motsi.

"Saddiq kuma?" Ta tambayi kanta da kanta a mamakance,sai ta tuna kuma bata da sauran lokacin batawa,don muddin ta bari wani bayan yaran nata ya taka wannan shirin akwai matsala,don haka ta zabura tayi zumbur ta miqe ta kuma nufi bakin qofar falon da sassarfa.

Wancakali tayi da doormat din,ta sanya hannu ta dauke abun da yake qasan,sannan ta finciki tsintsiya dake ajiye a can wani gefe daban ta fara tattara sauran abubuwan da suka rage.

"Kunyi addu'a ne?" Ya fada yana tsaresu da idanu duka su biyun. Juna suka kalla shi da musaddiq din

"Hamma ai daga masallaci muke" Saddiq din ya fada dukkaninsu suna sauke qafafunsu daga saman steps din da suka fara dorawa

"Kuyi addu'a kafin ku shiga.......haka musulunci ya koyar damu,kome zakayi akwai addu'ar da akeyi masa" Ya fadi idanunsa akan musaddiq

"To hamma" Suka fadi sannan suka maida qafafunsu kowa bakinsa yana dan motsawa.

Da kallo ya bisu zuciyarsa cike da wani wasi wasi da baisan daga inda ya samo asali ba. Sosai hankalinsa yana kan musaddiq da ya tabbatar baisan komai akan shirin maamah nason raba tsakaninsu da iyalin alhaji hamza ba. Shi kansa abban baisan komai ba akai,shi daya yake juya maganar tsakanin qirjinsa da zuciyarsa.

Dan ja sukayi suka tsaya sanda suka sameta duqe tana tattare wani abu da basusan meye shi ba. Ta daga kai tana dubansu,wani irin bacin rai ya cika mata zuciya fal.

Ta yaya banda sun raina umarninta zata ce tana buqatar ganinsu su biyu su rakito mata wani?. Fushin yanason yayi galaba a kanta amma tanata qoqarin danneshi. Yanzun ba lokacin nuna fushi bane ko fada..... Lokaci ne na sauke kai da maida komai ba komai ba muddin nasara take da buqata,wannan shine abinda hajja ta gaya mata.

Dole ta qirqiro murmushi tana cewa cikin nuna kulawa a garesu gaba daya

"Maraba da 'yan samari na" Saita zubda abun cikin kwandon shara ta kuma taka zuwa ciki tana fadin

"Ku qaraso mana". Sai da suka fara shiga sannan yabi bayansu yana kula da hagu da damansu

"Ina ma'aikatan suka barki kina shara?" Fuad ya furta da nutsatsiyar muryarshin nan yana zama hannun kujera hannunsa goye a qirjinsa yana kuma qoqarin karantar komai dama motsin komai dake a falon.

Dan murmushi ta saki tana zama saman daya daga cikin kujerun alfarma dake falon

"Ina buqatar kebewa da 'ya'yana,nayi sirri dasu irin na uwa da 'ya'yanta,shi yasa na sallamesu yau da wuri". Maganar tata sai ta kasance kamar ta jefi tsuntsu biyu ne da dutse guda,don haka saddiq sai ya rusuna kawai yana gaidata.

"Lafiya alhamdlh saddiq......ya mutanen gidan?"

"Suna lafiya maamah"

"Ma sha Allah,don Allah kace ina gaidata da kyau da kyau"

"Zataji in sha Allah......hamma zan qarasa,saikun fito" Idanu fuad din ya zube masa,yayin da maamah ta bata fuska tana cewa

"Ina kuma zaka daga shigowarku ko zama bakayi ba?". Dan murmushi yayi yana saukar da kansa qasa cikin girmamawa

"Gida zan qarasa,jibi zamu koma company ban kuma gama shiryawa ba,kinsan kuma hamma......bazai dagan qafa ba idan aka samu kuskure" Tabe baki tayi kadan ta yadda ba lallai bane su fuskanta,qasan zuciyarta kuma cike fal da baqinciki da bacin rai,amma kuma a fili saita saki murmushi

"Gaskiya ne,to Allah ya taimaka,ka gaisheta"

"In sha Allah" Ya fadi yana waiwayawa gefan musaddiq ya bashi hannu yadda suka saba yana yin gaba.

Shiru falon ya dauka sanda saddiq ke ficewa,cikin ranta take gayawa kanta da kanta saura kadan komai yazo qarshe.... .watan watarana saidai ya gifta katangun kamfanin ya ratse ya wuce ta bayansu,komai na wata dama ta shiga cikin kamfanin baida ita.

Sai daya kammala ficewa tsaf sannan ta maida dubanta garesu,dukansu ta fahimci kamar hankalinsu baya tare da ita,don haka ta danyi gyaran murya,gyaran muryar daya sanya dukansu suka dubeta,sai ta saki musu murmushi.

Amsa gaisuwarsu dukka su biyun tayi,a yau sai take jinta kamar a aljannar duniya,sai takejin kamar burinta ya gama cika duk da an samu matsala a karon farko,amma akwai tafiya ta gaba,ta tabbatar ba zasu tsallakewa abincinta ba.

Tanaso a yau tasan abubuwa masu yawa game da rayuwarsu,tanason tasan adadi da zurfin dukiyar da kowannensu ya mallaka,koda batasan duka ba,tanason ta karanci kaso me tsoka.

"Ina fata dukkaninku kuna lafiya"

"Alhamdulillah" Suka fada kusan a tare kowa ba karsashi a tattare dashi.

Ta fahimci hakan,don haka ta gyara zamanta tana fadada fara'ar fuskarta

"Ina fatan zaku cire komai daga zuciyarku,kuci gaba da kallona a matsayin mahaifiyarku,komai zai wuce mu fara gina sabuwar rayuwa tsakanina daku.....ina buqatar 'ya'yana a kusa dani kamar yadda kowacce uwa take da buqatar 'ya'yanta. Inaso na kasance daku tamkar komai bai faru ba,nayi alqawarin baku farinciki da kariya kaman yadda kowacce uwa ke bawa 'ya'yanta" Ta qarashe maganar cikin matuqar raunin zuciya da karyewar murya kamar wadda ke shirin sakin kuka.

Dukkaninsu dubanta suke,kowannensu da mabanbancin feeling a zuciyarsa,saidai kuma dukkaninsu akwai mamaki danqare qasan ransa.

Ci gaba da dubanta fu'ad yayi mamakinsa yana qaruwa. Tunda ta fara magana baiji inda tace tayi nadama ba......nadama koda qwaya daya akan abinda ta yiwa abbansu ba,su din basu da buqatar ta nema yafiya ko afuwarsu,tunda itace ta haifesu,tayi silar kowasu duniya.....ba wani abu da zasuyi mata wanda zasu saka mata da iya wannan aikin......amma kuma abban fa?,kota manta cewa itace silar komai?,ta manta itace silar faruwar komai?. A yanzun ya Fatimid tafi buqatar hankalunsu a kanta da abinda suka mallaka sama da nadama neman afuwa ta zahiri da yafiya daga mutumin da aka zalunta wanda yanzu haka yake kwance a qarqashin qasa.

"Banaso ku dinga nesa dani suka nesanta kanku dani,bani da wani abu dana mallaka a yanzu sama daku.......ina zaune ni kadai,idan mutuwa ma nayi kenan saidai kuji labari daga wajen bare?" Ta maida tambayar kan fuskar musaddiq. Kanshi ya girgiza mata yana sauke kan nasa qasa. Har yanzu idanunsa da sauran tunaninsa sun kasa goge masa komai,ballantana hammansa daya tabbata komai yana rubuce ne a allon zuciyarsa. A duk sanda ya kalleta sai ya tuna ruwan data watsa saman fuskar majinyacin mahaifinsu sanda ya buqaci ta bashi ruwa,shine ya zame masa rumfa yaje ya kwanta a samanshi da zummar kareshi saboda sanyi da yadda ya jiqe din sosai,a sannan ta taka ta fice a dakin hankalinta kwance tana waqe waqe abinta.

"Don Allah koda abincin dare ne ku kasance tare dani ko na safe... Ku bani koda awa daya kowacce rana mu zauna ni daku nasan na haifi 'ya'ya nima kamar kowacce uwa.....don Allah" Ta sake fada da muryar roqo sosai,raunanniyar muryar daka iya sauko da tausayi a zuciyar wanda baisan manufar me magana ba.

"In sha Alla" Kawai fu'ad din ya furta. Ya sani koma me zaice yanzu ba maslaha zai kawo ba,ba kuma zata taba fahimta tunda akwai banbancin manufa a tsakaninsu. Kowanne a cikinsu abinda ya ajjiye a zuciyarsa daban.

"Muje ga abincin dare can na shirya muku.....abinda nasan kunfi so sosai" Ta fada tana murmushi ranta yana mata dadi da yadda suka karbi request dinta suka amince da xuwan nasu.

Ba wanda ya musa mata,suna dai binta da ido da kuma hankulansu har xuwa sanda ta jawa kowannensu kujerar zama tana fadin

"Bismillah" Inda ta kasance daga kujerar dake facing dinsu.

Serving nasu komai da komai tayi,tana yi tana jansu da hira tare da qoqarin tuna musu wani abu na daga quruciyarsu. Shidai fu'ad idanu ne kawai nashi ba tare daya iya maida komai ba,har ta kammala tana fadin

"Gashinan kowa ya dauki nasa". Duban abincin yayi da kyau,gaskiya ta fada batayi kuskure ba,a baya baida abincin da yakeso irinsa,amma tun daga ranar data dafa abincin cikin gidansu,ta kuma yiwa mahaifinsu haramiyar abincin a sanda yake kwance yana jinya.....yunwa take sake take rawa wajen galabaitar dashi,ta hana masa abincin,abinda yayi silar kwanansa da yunwa,tun daga ranar har kawo yau bai sake saka irin abincin a bakinsa ba,daga ranar ya fita a ransa,fita ta har abada wadda har yau bai sake dawowa zuciya da rayuwarsa ba.

"Shikam hamma ai maamah yanzun wannan ba cimarsa bane......nima kuma kin manta dama ba kasafai na fiya ci din ba?" Musaddiq ya fada yana shafa kanshi idanunsa cikin na maamah din.


*D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

PAGE 65



Wani abu ne yaso ya tsaye mata a rai,tunzura takeso tayi amma kuma tana gayawa kanta ba yanzu ba......idan ma basuci na yau ba ai na gobe yana nan,muddin kuma zasu ci gaba da taka qafarsu cikin gidan yau ko gobe nasara tana nan tare da ita.

"Yaushe Muhammad ya daina ci?" Ta yiwa musaddiq tambayar sai kuma ta maida dubanta ga fuskar fu'ad din a mamakance,saidai kuma sanda suka hada idanu dashi sai komai daya faru a wancan ranar ya dawo mata a take,amsar tambayarta ta fita kamar budewar shafukan littafi.

Wani abu taji me nauyi wanda sam baiyi kama da kunya ko nadama ba,tabbas a baya din don ba cikin daidanta take ba.....ba yaran bane a gabanta ballantana abinda ya shafesu da har zata lura da meye ya damesu da wanda bai damesu ba.....amma tabbas sai yanzu ta tuna,tun daga ranar yake bar mata kwanonta gaba daya yadda ta zuba.

"To amma bai kamata ace bakuci komai ba koda lemo ne" Ta sake fadi tana jan jug din gabanta tare da qoqarin raba kofunan ta zuba musun kada ya zamana komai da komai ma tayi asararsa a yau din.

Idonsa still a kanta,ya miqa hannu ya jawo gorar ruwan daya tabbatar a kulle take ya soma budeta,qarar budewar ya sanya ta daga kanta zuwa gareshi tana dubansa

"Ruwa kuma muhammadu?,ga lemo dai" Ta fada tana tura masa wanda ta zuba

"Maamah dare ya soma yi.....idan kuma dare ya fara bana iya cin komai...." Dubansa ta sakeyi kadan sai kuma ta dauke kanta tana qirqiro murmushi

"Kowa time table zai bani na abinda yakeso yaci kullum har sati guda koma sati biyu.....masu girki na musamman zan ajiye muku.....burina naga kun kusanta dani......na maida tsohuwar alaqar dake a tsakaninmu" Ta qarasa maganar tana duban cikin idanunsu.

"Fu'ad" Ta sake kiran sunansa,ya daga fararen idanunsa da suka fara rusuna saboda gajiya da zama a wajen,sam baya jinsa comfortable sam sam

"Me yasa kabar musaddiq tare da farouq......duk da ba laifi bane.....amma kaman zaifi cancanta ya kasance tare dakai qarqashin naka kamfanin" Shuru ya biyo baya na second uku,sai ya maida idanunsa ya kulle yana jan boyayyen numfashi. Shikam yayi imanin ba zata canza ba,ya tabbatar abune me wahala da girman gaske da zai sauya mata hali farat daya. Wannan ya sanya kowanne taku ko motsi nata yake sanya masa ayar tambaya,wani lokaci idan tayi wani move din sai yaji gaba daya kanshi ya juye yana tambayar kansa anya da gaske maamah din itace uwa ta asali a garesu?.

"Kowanne bawa da abinda yafi shaawar yi yafi qwarewa a rayuwarsa......yadda abba ya ginemu shine kowa ya dauki zabinsa da ra'ayinsa a rayuwa muddin bai kaucewa hanya ba....inda kikaga farouq da musaddiq su suka zabi wannan sashen duk kuwa da cewa tare da farouq mukayi gwagwarmayar samar da abinda na gina din a yanzu.....ba wanda ya zaba masa ko ya tursashi gashinan maamah ki tambayeshi" Juyawa tayi tana duban musaddiq ranta duka a jagule,bata son kowa ya rabi fu'ad a duniya idan ba dan uwanshi ba,batason kowa yasan sirrin dukiyarsa idan zaiyuwu sai ita daya,wannan tunanin ya sanya ta yanke shawarar sanya ido me tsananin a alaqar fu'ad din da amna......don ba zata taba yarda amina ta dauki d'iyarta ta qwaquma masa ba su qarasa nadeshi.

"Shikenan,Allah ya taimaka" Ta fadi tana sauke numfashi bawai don ta haqura a zuciyarta ba. Kawai tana ganin tunda komai yana kan turba bai kamata ta bata lokacinta tana dogon zance dasu ba,lokaci kadan take jira ta soma bada umarnin wanda zai shiga ko ya fita daga rayuwarsu.

"To yaya sunan surukar tamu musaddiq?....koda wasa baka taba attempting kawota ta gaida mamarka ba?" Ta yiwa musaddiq tambayar tana dubansa da murmushi,cike da zaquwa da son jin kalar matan da suke shirin kawowa rayuwarsu. Wani babbab abu da yake cikin tsarin abubuwan da takeso ta yiwa garambawul idan damar da take tsimayi ta samu,tanason surukanta su zama qarqashin ikonta fiye da yadda hajja ke juya nata mulkin a gidan.

Murmushi kadan ya saki,karon farko da yaji 'yar kunyarta ta sauko masa

"Minal bata iya zuwa ko ina,daga makaranta sai gida.....zata zo wataran in sha Allah". Ba haka takeson ji ba,don haka ta gyara zamanta tana sake sakin fuskarta

"Aah wataran yaushe kenan?,ina buqatar ganinta mu tattauna ka shaida mata mamarta nason ganinta......" Ta fadi din don da gaske tanason ganin wace ita?. Zuwan nata kuma a nan ne zata samu amsoshin tambayoyib data tabbatar ba zata samesu daga bakin musaddiq ba.

"In sha Allah" Ya fadi a taqaice yana auna yadda abun zai kasance.

"Kai kuma fa?" Ta waiwaya tana duban fu'ad daya tattara hankalinsa duka saman wayarsa tamkar ma baya jin abinda suke fadi. Gajiyayyun idanunsa dinnan ya daga ya kalleta,sai kuma ya maida dubansa ga musaddiq. Kan musaddiq din a qasa yana satar kallon fu'ad din ta qasan idanunsa,boyayyan murmushi nason qwace masa.

"Me maamah?" Ya tambayeta da sautin muryarsa da tayi laushi sosai.

"Wa ka daukomin a matsayin suruka?" Ta sake maimaita tambayar tata.

"Babu fa maamah...." Musaddiq ya fadi muryarsa na nuna murmushin da ya boye.

Debe kallonta kacokam tayi ta maida kan musaddiq tanason sake samun tabbacin hakan

"Kamar yaya kenan?" Satar kallon fu'ad yayi sannan ya dubi maamah,yayi qasa sosai da muryarsa,duk da yasan dole ya jishi don yana da wannan baiwar ta kaifin ji

"Ba wata budurwa.....tsoronsa ma suke......ba wadda take iya tararsa maamah tace tana sonshi"

"Very good" Ta fada qasan zuciyarta. Tsananin farincikin da taji ya bayyana har saman fuskarta,tadan danne tana hada rai

"Garin yaya?.....har yanzu halinka dinnan bai canza ba?" Ta watsa masa tambayar . Karon farko kenan da magana kwatankwacin wannan ta taba hadasu,don haka ya

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login