Showing 81001 words to 84000 words out of 557259 words

Chapter 28 - πƒπ”ππˆπ˜ATA BOOK1 AND 2 HAUSA NOVEL

HUGUMA   

03 Nov 2025

487

takeso a tsara table din don zuwan musaddiq cin abincin dare gidan,daya yana ga duban cikar lokacin da zai iso din,yayin da dayan yake kan zuwaira tana sauraren zantukanta da a mafi yawan lokuta sukafi gama da banbadanci.

Sake gyara zamanta tayi tana daidaita zanin embroidery vlisco atamfa din dake jikinta wadda kudinta ya tasamma dubu sittin. Ta zube idanunta akan zuwairan karo na uku

"Duk yadda zanyi zuwaira.....kome meye ne zai faru dole zan dauki mataki fa.....ba irinmu ake zuwama da irin wadannan abubuwan su bari ba.....komai tsiya musaddiq da fu'ad 'ya'yana ne halak malak,babu wanda ya isa duk duniya ya kankare wannan matsayin" Ta fada har cikin zuciyarta tana jin zafi tsana da qyamar anni......tana jin a duniya ita da alhaji hamza sune manya manyan maqiya kuma abokan gabar da bata da sama dasu. Sake duba agogo tayi,yadda taga lokaci yana ta ja ya sake sanyawa ranta ya baci

"Zuwaira yanzu haka yana can ta riqeshi har sai sanda tayi masa izini zai taho gurina?" Kyabe baki zuwairan tayi tana tallafe kanta da hannunta tare da dogarashi jikin kujera,sannan ta karkatar da kanta tana kallon wani sashen,tabbacin abun yana mata matuqar ciwo kenan

"Kema ai kinsan kwanan zancen.....ai kinyi sake maryam ba dan qarami ba kuwa". Maganganun zuwaira suka sake zame mata tamkar allura,taja wata doguwar qwafa bacin ranta yana ninkuwa,a take taji duk wani danshi na maqogaronta ya bushe ruwa take da buqatar sha. Kamar ko yaushe a tsawace tayi kiran sunan me aikinta,ta nufota a gaggauce,ba tare data bari ta qaraso ba tace da ita

"Koma ki bani ruwa......banason kowanne sai swan.....karki maimaita kuskuren jiya". Jikinta yana ruwa ta amsa mata

" In sha Allah ba za'a samu matsala ba" Ta juya da hanzari hanyar kitchen.

Su biyu ne kadai zaune saman lafiyayyen dining din na wata iriyar mulmulalliyar kwalba me garai garai. Komai na gidan an zubashi ne bisa nunawa kudi iyakarsa,komai me kyau ne me kuma asalin tsada,kamar yadda komai aka zubashi bisa tsari.

Anni ce saman daya daga cikin kujerun,jikinta sanye da wata sassauqar cotton abaya 'yar asalin moroco wadda ta dace da jikinta da kuma shekarunta. Kanta sassalkan dan kwali ne da yazo da rigar,tana riqe da waya da alama wani kira take amsawa da ya janye hankalinsu su duka ita da musaddiq dake zaune saman kujerar dake fuskantar tata. Idanunshi akan annin yana dariya saboda yana iya sauraren abinda siririyar muryar ke fadi ta wayar. Jikinsa na sanye da yadin senate me asalin tsadar. Sosai yadin ya kwanta masa a jiki ya kuma dace da kyakyawar hularsa dake aje saman table din daura da plate din abincin da yaci rabi yana riqe da cokalin yana sauraren wayar anni.

"Don Allah anni kice mata ta zauna kin yafewa nanna ita" Ya fada qasa qasa yana boye dariya da muryarsa don bayaso ta jiyoshi. Annin ta jishi sarai,murmushi me sauti ya kubuce mata,saita cira wayar daga kunnenta tana cewa

"Ga qaramin yaaya zai baki saqo" Ta aje masa wayar a gabansa taja nata plate din a hankali taci gaba da diban abincinta tana ci tana kuma saurarensu.

Idan daru ne tsakanin amna da musaddiq a gidan ba wanda baisan da zamanshi ba. Saidai kuma akwai shaquwa me tsananin qarfi tsakaninsu da ba wanda ya isa ya taba daya a gaban dayan. Wani sabo da 'yan uwantaka ce me zurfi a tsakaninsu wadda tadan sha banban da wadda ke tsakaninsu da FU'AD da kallon UBA kusan sukeyi masa.

Tana jin yadda suke fafatawa da yace mata an barwa nanna ita,ya dinga kwasarta yana dariya anni na zaune kawai tana murmushi har sai daya tabata sosai sai ya yanke kiran,daidai sanda farouq ke shigowa falon.

Sassanyan matashi,cikamakin barin zuciya ruhi da rayuwar mamallakin kamfanin jadda diamond chores resources muhammad fuad jadda. Kaman twin brother dinsa fu'ad yadda ake kallonsu kenan,illa banbancin career da kowanne yake dashi.....yana da wani ajiyayyen kyau nutsuwa da haiba. Su biyun kam sun zamewa duniyar 'yammata da yawa jarabawa,ba'a maganar 'yammatan da karansu baikai tsaiko ba.....yammatan da basu da damar nuna yatsa ko tsaiwa a dandamalin da kowacce diya da take ji da gata da kudi zata tsaya......yammatan da saidai su gansu jikik TV mujallu da jaridu da kuma sauran kafafen sadarwa......aah.....wannan fagen na 'YA'YAN GATA ne,yaran da iyayensu da kuma su kansu suka ci suka kuma tayar da kai,yaran da suke da chance 50 to 60 percent na ganinsu,walau a gidajensu ko a guraren ayyukansu,ko tafiya ta hadasu a filin tashi da sauka na jirgin sama a kowacce jaha dake Nigerian,ko kuma su hadun cikin qasashen da aiki ko kuma hutun da sukan tafi dukka family din alhaji HAMZA KIBIYA zuwa wasu daga cikin kebantattun qasashen da sukanyi quri'ar zuwa.

Wata irin nutsuwa suke da ita,wanda kwata kwata harkar mata bata gabansu. Har gwara gwara farouq din,akwai wasu banbance banbancen dabi'u da kuma halaye tsakaninsu da fu'ad. Tun asali farouq mutum ne meson comedy ko yaya ne,abinda zai sakashi dariya da nishadi,yanason yaga ya tsokani mutum abinda ya sanyashi yasha wahala qwarai a hannun mariya......sabanin sadiq da yake da tsoro da kuma tsantseni. Saidai dukkansu a yanzun girma ya sauya wasu daga cikin halayensu. Raino na uwa da Allah yayi musu alfarma suka sake samu,sai dukka wannan tsoron na sadiq ya gushe,ya koma tsaiwa da jajircewa akan komai,saidai kuma ua biyo halin fu'ad na matsanancin miskilanci shariya da kuma maida kansa kamar baya fahimtar abinda kake aiwatarwa. Dauke kai da banzatarwa akan abu idan baiso ba,zaman kadaici da rashin son hayaniya ko doguwar magana. Farouq yana nan da halinsa,saidai ya ragu sosai,kusan dukka sakewarsa cikin gidan ne,idan ya fits waje ya koma boss saidai cikin abokai kuma. Shi dinma ya samu abokin tayi wato musaddiq,wanda shine copy dinsa,idan suna a gidan maida anna suke kamar kakarsu,abu daya ne yake bata salama idan fu'ad yana nan,tofa nan daya,sunsan qaryarsu tasha qarya,dole su shafa mata lafiya subar bakinta ya samu salama.

A boye musaddiq da sadiq suka fara zuwa zance abinsu. Ba wanda ya sani sai ranar da fu'ad ya fahimta. Da wannan salon hukuncin nasa ya ritsasu a falo,kowanne ya rasa da bakin da zai masa bayani,amma koda anni ta iskesu ana shari'ar goya musu baya tayi

"Ba wanda bazai iya riqe mace ba a cikinsu,tunda sama ta kasa,ai bai kamata qasa ta gaza ba" Ta bawa fu'ad amsa. Ya fahimceta sarai,ya kuma fahimci anni dasu take shida farouq......kai tsaye ma idan an tashi shi din za'a ce,don dama farouq din dab yake da bayyana nemansa gasu annin,shi dinne bashi ga tsuntsu bashi ga tarko,bai kuma san ranar da zaiyi tsuntsu ko tarkon ba,don a yanzun baya jin duk yarinyar da yace zaya aura din zai iyayi mata adalci,don a qasan ransa ko digo baya jin marmarin aure,baya ma taba hange ko hasashen gashi da macen auren ko gashi a sunan magidanci......duk da cewa shi kansa shaida ne akan jikinsa yakai geji yakai iyaka ya kuma kai maqurar buqatuwa zuwa ga diya mace......duk da tarin yanayin da yakan tsinci kansa a ciki.....shi kansa yasan kowacce irin lafiya ake da buqata yana da ita,don ba'a maganar cikakkiyar lafiya ma ga mutum ma'abocin motsa jiki. To amma baisan dalili ba.....ko kadan sabgar bata gabanshi,hasalima!,zai.iya cewa bai taba jin soyayyar wata 'ya mace a zuciyarsa ba......bai taba daga idanu ya kalli wata mace yaji ta burgeshi ba......bai taba zama koda da minti daya ba....kaf rayuwarsa tunda ya mallaki hankalinsa wai yayi imagining aure cikin rayuwarsa ba. A yanzu ya sake gina rayuwarsa bayan ginin da yayi mata shi yafi sawa a gaba,aikinsa kasuwancinsa da sana'arsa sune budurwarsa kuma matarsa,baya da wani buri a yanzun illa ya sake zama gwani ta fannin ayyukansa gaba daya.

*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*

*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*

*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*

*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*

*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*

*ZAFAFA BIYAR*

*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*

*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*

_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_

_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_

_K'ALBIM Mamuhghee_

_AJIYA A DUHU Billynabdul_

_DUNIYATA Huguma_

_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_

*hudu 2k*

*uku 1500*

*Biyu 1k*

*Daya 500*

_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_

*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*

*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*

*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*

*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*

*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*

*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*πŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺ

89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf

*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*

*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*πŸ₯°πŸ₯°


*D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

PAGE 45

________________________
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX

*_assalamu alaikum warahmatullah_*

*_kina ta ganin kaya kala kala online?,kinason siya amma kina tsoron damfara?,tsada ko rashin ingancin kaya?_*

*_wannan tsoro da taraddadi ya yanke miki indai da HUGUMA CLOSET_*

*_muna da nau'ikan kaya kala daban daban bisa farashin da ba kowanne dan kasuwa ke iya bada kayansa akan hakan ba_*

Shadda
Laces
Atamfa
Kayan yara English wears dana jarirai
Qawatattun handbags
Mayafai
Abayas da jallabiyas
Inner wears
Huluna na maza da mata yara da manya socks
Takalma na maza da mata yara da manya
Lafayas
Sarqoqi agoguna banguls da rings

_kai komai daya danganci kayan ado na fita kunya wa dan adam_

_bisa farashin da zaiyi daidai da buqatarka_

*_Me kike jira sallah na gabatowa?,ana can ana ruwan suturu daidai da qarfin kowa?_*

*_masu manyan qarfi da matsakaita?_*

*_ki dinga siya da kadan kadan kina saka kudin kina tara abinki har sukai sanda zaki karba?,ko ki siya lokaci daya a kai miki_*

*_muna aika kaya ko ina a duniya in sha Allah_*

*MUNA BONONZA LOKACI LOKACI NA DUKA ABINDA RABO YA TSAGA*

*_MASU REPOSTING DA MASU SARI DUKA BA'A BARSU A BAYA BA,KI SIYA KI SAIDA KI SAMU RIBARKI HANKALI KWANCE,BA TARADDADIN INGANCIN KAYA KO WANDA KIKA BAIWA KUDINKI_*

*_KIYI JOINING KI TURAWA 'YAN UWA DA ABOKAN ARZIQI_*

*_INGANCI RAHUSA GASKIYA DA AMANA SHINE TAKENMU_*🫢🏽🫢🏽✌🏽✌🏽✌🏽✌🏽
__________________________


Yana da matuqar karsashi da qarfin zuciya......da kuma fuskantar dukkan wani goal nashi har sai ya cimmasa ya kaishi qasa. Baya taba bari buri tsoro ko fargaba suyi masa iyaka ko shamaki......faduwa kuma bata sanyashi yayi giving up,wannan shine sirrin nasarar da kullum yake dada samu.

Za'a iya cewa kai tsaye farouq hannun damanshi ne,don haka ba wani motsi ko mission nasu da dayan bai ganewa koda bai gayawa daya ba,duk da cewa ma babu boye boye gaba daya a tsakaninsu. Wannan ta sanya farouq ya jima da fuskantar fu'ad,idan magana kake ta aure ko soyayya to kada ma ka fara kiran sunanshi a ciki,domin baya gane komai ta wannan bangaren. Yakan jima yana dubansa cikin mamaki,ya bawa kasuwancinsa lokacinsa da rayuwarsa fiye da komai baya ga familynsa,wato shi sadiq musaddiq anni da abba,kullum lissafinsa da target dinsa moving forward.....moving to the next step. A hankali ya fara zolayarsa don gane gejin yadda idanunsa basa gane kowacce halitta da ake kira da DIYA MACE,sai ya sake karatun nasa da kyau yadda ya kamata,har daga qarshe ranar yakai kusan biyu na dare saman system yana duba wasu sabbin diamond da aka samu nasarar cirowa,yadda zasu sarrafashi da kuma kamfani mafi dacewa da zasu kai.

Shi kam har yayi bacci ma kai na biyu ne,ya fito main parlor na sassansu ya sameshi zaune dungurgur saman sofa yana fama da zazzafan coffee don hana idanunsa kamuwa da bacci. Farouq din da mamaki yake kallonsa,saidai baice masa komai ba har sai da yaje fridge ya ciro ruwa me sanyi ya dawo gefansa ya zauna

"Sannu bawan kasuwanci" Ya fada cikin gatse,gatsen da bai damu fu'ad ba saima maida idanunsa kan ruwan hannun farouq din da yayi. Har ya dauke idanunsa kamar bazai magana ba cikin dabi'ar nan tasa ta shariya da banzatar da abu,sai kuma ya dawo da dubansa kanshi.

"Kana da jarabar son aure.....amma kana kashe kanka da abubuwan banza da wofi.....kana namiji me yake hadaka da kayan zaqi da sanyi?" Yayi masa tambayar fuskarsa a hade yana duban idanunshi.

Qaramar dariya farouq din ya saki yana qoqarin bude gorar hannunsa

"Kasan me?,nifa bazan iya rayuwar da kakeyi ba,duk wani abu me dadi ka haramtawa kanka ci sai d'ai d'aiku,ka tattaro abubuwan da sam basu da dadi ko dandano a harshe kullum dasu kake mu'amala......yanzu kalla don Allah" Ya fada yana nuna tray din gaban fu'ad da awannin baya kadan ya gama amfani dashi.

"Gasashen zaitun.....hadin salad me man zaitoon,shayin ginseng,wolf Berry smoothie.....meye mai dadi a ciki?" Ya fada yana yamutsa fuska.

Idanu kawai fu'ad ya zuba masa har yakai qarshen zancan. A nutse ya saki wani qaramin murmushi da bai bayyana ba yana dauke idonsa daga kan farouq

"Dukka abinda ka lissafa yanxun kaje kayi binciken amfaninsa ga jiki da lafiya" Ya amsa masa yana jawo wata takarda dake aje a gefansa yana son hadesu waje daya da stapler.

Kai ya girgiza yana tabe baki

"Wanne amfani zan tsaya dubawa abinda basu da dandano ko kada......kaifa a taqaice ko?,bakasan meye dadi ba kwata kwata wallahi"

"Tashi don Allah ka tafi mr ciye ciye karka cikamin kai da bayanai.....kaci gaba da ciye ciyenka yadda kake da hazaqar son kayi aure,auren zai baka amsarka". Dariya ta kubcewa farouq din harda buga qafa tamkar ba dare ba

" To mijin aljana.....don dai na tabbatar zaiyi wahala kaidai idan aka kira me ruqiyya yayi maka ruqiyya inajin mata hudu gareka cikin jinsin aljanu".

Duk yadda yakai ga pressure dinsa hade rai ko salon miskilancinsa farouq kadai ke saukeshi. Ya addabeshi wasu lokutan har yaji kamar ya makeshi amma ba yadda ya iya dashi,don kaf duniya baya gashi ba wanda yake masa karan tsayen da yake masa irin haka. Ko a yanzun ma sai da yayi silar fitar murmushi daga kyakyawar fuskarsan nan ma'abociyar tsukewa da ba kasafai ta fiya fidda fara'a

"Kaga bakina alaikum na huta ai.....don wadannan matan na bil'adama......." Sai kuma yayi shuru ba tare da ya qarasa fade ba. Ba kasafai ya fiya son tona abinda ke danqare a zuciyarsa ba,baisani ba ko Allah ya nufeshi da rahama daya zare son aure ko son mallakar mace kwata kwata daga zuciyarsa ba?.

Dan kadan farouq ya kalleshi ta gefan idanu ganin ya dauko magana ya kuma katseta,sai shima yayi shuru kawai bai sake cewa dashi komai ba.

Tun daga wannan lokaci idan yaso masa tsiya da shaqiyanci yakan kirashi da mijin aljana. Anni tayi tayi ya daina amma ina,lamarin farouq sai a hankali,mugun shakiyyi ne idan yaso,idan kuma ya sakaka a gaba ka saku kenan......amma kuma tamkar hawainiya yake,idan yaso canzawa zaka rantse da Allah bashi bane matsokanin nan ba.

Kusan a tare suka amsa sallamar farouq din

"Kana nan dama?" Farouq din ya fada sanda ya qaraso dining din yaja kujera dake tsakiyarsu ya zauna yana tattare long sleeve din shirt din jikinsa sama.

"Yana nan sunatayi shi da mutuniyar" Anni ta bashi amsa tana dariya qasa qasa.

Baki ya tabe yana bubbude warmer din dake jere kan dining din

"Wannan autar taki anni taci kai wallahi.....wai ita an gaya mata zama zamuyita yi da ita a gidan nan?,baka gaya mata gaskiya wallahi" Ya qarasa maganar yana duban fuskar musaddiq cikin salo na harara.

Dariyar ta kubcewa musaddiq ya kalleshi da kyau yana daidaita zamansa idonsa akan farouq

"Yanzu don Allah BB(big brother suke masa abbreviation),so kake ayita kada mata hanjin ciki?,duka duka amna nawa take?"

"Allaaaaahu akhbar.....kaga masuyi don Allah,dama kana cikin masu lalatata a gidan nan......don Allah kayita gaya mata damu zata rayu.....Allah ka sakata ne kawai a keken bera......itafa har yanxu bata da hankali na lura......na godewa abba ma da yace sai taje ta raka nanna......tafiya duka duka sati biyu kawai amma ta cika mutane da qorafin yhan yhan yhan......itafa gida zata dawo waye ya mutu waye ya tashi.....shi kuma wancan mijin aljanar yana can yana sake daure mata qarqashi...."

"Farouq?" Anni ta tsaidashi tana dubansa

"Sunan nan bazai fita a bakinka ba ko?" Ta sake jefa masa tambayar tana dubansa.

Gyara zamansa yayi yana wani tsuke gira,shi ala dole yana son zama serous.

"Allah dai ya bada haquri anni......amma shima ai anni ba sunan da yafi dacewa dashi sai wannan.....banga alamar lafiyarsa qalau ba" Ya qarasa fada qasa yana fara serving kanshi da abincin da yafi so. Idanu anni kawai ta tsura masa tana kallonsa ba tare da tace komai ba,ita kanta yadda fu'ad keyi da lamarin yana tabata,ko a fuska ko kuma a aikace bai taba damuwa da ganin dukansu su ukun suna shirin yin aure ne su barshi ba,yana shiga dashi akayi dukka maganganun da zaayi da iyayen yara,amma shi yana zaune ba wani damuwa a gabanshi,saima lissafin yadda zaici gaba da juya kwabo ta koma dari.

"Kaga MAN.....ka koma gaya mata gaskiya,aurar da ita zamuyi da wurwuri.....ba zancan yin PHD a gidan nan.....munason ganin jikokin 'yar uwarmu mace". Daga anni har musaddiq ba wanda farouq din bai bawa dariya ba ganin yadda yayi maganar da gasken gaske har yana tabo

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login