Showing 39001 words to 42000 words out of 557259 words

Chapter 14 - πƒπ”ππˆπ˜ATA BOOK1 AND 2 HAUSA NOVEL

HUGUMA   

03 Nov 2025

559

talatin na samu ashirin da takwas......sannan an bamu assig....."

"Kai haneefa haba" Nadra ta fasa tana hade fuska. Murmushi ta saki,saita dagawa nadra hannu

"Qyaleta,zo.nan auta" Ta kirata sanda huda ke qarasowa ta aje mata ruwan pure water me sanyi guda biyu

"Ki aje komai sai zuwa anjima zan duba,duka yau tare zamuyi assignment din kinji?" Kai ta daga tana murna ta cilla da gudu ta koma bedroom dinsu da jakar.

Sai data bula ruwan sannan ta kalli huda

"Me yasa baku wuce islamiyya ba?" Gyara zamanta kadan tayi sannan tace

"Jiran dawowarki mukeyi" Rabi tasha ruwan ta ajjiye tana sake karantar wani yanayi na daban daga huda din

"Sai na dawo sannan zakuje Islamiyya huda?,yaushe aka fara wannan tsarin a dakin nan?" Tadan furta a zafafe tana dubanta. Qasa da kant huda din tayi,ba kasafai take ganin fushi ko fada dava Fuskarta ba,to amma duk sanda tayi din ya tabbata laifi sukayi mata babba.

"Kiyi haquri.na tsaya dora abinci ne" Sassautowa tayi kadan tana sauke boyayyen numfashi. Bata qaunar abinda zai zaunar dasu cikin gidan ko kadan ballantana idanuwa ko kunnuwansu suji ko suga abinda rayuka zasu baci. Hakanan koda wasa bata qaunar suyi wasa da makaranta. Tana jin ciwo idan ta tuna iya inda matakin karatunta ya tsaya a shekaru ashirin da daya hudu da take dashi a duniya,wanda a yanzun kimanin shekaru hudu kenan rabonta da wata bawa wai makaranta.

"Ku shirya ku wuce,duk da lokaci ya fita amma baiyi nisa ba ai" Ta fadi tana duba agogon hannunta sannan ta fara zareshi daga hannunta.

Tana zaune dukansu suka gama shiryawa cikin fari qal din uniform da baqar doguwar riga daga sama. Hankalinta bai dawo daidai ba sai data tabbatar sun fita a gidan.

Kai tsaye ta rage kayan jikinta ta zura sassauqar riga sannan ta wuce kitchen din dake falon tana duba girkin da huda ta fara yi.

Komai yayi daidai,dole ta sanya huda ta koyi girki tun batakai minzali ba. Tana fita ta bar mata nadra da haneefa,tun bata san ya zata kula dasu ba har ta koya. Ko a yanzun idan huda tayi girki,itama tayi sai na huda ya dara nata.

Sai data kammale komai sannan ta daura alwalar sallar la'asar,sanda ta idar idanuwanta sun fara nauyi,tana zaune daga saman abun sallar tana dan murxa idanunta. Ba baccin take buqatar yi ba a yanzu,tana son magana da jib ne. A yawancin lokuta a irin wannan lokacinne take samun tattauna maganganu ire iren wadannan,sam bata yarda tayi komai bisa idanunsu,bata taba bari ta rab'a lamarin rayuwarsu da nata rayuwar,komai tana tsaidashi ne iya muhallinsa.

Hakanan tana hamma ta miqe ta koma daki. Locker gefan gadonta ta jawo,ta fidda madaidaiciyar baqar jaka dake dauke da mini laptop dinta,sannan ta zaro wayarta dake cikin jaka ta sake dawowa cikin falon.

Kalmomin sirri ta sanya ta bude laptop din,sanna ta maida hankalinta akan wayarta tana barin laptop din ta daidaita. Maadanar lambobi ta shiga bincikawa har ta kawo kan sunanshi,ta danna masa kira tana aza idanunta akan screen na laptop din tana duban hoton daya mamaye fuskarta. Hoto ne da bata gajiya da kallonsa,duk sanda ta dubi hoton sai taji kamar tana tare da ita,kamar zata kirayeta ta amsa,kamar zata iya jin kadan daga radadin da take fuskanta,kamar zata damqi hannunta su fuskanci wannan JUYAYAYAR DUNIYAR su kuma kutsa cikin birkitacciyar rayuwarta su kawo daidaito.

Daga wayar da akayi shi ya katse mata tunaninta,ta daidaita idanunta da suka fara zugi kadan kadan da alamun son tara ruwan hawaye

"Aikin jeeb ya taso?" Boyayyen murmushi ta saki tana gyada kai

"Sosai......ka zama kusa da na'urarka......inason sanin wayeshi"

"An gama" Ya fada a taqaice

"Aikin dazu fa?" Ta sake tambayarsa

"Adda ya zama tsohon tarihi......bashi ba......ko bankinsa basu isa susan ya akayi kudin sukayi fiffike ba bare inda suka sauka"

"Yayi" Ta amsa masa a taqaice tana sauke wayar daga kunnenta.

Sake duba bagaren kira tayi a nutse har ta iso number wayarsa. Ta tsaya kadan tana kallon numbers din. Daga yanayinsa da yanayin shigarsa ta tabbatar ba qaramin mutum bane. Amma ko daya batajishi koda a gefan zuciyarta bama bare a shiga wani batu na daban. Hasalima yadda yaso bata mata lokaci ne yafi bata haushi,kalaman bakinsa kuwa aqalla taji masu kamanceceniya dasu a bakin gomman maza......maza iri daban daban,masu mabanbantan halaye da dabi'u.

Tana jan system din kira yana sake shigowa. Ta dora zagayayyun idanunta ga fuskar wayar tare da zubawa numbers din idanu kamar me nazari. Batasan wadanne irin zukata suke dasu ba.......a sanda sukaso abu suna zamewa tamkar wadanda ba zukata a qirjinsu,tamkar wadanda hankulansu ke zamewa daga gangar jikinsu,idanuwansu da dukka kunnuwansu suna rufewa ruf izuwa ga cikar muradinsu.

Dukka layukan da tasan zasu zame mata damuwa ta ciresu kwanaki biyu kenan,ta kuma tabbatar akwai masu nemanta da yawa.

Qaramin tsaki taja ta saka hannu ta jawo wayar,ta daga tana karawa a kunnenta


*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*

*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*

*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*

*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*

*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*

*ZAFAFA BIYAR*

*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*

*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*

_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_

_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_

_K'ALBIM Mamuhghee_

_AJIYA A DUHU Billynabdul_

_DUNIYATA Huguma_

_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_

*hudu 2k*

*uku 1500*

*Biyu 1k*

*Daya 500*

_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_

*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*

*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*

*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*

*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*

*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*

*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*πŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺ

89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf

*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*

*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*πŸ₯°πŸ₯°

*D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

*Arewabooks@:Huguma*
https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997

PAGE 24
____________________________

*_ALBISHIR A GAREKU!!_*

*_SHIN KUNSAN UMMUMAHNOOR LUXURIES TA TANADAR MUKU INGANTATTUN KAYAN ADO NA FITA KUNYA KUWA?_*

*_KAMAR SU_*

Atamfofi
Laces
Shadda
Materials
Takalma
Jakunkuna
Mayafai
Trolley
Sarka da dan kunne
Oil perfumes

*_karki tsaya sanya har ayi babu ke,maza garzaya ta nan_*

Numbers
08034469681
08135142610

Handles
Instagram @ummu_mahnoor_luxuries
TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries
Facebook ummu_mahnoor_luxuries

*_inganci da kwalliya shine muradinmu_*
____________________________


"Ranki ya dade.....girmanki ne ai" Idanunta ta lumshe sannan ta budesu,shima dai kaman sauran,gwanayen dadin baki da iya tsara mace,abinda basu da masaniya akai....ya zuwa yanzu babu wani d'a namiji da yake burgeta duk duniya. Sunan soyayya kawai da labarinta tana daukanshi a mazaunin wani wasa ne.....wasa da qwaqwalwa da wani salo na batawa kai lokaci.

Ya'aqoub,daya daga matasan mazan dake sharafinsu,kuma giyar soyayya da ta sha'awar sabreen suka yiwa qawanya. Daya daga cikin mazan da sukejin zasu iya kashe komai......zasu iya bada komai,hakanan zasu iya salwantar da komai saboda ita

"Ayimin afuwa nasan wataqila nazo da takura......ba wani abu nake bida ba illa a bani dama zan turo dan saqo da aike"

"Ka wuni lafiya?" Ta katseshi ya hanyar tambayar lafiyarsa. Wani boyayyen numfashi ya aje,daya daga cikin dabi'unta da suka banbanta dana sauran matan da ya sani wadanda suke rayuwa shigen tata......dabi'arta guda daya dake tsundumashi a kokwanto da tunanin WACECE ITA?,YADDA ZAHIRINTA YAKR HAKA BADININTA YAKE?.

Yana da tarin buqatu da yakeson gabatar mata dasu,saidai kwarjininta da wani irin shakkarta yakan daki zuciyarsa a duk sanda yayi yunqurin hakan. Ta sha bashi damar haduwa sama da damarmakin da take bawa kowa......hakan kuwa baya rasa nasaba da yadda yake kame kansa a gabanta

"Lafiya qalau.....saidai tsananin kewarki......na iso qasar nan da burin ki zama mutum ta farko da zan fara tozali da ita....... Amma inajin nauyin tambayar hakan don kada na aza miki abinda ranki baiso"

"Banayin abinda baniso......hakanan bana yin abinda zan takura" Ta fadi mishi kai tsaye kaman yadda halayyarta take.

"Na sani nadeeya" Ya amsa mata da karsashinsa,har sai da boyayyen murmushi ya kubce mata. NADEEYA shine stamp din ya'aqoub,kaman yadda muhseena yake stamp din MASHKUR,mashkur din da tayi imanin zuwa yanzun qila ya kusa zaucewa da rashin samunta a waya da bayayi. Shi kansa ya'aqoub din wata irin saa ya taka a sanda yayi katarin samun number wayarsa. Dashi da mashkur dukkansu ta hadu dasu ne a rana daya,saidai kuma a mabanbantan gurare da lokuta.

"Zaa yimin wannan alfarmar?" Ya tambayeta yana langabar da kansa tare da sassauta muryarsa da kyau

"Zan duba"

"Zuwa yaushe please......zuciyata a jigace take nadeeya.....i beg you karki sakamin lokaci da nisa....."

"Baka da damuwa" Ta sake bashi amsa a gajarce

"Dan saqo na yana iya isowa?"

"Sharada yahaya gusau road,najbil road" Ta fadi a nutse tana yanke kiran.

Wayar ya cire a kunnensa yana binta da kallo. Ya zaci inda yayi mata aike wancan karon wannan karon ma can za'a kai mata?. Iska ya furzar daga bakinsa,bata da wuyar canzawa tamkar waya hawainiya. Har yanzu bashi da wani yaqini ko tabbaci a kanta. Baisan komai a kanta ba banda suna da kamanninta. Yana da buqatar abubuwa masu yawa game da ita amma bata bashi dama ko qanqani a kanta ba.

"Allah yakai damo ga harawa" Ya fadi yana furzar da iska daga bakinsa. Ya miqe a hankali yana ture kyakkyawan mulmulallen table na glass dake gabansa cikin qawataccen falon nasa da ya tanada domin hutawarsa yana laluben number wayar babban yaronshi. Yanason saqon ya isa gareta da wuri,don yanason ya sanya qaimi ya matsa da kyau don samun kyakkyawan kusanci tare da ita.

A yadda ya ganta baiyi tsammanin za'a dauki wani dogon lokaci ba tare da ya samu abinda yakeso ba. Saidai duk sanda ya tuna yanayin jin kanta,miskilancinta da shariyarta,sai yaga eh.....ba abun mamaki bane,mata irinta daban Allah yake halittarsu.

Baki ta tabe tana ajjiye wayarta a gefe,sai kuma taja dan siririn tsaki tana sake bada duka hankalinta akan system din.

Folder da takanyi rubuce rubuce ta adana a duk sanda zuciyarta ta buqaci abokin hira ta shiga,ta budeta,sannan ta fara rubutun daga dukkan abinda taji tana da buqatar amayarwa.

Wata irin rayuwace da babu qawa ko aminiya......babu aboki ko amini......qawayenta sune qannenta da suka fito daga tsatso guda......saidai har kwanan gobe bata bari sun zame mata aminai ba.......saboda batason tunaninsu da hankulansu su gurbata ya zuwa wani tunani na daban. Tana jin itace dole.....kuma tilashin daukan alhakin komai yana a wuyanta.

Awa guda harda qarin wasu mintuna ta dauka kafin ringing na wayarta ya janye hankalinta. Ta dauke idanunta da suka dan sauya launi tana mayarwa kan wayartata,daidai sanda take iya jiyo hayaniya da ifce ifcen wasu daga cikin jikoki da yaran gidan. Bame son hayaniya bace sam,zata iya rayuwa cikin muhallin da babu motsin kowacce halitta sai ita......tana da wannan damar ta samarwa kanta irin wannan muhallin da kuma wannan rayuwar......amma qaqqarfan dalili guda daya tal zaya hanata kaiwa zuwa ga wannan burin nata,tna buqatar tsira da sauran burbushin MUTUNCINTA tana son ta sake tabbatarwa da kowanne me zargi abinda yake zargi a ransa yaji haka ne?,ko kuma ya sauya bigiren ra'ayinsa a kanta.

A nutse ta karanta sunan dake saman screen din,sai ta tattara dukka hankalinta akan kiran ta ture system din tana jingina sosai da makarin kujerar tata.

A nutse tayi mata sallama

"Wa'alaikumussalam" Aka amsa daga daya bangaren cikin matuqar nauyin jiki dana murya.

"Lafiya kike titi?" Sabreen din ta tambaya murya a sanyaye itama. Tana jin dukka wata gaba ta jikinta tana yin sanyi

"Alhamdulillah sabreen.....,saidai......"

"Aisha ko?,ayshatu?" Kai titi take jinjinawa tana qoqarin hadiye abinda yake taso mata. Saita kass cewa da sabreen din komai,bataso ta bijiro mata da abinda take da tabbacin itama yafi qarfinta......bataso ta bijiro mata da abinda zai hautsina nutsuwarta,duk kuwa da tarin qoqarinta.....sadaukarwa da tsaiwar dakanta akan yarinyar

"Titi ki fadamin me ya faru?" Ta sake jefa mata tambayar tana jin kamar ta tashi a daren ta iskesu a inda suke

"Ki nutsu sabreen.....Allah yana sane da halin da take ciki......kinyi iya yinki......kinyi kuma iya abinda zaki iya,mu barwa Allah komai"

"Titi ki fadamin!" Ta furta adan tsawace,tsawar ma da batasan ta yita ba

"Sabreen.....naira million takwas suke da buqata wajen aikinta" Wani qaramin jiri taji tana niyyar kayar da ita tana daga zaunen. Tayi luuu da idanunta tana son furta addu'a ko qwaya daya ce amma bakinta ya kasa lalubota.

"Tabbas titi akwai abinda kika boyemin......baya rabuwarmu wani abu ya biyo baya amma titi baki gayamin ba......tabbas" Ta fadi muryarta tana rawa. Tana ji har tsakiyar zuciyarta da ruhinta tausayin aisha kamar zai kasheta.

"Wannan wacce irin DUNIYA ce dake cike da al'umma masu tsananin son kansu?,duniyar da kowa kansa ya sani?" Ta fadi a sarari tana iya jiyo kukan titi wanda takeson boyewa.

Kasa riqe kanta itama tayi,sai kawai ta tsinke wayar,ta dora Fuskarta saman hannun kujerar da take kai. Ba zata iya riqe quncin da takeji saman qirjinta ba,ciwo nauyi da kuma radadin ya mata yawa. Abinda ta saba kamar kullum shi tafi buqatar yi a yanzu wato KUKA. KUKA abu guda daya daya zame mata solution na dukka matsalolinta,duk da ta dade da sanin kukan baya maganin komai.

A hankali take rera sirin kuka wanda take kokawa rayuwar su da rayuwar aisha. Tsananin talauci da rashin galihu ya sanya ta tsinci kanta a halin da take ciki yanzu. SON ZUCIYA da rufewar idanuwa da tsananin zallar rashin imani ya sanya yayi mata silar zamowa daya daga cikin mutanen dake ziyartar asibiti domin ganin LIKITAN ZUCIYA.....ciwon da yakai minzalin da take buqatar TIYATA don ceto rayuwarta


*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*

*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*

*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*

*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*

*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*

*ZAFAFA BIYAR*

*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*

*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*

_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_

_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_

_K'ALBIM Mamuhghee_

_AJIYA A DUHU Billynabdul_

_DUNIYATA Huguma_

_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_

*hudu 2k*

*uku 1500*

*Biyu 1k*

*Daya 500*

_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_

*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*

*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*

*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*

*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*

*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*

*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*πŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺ

89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf

*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*

*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*πŸ₯°πŸ₯°


*D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

*Arewabooks:@Huguma*
https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997

PAGE 25
__________________________
*_ALBISHIR A GAREKU!!_*

*_SHIN KUNSAN UMMUMAHNOOR LUXURIES TA TANADAR MUKU INGANTATTUN KAYAN ADO NA FITA KUNYA KUWA?_*

*_KAMAR SU_*

Atamfofi
Laces
Shadda
Materials
Takalma
Jakunkuna
Mayafai
Trolley
Sarka da dan kunne
Oil perfumes

*_karki tsaya sanya har ayi babu ke,maza garzaya ta nan_*

Numbers
08034469681
08135142610

Handles
Instagram @ummu_mahnoor_luxuries
TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries
Facebook ummu_mahnoor_luxuries

*_inganci da kwalliya shine muradinmu_*
____________________________


Ita kanta batasan yawan lokacin data dauka a wajen ba,batasan kuma ta jima a wajen ba sai data fara jiyo muryoyin yaran gidan cikin wadanda ke zuwa islamiyya sannan ta tuna da HUDA NADRA DA HANEEFA.

Ta tabbatar muddin suka shigo suka sameta a irin wannan yanayin sai hankulansu ya tashi. Wani irin soyayya da kulawa suke mata,wadda sam sam basa qaunar abinda zai tabata komai qanqantarsa.

Da azama ta miqe tana leqa fuskarta tsakanin labulen falon zuwa filin tsakar gidan. Tanaso ta fita ta wanke fuskarta ta kuma daura alwala,amma bataso taci karo da kowa ballantana su tunzura hali da yanayin da take ciki.

Idanunta ta maida ta lumshe muryar titi tana mata amsa kuwwa a kunneta. Cikin duhuwar idanuwanta tana hangen aisha da wannan innocent face din nata. Har yanzu bata huce ba daga abinda azzalumin ya aikatawa aishan ba.....duk da burinta ya cika na danganashi da gidan kaso da tayi. Har yanzu tana jin kamar hukuncinsa yafi qarfin wannan hukuncin da akayi masa a yanzun.

Lokaci guda taji hankalinta yana neman tashi

"Million takwas" Sautin adadin kudin ya ratsa kwanyarta. Ta ina zata soma nema?,ta ina kuma zata samu?.

"Mashkur" Zuciyarta tayi mata hasashenshi farat daya. Tsam tayi da ranta tana juya sunan cikin zuciyarta. A hankali sai kuma ta dinga gyada kanta,tana bawa kanta da kanta tabbacin yes......a jikin mashkur yafi cancanta a hada wadannan kudaden,iya wannan tunanin ya sanyata

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login