Showing 489001 words to 492000 words out of 557259 words
yazo mata da nasara ba a karon farko ba sai wannan.
"Komai kakeso zaka sameshi tunda har ka cikamin muradin raina,iya wannan nasarar daka tabbatarmin ta isheni farinciki......wannan yarinyar dake hannunku kadara ce.....kadara ce me girman gaske,kada kuyi wasa da ita har sai kun samu abinda kuke nema"
"Na sani hajiya,daga adadin abinda muka fara tambaya kuma muka samu tabbacin samunsu nasan munyi babban kamu,munyi kuma babban aikin da zamu fita daga talauci har abada".
"Qwarai da gaske" Ta fada tana jinjina kai.
"Ina yarinyar take?" Ta buqata ganin amna,ba bata lokaci ya juya kiran video call ya kuma haska masa amnar.
Tana ya she tun sanda suka sheqa mata abun bata dawo hayyacinta ba. Baki ta tabe
"Wai wannan abarce zata cakuda jinina da nasu?....kuci gaba da aliyarta.....tabbas sai na sanya sunyi nadamar hada hanya dani da kuma sanina koda sau daya ne a rayuwarsu" Ta fadi tana dauke idonta daga kallon amna.
Kiran ta katse tana sake murmusawa,idanunta kan farfajiyar gidanta.
"Wannan wasan zaiyi dadin kallo.....zan samu farinciki matuqa idan naje idanuna suka ganemin jigatar da ahalin alhj hamza sukayi tsakanin jiya shekaran jiya da yau" Ta fadi a ranta,sai kawai ta fada wanka.
A nutse ta shirya cikin qasaitaccen lace,lace ne na alfarma da ita kanta a jininta tasan ba qananun kudade fu'ad ya sanya ya siya mata shi ba.
Laluba ma'ajiyar sarqunanta tayi,duka gold sun qare sai fashions masu tsada. Su ta sauko ta zuba tsakanin hannuwanta wuyanta da kuma kunnenta,ta bade jikinta da turare,ta kuma dauko tsadajjen mayafinta mahadin lace din ta yafa.
Tunda tazo gidan taga yadda anni da musaddiq ke a birkice idanunta basu huta da zubda hawaye ba,ba iyasu ba.....hatta saddiq dimma da hudan gaba daya. Sak gidan ya koma musu kaman gidan makoki,sauqin abun daya duk an sallami kowanne baqo ba tare da an bari ya fahimci komai ba.
Duk yadda anni keji daga qarshe ita ta koma lallashin sabreen,wani irin abu takeji daya kasa tsarga mata,qaqqarfan zato da zargi maras iyaka dake mata kai kawo,wanda tayi imanin wannan karon komai ya kawo qarshe muddin ya tabbata abinda take zato dinne.
Cikin isa da izza take takawa zuwa ainihin babbar qofar parlor din. Iska take zuqa sosai d'ai d'ai tana fesarwa. A yau jin kanta dama duniyarta sabuwa takeyi,a haka ta isa qofar falon annin ta turata ta shiga tana rangada sallama da muryarta data fita fes.
Sabreen ce mutum ta farko data fara daga idanunta ta kalleta,fes ta zube mata kallonta sanda maamah din ke takowa zuwa cikin parlor din.
Kasa motsa bakinta tayi bare ta amsa mata sallamar,sai idanunta da suka zuzzurma saboda kuka data kafeta dasu.
Anni wadda ke zaune saman abun sallah bayan ta idar ce ta daga idanunta tana amsa sallamar.
A mamakance anni take duban maamah dake takowa parlor din,ci gaba da dubanta anni takeyi haka kawai tana jin wani yanayi daban yana shigarta game da maamahn.
*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
π π π π π π π π
_Zafafabiyar_
ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2
β±§Ιβ²Ιβ₯β³
ππΌππ 146
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
146
Murmushi ta saki tana sake takowa da wani irin qarfi da conference,laushin da take gani iya idanuwansu da fuskokinsu wani nishadi yake bata.
"Barkanku da wannan lokaci" Maamah ta fadi tana yiwa kanta da kanta wajen zama gami da harde qafafunta guri guda.
Idanu anni ta sake binta dashi,tana so tace mata ta tashi ta fita idan ba alkhairi tazo dashi ba,tana so tace mata ta fita salin alin bata buqatar dogon magana,tanaso ta gaya mata ta nesanta fuskarta daga garesu muddin ba zaman lafiya ya shigo da ita ba......saidai kuma shi wanda bai sonka,ba'a ko yaushe ba,ba kuma a kowanne lokaci bane kake bashi daman da zai fahimci wani yanayi da kake ciki na matsatsi ko tashin hankali ba.
"Mun yini lafiya ameenatu?,ya taro kuma ya tashi?" Maamah tayi maganar data bawa anni mamaki sosai.
"Lafiya alhmdlh" Anni ta furta tana tsareta da idanu. Wannan sauyawar yanayin daga Mariya baiyi mata ba,wannan sanyin da nuna kirkin gaisuwar bai gamsheta ba sam sam.
"To ai haka akeso,yayi kyau....Allah ya maimaita.....nace ba fada me ya kawo gaba ameena?,ina cewa duk tsiya dai nice mahaifiyar musaddiq,har abada kuma tuwo sunansa tuwo,babu me canza masa suna......ace an tashi bikin d'ana na ciki na amma bani da masaniya?,haba ameena,son kan naki ai yayi yawa,ko a 'yan Allah ya sanya alkhairi ai nazo ko?". Idanu anni ta dauke tana maidawa wani guri. Ko daya bata tsinci wani abu me ma'ana a cikin zantukan maamah ba,hasalima ciwon kai kawai zasu qara mata ba wani abu ba.
"Yanzunma bata baci ba.....baki kuma makara ba" Annin kawai tace da maamah.
Wani murmushi maamah ta saki tana dan doka hannunta saman kujera,a nutse sabreen ta sake kai dubanta wajen tana aje wata qatuwar ayar tambaya a kai,sai kuma ta sake maida dubanta ga maamah din.
"To Allah dai ya kyauta,amma ko don gaba ya kamata a dinga sanin matsayin kowa".
"Idan kin gama zaman don Allah mariya in zaki fita ki rufe qofar parlor din" Anni da takejin ba zata iya ci gaba da zama tana sauraren soki burutsun maamah ba ta fada,don bata da juriyar zama sauraren nata a yau.
"Kwantar da hankalinki ameena......tafiyar zanyi don banga alamun ana maraba dani ba.....amma na miki uziri,duk da cewa idan naqi fita a gidanma banyi kuskure ba,wanda ya gina gidan daga jikin mariya aka ciri halittarsa ya zama gudan mutum abun mora a yanzu" Ta fada tana sake hakimcewa alamunta suna nuna bawai tafiya zatayi yanzu yanzu ba kaman yadda tace.
Ko sau daya anni bata waiwayeta ba,ta dauki abun sallarta tana wucewa ciki.
Daga yadda take bin anni da kallo tana sake sakin faffadan murmushi ya isa ya gaya maka cewa batasan da wani mutum daban cikin falon ba. Wani abu daya sake qarfafawa sabreen dukka wani zargi da tunaninta a kanta.
"Dariyarku takan zam kuka gaba,da nadamar me qin gaskiya......" Furucin da ya fusgi hankalinta kenan,ta maida dubanta sashen da sabreen ke hakimce qafa daya saman daya.
Wani zazzafan duba take binta dashi,wani mayunwacin kallo me dauke da tarin ma'anoni,wani irin kallo dake da wani irin zafi.....kallo ne na kota kwana,kallo ne na ko a mutu ko ayi rai da wadannan fitattun idanun nata masu zafi da basu da sauqi ko kadan.
Kallo kallo akayi tsakaninsu na wani mintuna,cikin jinin jikinta maamahn ke jin bata aminta da wannan kallon ba. Wani kallo ne da tafi kowa saninsa......tafi kowa kuma sanin ma'anarsa......tafi kowa kuma fahimtar yaren dake cikinsa.
"Akwai wani yare da ba kowa yake fahimtar sa ba sai me matsanancin hankali......akwai wani juyi da idan ya tashi juyawa yake watsi da dukka wani abu dake kusa dashi ko nesa dashi ma......." Ta fada tana juya idanunta sannan ta sake maidasu ga maamah
"Na jima ina gurnani......na dade ina gargadi.....na dauki lokaci inata jirwaye me kama da wanka......amma inajin cewa lokacin yin wankan gaba daya yazo don a batad da sahun wannan jirwayen.....jirwayen dake cutar da farar tufa yake nakasa kuma lafiyar jiki......gargadi na qarshe da bazan sake irinsa ba.....saidai fallasa ya biyo baya.....ruwan kura ne ta fiddo ajiyayyen naman data aje....don kuwa yafi qarfin bakinta,kalar nama ne da bai ciyuwa a gareta kasancewarsa me dauke da wata babbar guba.....a wannan karon lokutan bada damar gaba daya awa biyu ne kacal....do or die" Tsam ta miqe daga kujerar da take kai still idanunta akan maamah da wani zazzafan kallo tana wucewa ciki itama.
Haka kawai kowacce gaba ta jikinta tayi wani irin sanyi,bugun zuciyarta ya dinga qaruwa da wani tsoro da batasan daga inda yake ba.
"Kada fa maganganunsa su tabbata.....kada fa lokacin da yake maimaitamin ne yazo" Take fadi a Karan kanta tana jin wani irin razanannen yanayi yana ratsata.
Fes maganganunsa suke ratsata kaman a sannan yake furta mata su,tsoro ta sakejin ya saukar mata,ta miqe da zummar barin falon sai taji jikinta ko ina ya dauki rawa. Qoqarin daidaita kanta takeyi,batasan wacce irin matsoraciya ta koma har haka ba,batasan dalilin da ya sanya take yawan samun rawar jiki ba idan tashin hankali ya durfafeta(badai.baki yarda baki da hawan jini ba?).
"Ita din ba komai bace.....ba zata iya aikata komai ba don bata da hujja" Abinda zuciyarta ta shiga maimaita mata kenan,abinda kuma yadan bata nutsuwa 'yar kadan,saidai ta gaza samun irin nutsuwar da take da buqatar samu.
K'arfe goma na dare daidai take takawa a harabar gidan tana nufar motar da fu'ad ke zaune a ciki yana jiran ta qarasl su wuce gida.
Ta madubi ya hangeta,sai ya ajiye wayarsa da system din daya wuni dasu yana aiki ya bude motara a nutse ya fito ya bude mata qofar yana jiran ta qaraso.
Tun bata qaraso din ba ya karanci baqon yanayi a tare da ita,yadda yasan sabreen dinsa ba haka take ba,duk da yasan dole akwai damuwa da dukkaninsu suke a cikinta,
Baice komai da ita ba har ta qaraso,ta shiga ta zauna ba tare da tace masa komai ba,wannan ma ya bashi mamaki,don komai runtsi.ba haka ta saba yi masa ba,sai ya rufe ya zagaya ya shiga yana bada umarnin tashin motar.
Hannunsa ya miqa mata,ta dubeshi sau daya ta miqa masa nata,sai ya jawota jikinsa ya rungumeta sosai yana sauke ajiyar zuciya.
"Ina cikin matsi da tsanani sabrrrr,bana cikin nutsuwata da walwalata.....please karki bari ki wanzu cikin damuwar nan kema,domin ke kadai ce kika ragemin da zan samu sassauci da ita". Tausayinsa yayi tsananin tsarga mata,yana tare da abu mafi hadari da muni ba tare da ya sani ba.....yana tare da halitta mafi zamewa rayuwarsa barazana ba tare da yasan da hakan ba.
"Zamu kasance tare cikin tsanani da sauqi......zan zame maka garkuwa alqawari ne wannan,your battle is my battle.....we fight together".ta qarasa fada tana matse hannunsa da kyau cikin nata. Sosai maganarta ta sake bashi nutsuwa,yadda ta sakashi a jikinta tana qoqarin bashi dumi daga dumin jikinta ya tattaro hankalinsa dake son kaduwa waje daya.
"Thank you duniyata" Maganarsa ta qarshe kenan shuru ya biyo baya.
Samansa kawai suka haura shi da ita,don gaba dayansu ba wani me cikakken kuzari. Yana ajiye wayoyin da yaketa dakonsu tun kiran jiya wayar farouq ta sake kadawa. Da wani hanzari yakai dubansa ga wayar. Number jiya ce,don already ya riga yayi marking nata,da wani irin zafin nama ya jona komai yana qoqarin turawa team dinsa saqon kartakwana don buqatar kasancewarsu dashi koma saman minotti sofa dinsa ya zauna yana aza kafatanin hankalinsa akan komai. A hankali ta samu kanta da dawowa da baya,ta samu hannun sofa din da yake kai ta zauna tana jin 'ya'yan cikinta suna curewa waje daya.
"Mun sake kiranka a karo na biyu,kiran kuma da ba lallai muyi na uku ba,zamu gaya maka inda zaka ajiye mana wannan kudin....."
"Ni kuma a ina zan karbi qanwata?" Ya tambayesu muryarsa a tsaye. Ya gama shirya komai,a yanzun bawai lallabawa yake buqatar yayi musu ba,ko na bayan dama akwai gacin da yaso ya cimma shi yasa ya biyo ta sigar lallami,a yanzun kuwa dole ya canza hannu ya gani ko zai samu kaiwa ga wannan matakin.
"Au maganar karbar qanwarka ma kakeyi?.....muna maka maganar kudin aikinmu?".
"Wanne aiki kenan kukayi?" Ya tambayesu cikin salon rainin hankalin da yana sane ya tsiro dashi.
"Lallai kana buqatar mutuwar qanwarka a wulaqance kenan a hannunmu".
"Da na sanya kunyi nadamar haihuwarku da iyayenku sukayi,dana sanya kun gane duniya sashe biyu gareta". Shuru ya ratsa tsakani kafin yaji an danqaro ashar
"Kuna tunani kuna da qarfin kudin da zaku iya kamamu ko?,to zamu nuna muku kudinku bai isa ya saka muzo hannu ba.....don ita kanta wadda ta bamu aikin me kudin kanta ce....kuma tana da nata ikon da ko kamamu kukayi din a dole zaku sakemu".
"Au Allah?,amma ta kasa baku kudi wadatattun da zaku rayu?,saita hadaku da aikin wahala aikin kidnapping?".
"Bayau muka fara mata aiki ba.....kuma wannan bazai zama na qarshe ba,ko ta bamu ko bata bamu ba sana'a mukeyi,kuma ba zamu fasa ba...koda ita ko babu".
"Koda ita ko babu din kuwa daga wannan karon ba zaku sake zaluntar kowa ba.....daga wannan lokacin kun daina aikin ashshsha"
"Kaga dakata malam!" Ya daka tsawa daga daya bangaren,tsawar da har sai data sanya fuad lumshe idonsa sannan ya budeshi,yana ji a ransa inama ce gaba da gaba suke da wadannan qananun 'yan iskan.
"Bama doguwar hira da kowa faruqu kake ko wa?,kuma ba zamu fara a kanka ba.......ka kawo kudi ko qarawa qanwarka tsahon kwana....ko kaqi muyi kaca kaca da namanta kaman yadda hajiyarmu ta buqata daga nan zuwa wayewar gari"
"Kuyi duk yadda kukeso" Ya fadi yana tsinke kiran don ya kwashi mintunan da yakeso.
*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
π π π π π π π π
_Zafafabiyar_
ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2
β±§Ιβ²Ιβ₯β³
ππΌππ 147
*_Bgawo's KITCHEN AND APHRODISIAC_*
*_WATA KILLATACCIYAR MASARAUTA CE,WADDA KE QUNSHE DA DUKKAN NAU'IKAN ABINDA KUKESO_*
*_GIRKE GIRKE NA ZAMANI_*
*_KAYAN MAQULASHE DA NAU'IKAN DRINKS KALA KALA_*
*_INGANTATTUN TSUMAMMUN MAGUNGUNAN GYARAN MUTUNCIN 'YA MACE......GYARA IRIN NA IYAYE DA KAKANNI DA INGANTATTUN MAGUNGUNAN DA BABU DUNGUSHE KO KOKWANTO A KANSU_*
*_KALAR MAGUNGUNAN DA SAO WAJEN IYAYENMU NA DAURI.....INGANTATTUN SAUWOYI DA SAQE SAQI DA AKA SARRAFASU ZUWA MAGANIN GYARAN DIYA MACE_*
*_BIKI KUKE DASHI KO SUNA?_*
*_SAUKAR KARATUN QUR'ANI?_*
*_KO KUMA WALIMAR AURE QARIN MATSAYI A GURIN AIKI KO KUMA WANI QWAR QWARYAN TARO?_*
*_KO YAU DIN BAKIJIN SHIGA KITCHEN?,TSAFTATACCE KUMA INGANTACCEN ABINCI KIKE BUQATA A CIKIN WARMERS DINKI KO FOOD FLASK?_*
*_HAIHUWA KIKAYI?_*
*_KO GYARA ZAKIYI KAWAI A MATSAYINKI MA CIKAKKIYAR MACE?_*
*_BGAWO'S KITCHEN SHINE MUHALLIN DAYA DACE DA DUKKA WADANNAN BUQATUN NAKU_*
_Maza garzaya ki tuntubesu ta wannan number wayar_
08104553105
08127084190
*_zaki godemin qwarai da haduwa da BGAWO'S KITCHEN_*
*_BGAWO'S KITCHEN_*
*MATATTARAR BIYAN BUQATUNKU*
147
"Ya zakace musu haka?,ya zakayi haka hamma?" Sabreen data barke da kuka cikin rawar jiki ta furta,sabreen din da baisan da zamanta a wajen ba sai a sannan.
"Ba zasu aikata ba.....kudi sukeso,sunsan kuma kudi ba zasu karbu ba muddin suka tabata......sai hajiyar da....." Cak ya dakata da maganar yana nanata sunan hajiyarsu da suke fadi.
"Hajiyarsu.....kasan wacece hajiyarsu?" Sabreen ta fada tana miqewa tsaye cikin wani birkitaccen yanayi. Gaba daya ji takeyi tayi loosing duk wani control nata da tunaninta......tana jin komai yazo qarshe,komai yazo gaba.....tana jin ko na minti daya ba zata sake iya ci gaba da rufe sirrin matar nan ba,duk wani signal ya kama ya kuma nuna kanshi......sannan ya bayyanar da komai da komai.
"Nace kasan wace hajiya suke magana akai?" Ta maimaita tana ware hannayenta gami da fiddo idanunta waje kaman wadda ta zare. Bata jira amsarsa ba ta dora.
"Ba kowa bace sai MAAMAH!" ta fada da wata irin tsawa da bata tashi tarwatsewa ba sai a tsakiyar kunnen fuad da wani irin nau'in mafi munin sauti.
Idanunsa da yakejin sun masa nauyi ya aza akan fuskar sabreen da wasu manya manyan alamun tambaya a kansu.
"Maamah?" Ya maimaita sunan da salon tambaya.
"Eh maamah.......maamah itce ya dauke amna.....maamah ita ta saka a dauke amnah!" Ta sake fada kuka me qarfi yana kubuce mata.
Daga zaune da yake amma sai yaji kaman duniya tana zpagayawa ba daidai ba......kaman akwai wasu sautuka da abubuwa da suke tafiya ba daidai ba.
"Kinsan me kike fada sabreen?....maamah fa?.....rashin imani da qeqashewar zuciyarta har......" Bata jirashi ya qarasa ba wani sashe na zuciyarta ya soma gaya mata cewa,kariya yakeson bata,qaryatata ita kuma yakeso yayi.
"Abun nata baikai haka ba ko?,haka kake zato?.....kana ina sanda ta tursasamin aurenka don kawai ta mallakeka......ta tsundumani a rayuwarku don kawai na zama silar mallakarka gareta ta hanyar yin garkuwa da 'yan uwana......ta sanyani a kwanaki mafiya tsaho da tashin hankali a rayuwata?......kana ina a sanda ta sake diban qannena ta riqesu don ta samu damar cimma burinta a kanka da kaina......ta tirsasamin lallai saina shayar da kai na kuma ciyar dakai da asiri?.....na tufatar da jikina da rigar da zata zama silar soyayyarka a gareni?.mashkur......dama sauran wadanda suka kawowa rayuwarmu farmaki kina tunanin yin kansu ne?.....fareeda data samu nasara a kanka kana tunanin haka siddan ta sameta?......." Dora hannunta tayi saman matashin cikinta.
"Hatta da wadannan yaran da basuzo duniya ba kana tunanin sun tsira a hannunta?,banda kiyayewar Allah zuwa yanzu lissafin watana nawa da barinsu akeyi.........ka duba wannan" Sai ta ciro wayarta daga handbag dinta tana bude masa inda ta adana videos dinnan da sauri sauri ta dangwarar masa ta juya da sassarfa tana fita a parlor din tana sauka qasa.
Wayar yabi da kallo yana jin yadda jijiyar kansa ke wani irin harbawa. Yanajin kira na shigowa ta wayarsa dama system din gabansa,wanda ya tabbatar team dinsa da suke bincike tare ne suke kiran nasa,saidai baida wani kuzari ko kadan.