Showing 321001 words to 324000 words out of 557259 words
zaija hankalin masu kallonshi.
Ficewarsa daga falon ya bata wani qaramin sukuni,sai ta fasa komawa dakin ta sauka saman sofas din dake falon ta zauna tana maida numfashi. Idanunta ta maida hanyar daya wuce din
"Fareeda KHALED MUSTAPHA" Sunan ya dawo mata radam a kunne,murmushinsa kuma ya sake giftawa ta idanunta,ta sake lumshe idonta ta kuma budesu lokaci daya
"Waya sani ma ko ita ta kirashi?,wa yasan inda zasuje?" Ta furta can qasan zuciyarta tana tuna irin tuhumomin da take gani a kanta cikin idanunsa.
"Waye yasan abinda shi yake aikatawa ma?" Ta sake samun kanta da fada qasan zuciyarta. Ko daya ba zata taba aminta da cewa shi din a tsare yake ba......taga matasa masu tarin yawa da ni'ima da baiwar dukiyar da yake da ita yasu bata taka rabinsa bama......amma qazantar dake cikinsu sai Allah. Kamar dai shi......a haka kamilallen mutum....amma badininsu wata irin danqararriyar qazantace maras dadin gani ko tabawa.
"Adda......." Taji muryar amna daga gefanta. Fararen idanunta ta daga tana duban amna gami da katse tunanin dake kai kawo a ranta
"Amna" Ta amsa mata murya qasa qasa tana nazartar fuskarta. Fuska ta narke sosai tana zagayowa gabanta ta zauna.
"Nace wani abu adda bazai zama shishshigi ba?" Tayi maganar da alamun son ta furta abinda ke bakinta. Qaramin murmushi ta sakar mata don ta bata nutsuwa da gamsuwa akan duk maganar da zatayi
"Fadi amna mana" Sai data gyara zamanta tana maida mata murmushin sannan tace
"Yaaa saddiq yana bani labarin hamma......duk da na fisu sanin hamma ta wasu abubuwan.......amma ya saddiq kuma zai iya fina saboda shi din PA dinsa ne.....duk inda zai saka qafa a gida ko a office suna tare.......kinsan waye hamma kuwa?,ya yake?" Tayi tambayar da murmushin daya kusa zama dariya akan fuskarta.
Numfashi taja a boye tana jin sunansa kawai da amna ta kira yana qara yawaita bugun zuciyarta,inda zata iya zata dakatar da amna daga yi mata duk wata hira data shafeshi......kwanaki kaddan suka rage masa cikin rayuwarta.......tana jiran kawai ranar da zata samu tabbacin su huda sun isa mali lafiya hannun momma bahijja.......a wannan lokacin komai zai tarwatse.
"Saikin fada amna" Ta fadi bawai don ranta yana so ba,sake gyara zama sosai tayi ta riqo hannun sabreen
"He's a loving and caring partner.he wants a deeply romantic connection with his wife" Ta fada murya can qasa,kaman tana tunanin yana kusa dasu kuma tana tsoron kada ya jiyota. Dukka idanunta sabreen ta fiddo waje tana kallon amna,yadda amna din tayi maganar da wani confidence da qwarin gwiwa ya bawa sabreen mamaki.....can qasan zuciyarta kuma sai taji kaman tanason taja hira kadan da amna din. Abu daya dai tayi amanna fuskar fuad ta gida daban......fuskarta ta gidansa daban.....kamar yadda fuskarsa ta mu'amalarsa ta waje daban,banda haka mutum kaman fuad dinne zata siffanta haka?.
"Kina da ja ko adda?......" Ta tambayi sabreen kai tsaye,tana jin tanason tayi hira da ita.......tanaso ta fadi mata abinda ta fuskanta ko ita ta fahimci ba daidai ba
"I swear adda........He envisions a future where he and his wife grow old together,hand in hand......ko a gabana wannan yasha fadinsa......musamman idan suna hira na sako da sako shi da BB farouq.......hamma na yana son soyayya,ya kuma cancanceta......hammana yana son kulawa......that's why yakeji dani,komai na hammana daban yake a wajena.....tausayin hamma nakeji coz....He suffered a lot in his life
He had a rough past" Ta fada dukka a jere tana riqe da hannun sabreen kaman hakan shine zai saka ta fahimta abinda takeji a zuciyarta na tausayin hamman nata. Baki da idanu kawai sabreen ta sake tana kallon amna,tana sake gasgatawa da imanin cewa eh lallai da gaske wannan mugun yana da muhalli me girma da fadi a rayuwarta......amma wanne irin hardness ne haka ya fuskanta?,mutumin da ya rayu tsakanin iyaye biyu 'yan uwa hudu?,mutumin dake cikin daula da dukiya?.
"Believe me adda......please,ki qara akan kulawan da kike bawa hamma,He's passionate about building a strong loving relationship with his wife.......na dade da sanin duk wadda ta samu hamma fuad.....She's the luckiest woman alive and she's incredible fortunate" Murmushi ta samu kanta da subucewa dashi,saita miqa hannu ta riqe amna din sosai bawai don maganganu da yabo a kansa sun burgeta ba,aah......sai don ita din mutum ce me girmama 'yan uwantaka,saboda tasan girman soyayya da qaunar dake tsakanin 'yan uwa me girma ce......itace babbar shaida ta farko akan hakan akan kanta ma.
"Duka wannan yabon amna......anya baki fiya son kanki da yawa ba kuwa da wannan birkitaccen hamman naki?" . Murmushi amnan ta saki itama,har qasan ranta taji dadin yadda sabreen ta karba maganganunta,amma har ga Allah tana son matar hammanta ta zama dream wife nashi kaman yadda dukkaninsu suka fahimta
"Ki budewa hammana zuciyarki da kyau.....zaki sha mamaki adda.......inajin tukuicin zuwa dubai zakimin duk sati.....nayita zuwa ina ganin burj" Murmushi ta sakeyi kawai batace komai ba......abinda ya bawa amna daman sake cewa
"Adda.......na baki kadan daga tarihin hammana dana samu tun kafin a haifeni.....wannan ne kadai zai zame miki jagora wajen sake fahimtar waye.....ya kuma.baki qwarin gwiwan tallafarsa" Zame hannuwanta tayi daga cikin na amna tana girgiza kai
"Zaki bani.....amma ba yanzu ba amna.....kinga bana jin dadi sosai" Itama tayi maganar tana narkewa amna kaman yadda amnan keyi. Murmushi ta saki tana tuna warning nata da anni tayi akan ta kula da ita,kuma kada ta matsa mata da yawa,don haka sai tace
"Mu barshi pending......har sai kin samu lafiya" Kai ta gyada tana lumshe ido kadan
"Na gode" Har qasan zuciyarta tana jin dadin yadda amna ta fahimceta ta qyaleta. Sam bata son jin komai daya shafeshi,saboda tasan zasu fadi kirkinsa ne kawai bawai don haka yake ba,zasu fadi kirkinsa ne don haka yake nuna musu a fuska da mu'amalarsa da su,amma a waje kuwa.....babban azzalumi ne a wajenta mugu kuma.
Maida dubanta tayi kan maamah
"Ban taba kiran wani d'a namiji da adadi me yawa ba irin wannan sai d'anki......na masa kiran qarshe......inaso naga naki qoqarin" Abinda fareeda ta fada kenan ranta yana motsuwa hadi da qara baci akan lamarin. Bata taba daukan plan dinta bazaiyi wani aiki ba,kudade ta kashe masu nauyi don a buga ninkin adadin news paper din da aka saba bugawa a kowacce rana......sannan a fiddata tituna a kuma rabata kyauta ga kowa basai kowa ya siya news paper ba a ranar.
Guri daya maamah ta zubawa idanu tana murza tafin hannunta,tana ji a jikinta lokaci yayi da zata koma wajen boka ta zube masa komai.......ta gaya masa buqatarta ta gaba,ta zube masa ruwan kudin da ko bai shirya ba dole yayi aikin nan......daga can wani loko na zuciyarta tana fargaba.......tana fargabar kalamansa na can watannin baya......kalamansa na qarshe a haduwarsu ta qarshe dashi.
_taurarinta nada tsananin haske da wahalar cusa kai a cikinsu.......tabata abune da zai iya zuwa da nasara da kuma akasinta.........KINYI KUSKUREN ZABINTA......amma itace mahadin masarrafin b'arin nasa tauraron..........taurarinta sune abokan tafiyar nasa taurarin.........kusan komai nasu suna kamanceceniya da juna.......ITACE TA DACE DA CIKAR BURINKI MUDDIN AKA SAMU GUSHEWAR AKASIN DA NAKE HANGOWA_
Gumi ne taji yana tsatsatsafo mata......a take sai taji ai kaman ta fara shiga matsalar daya ambata mata. Sai yanzu kwanyarta ta fara aikin da a wancan lokacin bata yishi ba wato na fahimtar ma'anonin maganganunsa. Kenan aikin banza takeyi?,kenan ba wadda zata iya cika mata burinta akan faud sai sabreen din da take kokawar fitarwa a gidan?,wannan wanne AKASI NE da boka ke magana a kai wanda yace muddin ya gushe ita zata iya cika mata burinta......wanne akasi ne?.
*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
π π π π π π π π
_Zafafabiyar_
ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2
β±§Ιβ²Ιβ₯β³
ππΌππ 66
66
_ko kisan manzan Allah S A W da kansa ya kasance yana neman tsari daga sharrin abinda ya aikata da wanda bai aikata ba? Yakan ce"Allahumma inni a'uzu bika min sharri ma amiltu wamin sharri ma lam a'amal"_
_shi daya kasance Allah ya gafarta masa duk wani abu da zaiyi da wanda ma yayi,ina gake?_
Dukka jikinta sai ya dauki wani irin dumi,tamkar ma ta manta da fareeda dake zaune gefanta,wani yalwataccen tashin hankali ya duro mata......cikin qasa da minti guda taji tana tsananin buqatar ganinsa.
"Ke nake sauraro" Muryar fareeda ta yanke mata tunaninta. Idanu ta zubawa fareedan na wasu daqiqu kafin ta kammala tunani a kanta dukka cikin sakanni,murmushi ta sakar mata.
"Mu da kikaga muna cimma nasara a rayuwarmu......ba da gaggawa muke tafi da komai ba......kibarmin komai a hannuna......indai kinga baki samu fu'ad ba.....to tabbas bani na haifeshi ba". Maganar ta faranta ran fareeda duk da ta xuba mata kokwanto me yawan gaske. Amma itama ta yarda da kanta......tasan kuma nata kalar takun,don haka ta miqe da nata murmushin tana ajiye mata bundle na dollars.
"Ki qara da wannan......amma buqatata yazo ya ganni koda na minti talatinne kacal" Ta furta tana zuge zip din Jakarta,a qasan ranta kuma tana samun tabbacin da gaske ne fu'ad baya sakar mata zallar ruwan kudi.......abu na farko daya fara jefa mata shakka a zuciyarta akan matar.
Matashin billionaire irin muhammad jadda......wanda tsananin yawan dukiya da arziqin daya mallaka a gefe guda quruciya da kyau su suka saka mata kwadayin mallakarsa......kudaden data bata din ya kamata ace a kullum a arziqinsa basufi kudin siyan wasu qananun abubuwa ba....amma ya zamana ita ke fara'a da samunsu?. A arziqin mahaifinta idan aka kasa arziqin fu'ad hamsin qwaya daya ne.....amma ace ita karan kanta tana da qarfin halin yin kyauta irin wannan?. TABBAS AKWAI MAGANA.....MAGANGANU MA,ta furta a sarari qasa qasa.
Kudin kawai take juyawa a hannunta farinciki yana kamata. Ta samu kudin da zata tunkari aikinta,duk da tana baqincikin yadda kudin xasu salwanta,amma kuma idan ta tuna da ribanya ribarsu da zatayi sai taji koda ta salwantar da finsu ma ba komai bane. Saidai tana buqatar magana da yarinyar.......maganar da zata sake bata haske akan mataki na gaba da zata tabbatarwa boka shi take da buqata. Wa zara kira?zuwaira.....
Kira daya biyu uku hudu har goma wayar zuwaira a kashe take. Tayi tsaki har batasan adadinsu ba,da waye zatayi magana ya hadata da yarinyar?. Tsam ta miqe data tuna daxun maganarsu ta qarshe zuwaira ta gaya mata yarinyar taje gidan ita da mamarta,saidai batasan ko tana can ko sun dawo ba. Ta qwalawa badawiyya kira
"Ki tafi gidan hamza ki karbomin number wannan yarinyar"
"To hajiya" Ta amsa mata a ladabce sannan ta juya tana ficewa ba tare data tsaya jiran komai ba.
Hannunsa ya sanya saman labbansa kawai yana sauraren bayanin manager na gidan jarida na qarshe da yakeyi,wanda banbancinsa dana sauran qalilanne
"Amma wallahi wallahi ranka ya dade kaman yadda 'yan uwana suka fada ne......wallahi bansan sadda aka buga labarin ba......ni dinma kamarsu gayyata na samu na taron 'yan jarida unexpected.......amma sanda na iso na samu jaridar ta fara fita hannun dealers na dakatar da saidata......waye zaiyi wasa da mutum kamar kai?,wanne gangancinne zai debi mutum......ko baya ga haka kana da mutunci da martabar da bai kamata mu bari a bata sunanka dana iyalinka ta wannan hanyar ba" Mutumin da aqalla ya kusa shekara sittin a duniya ya fada cikin matsanancin takaicin yadda duk karamci irin na jadda jaridarsa ta shiga sahun wadanda suka ci masa mutunci....duk da Allah ya taqaita an daqile fitar jaridar.
Iska me zafi ya furzar daga bakinsa yana sauke qafafunsa qasa,kanshi yana sake daukan zafi da lamarin.
"Inason list na dukka mutanen dake da aiki a ranar a dakin buga labarai.......da full details na kowa" Ya fadi a ransa yana jin zaiyi aikin daya jima baiyi ba.
"Sir.......ai mun kammala wannan.....muna jira ne kawai ka gama ji daga bakinsu......dukkanin dealers din mun karbi copy na newspapers din daga hannunsu,yanzu haka ba wanda keda sample nata.....Allah yasa munyi abun da sauri basukai ga rarrabawa qananun 'yan kasuwa ba,mun samu dukkanin jerin mutane hamsin da uku dake da aiki ranar a gidajen jaridu ukun......saidai mun rasa mutane uku a ciki,mutum daya daga gidan kowacce jarida......abinda ya qarfafa zarginmu akan suke da hannu.......na tura ma'aikata don binciken inda suke,kuma ina saka ran koda wanne lokaci zasu bani information,amma sauran mun tabbatar basu da masaniya akan komai" Wani abune daya tsaya masa tun jiya ya dinga sulalewa yana narke masa,ya gyada kai yana jin sassaucin dunqulallen abun daya tare masa wuya. Kafin yayi magana aka nemi izinin shigowa dakin. Ma'aikacin ya duba ya kuma bada izinin shigowa.
Salute nasa sukayi mutum biyun da suka shigo,suka kuma miqa masa wani takardu.
"Auwal sadi.....nura mahadi......labaran isyaku.....gaba dayansu mun samu tabbacin sun fita daga qasar nan kusan awanni biyu da suka shude,saidai kowannensu mun samu tabbacin qasar daya sauka.....auwal ya sauka a uk.......nura South Korea......shi kuma labaran ya sauka a china".
"South korea.....UK.....china" Fu'ad ya furta sunayen a fili yana irgawa da yatsunsa,sai ya fesar da iska a bakinsa yana maida dubansa kan CP.
"Well done sir......i really appreciate your effort,thank you for your hard work.......a sallamesu inason muyi magana privately"
"Okay sir" Ya amsa masa cikin girmamawa.
Cikin qasa da mintuna ya sallami kowa,ya kuma riski fu'ad din cikin motarsa qirar Mercedes sprinter. Duk yadda yaso mazewa da ganin alatun dake cikin motar tamkar kana cikin wani hamshaqin parlor din bawai mota ba amma ya gaza,sai daya daga kanshi ya kalli saman roofing din da yafi kama da lafiyayyen roofing din dakin sanda fu'ad ke qara hasken cikin motar daga galaxy blue stars zuwa brighter light.
"Ina expecting tafiya nan da kwanaki uku......inason kayi gaba da kula da komai har zuwa sanda zan dawo......saidai banason binciken ya dakata......zanyi qoqarin ganin an kawosu daga dukka qasashen da suka tsallaka din don su fadi wanda ya basu contract din......wadancan mutum biyun kuma,ko tambayarsu bana fata kuyi.....ajiya na baku......irin ajiyar nan ta ma'anan ajiya" Yakai qarshen maganar yana tura cheque na kudi daya rubuta masa masu yawan gaske. Kai ya girgiza
"Nop sir.....bazan amshi komai ba,aikina ne nakeyi kuma dole mutum irinka a masa aikin daya dace saboda alfanunsa ga al'umma". Wani abu dake gefansa ya dannan wata qaramar ma'ajiya ta fito,ya jefa cheque din yana cewa
"Ba bribing naka nakeyi ba.......wannan din kyauta ne na baka,na jima da sanin wanene kai......inda baka cancanata ba ko qwandalata ba zata shiga hannunka ba.....kana daya daga cikin mutane masu aiki tuquru da qoqarin kamanta gaskiya duk da yadda qasarmu ta lalace.....so you deserve it,xan baka koda bakamin aikin komai ba"
"Thank you sir.....thank you so much" S.nuhu ya fada yana jin dadin gwaggwabar kyautar da me jadda din ya bashi.
Tunda wuri taqi zaman parlor din don batason ma ya dawo shi ya gansu ko ita ta ganshi,ta zame tayi zamanta a daki dole amna ma ta biyo ta can.
Tana saman sofa din dake gefe daya a dakin,amna na zaune saman tattausan carpet din tana assignment. Idanunta kan takardun tana jin sha'awar amna din,tana jin inama ace itace ta samu dama irinta amna?,inama ace ta samu daman zuzzurfan karatu kaman amna?,wadda gata ya sanya tace bazatayi karatu wata qasar ba tsabar samun dama.
Maida bangon littafin tayi tana duban sabreen cikin murmushi
"Done......sai yanzu hankalina ya kwanta...lecturer dinnan mugu ne adda.....any mistake game over" Murmushi ta tayata dashi,ta jawo jakarta tana qoqarin maida litattafan
"Adda......kin taba jin labarin labarin uwar data watsar da yaranta tun suna qananu ba tare data damu da waye zai kula dasu ba?,waye zai zama gatansu?" Takai qarshen maganar tana zuba idonta akan fuskar sabreen. Maganar sai tayi ma sabreen wani iri,a hankali ta girgiza kanta
"Aah amna"
"Kin taba jin labari,bayan wasu shekaru ta dawo garesu,amma kinsan me yasanya ta dawo garesu?" Kai sabreen ta sake girgizawa
"Kudi......arziqi da rufin asirin da suka samu tazo ci,ba yadda suka rayu bane damuwarta......ba lafiyarsu ko akasinta ba". Idanu sabreen ta zubawa amna tana jin labarin ya kasa kama hankalinta,tsahon wasu mintina ba wanda yace da kowa komai,har sai da sabreen ta fara magana
"Wanne irin cukurkudadden labari ne wannan amna?,a ina kika jiyoshi." Qaramar dariya amna ta saki tana janye jakarta gefe
"Labarin mijinki kenan.....hamma na....." Bata qarasa ba shigowar saqo wayarta ya katse sauran maganar dake bakinta. Wani irin shuru sabreen tayi lokacin da hankalin amna yayi kan wayarta
"Maamah?,mariya?....." Abinda kawai sabreen ke iya juyawa cikin ranta kenan
"Bai rayu da ita ba?......batasan komai nasu ba?......batasan wahalarsu ba?,dukiyarsu tasa ta dawo??,dukiya???" Tarin tambayoyin da suka jujjuyawa cikin kwanyarta kenan. Maganganun amna gaba daya sai suka kasance mata kamar ta jefeta da wata cukurkudaddiyar sarqa,ta kasa hada daya da daya ya bata biyu.
"Unbleavable!......oh my god!" Amna ta furta da wani irin qaraji,abinda ya yanke zaren tunanin sabreen kenan,ko kafin ta farga har amna ta fado jikinta ta cukuikuyeta
"From nigeria to Maldives........wedding bells adda.......wedding bells" Ta fada tana dariyar dake cakude da farinciki zalla a muryarta. Qoqarin dagata sabreen takeyi cikin murmushi da mamakin abinda ya sanyata tsananin farinciki irin haka
"Zaki karyani auta" Ta fada a dan shagwabe tana riqe amna din. Da sauri ta dagata tana fadin
"Am sorry adda.....wani irin mamaki uncle BB ya bani......yayi surprising dina irin wanda ya jima baimin ba......adda hutunmu na wannan shekarar zai fara daga Maldives......kinsan mafarkaina akan wajen kuwa?,kowanne year idan anzo zaben wanne qasa za'a je idan na kawo sai BB da saddiq sun kushemin.......yaa musaddiq kawai ke goyon baya na" Ta qarasa maganar muryarta a narke,da alama tana jin haushin yadda abun yake kasancewa. Dan murmushi sabreen ta saki,don ita inda take maganar ma batasan ina bane ballantana tasan muhimmancin da yake dashi ba da za'a dokanta aje.
"Your dream have