Showing 42001 words to 45000 words out of 557259 words

Chapter 15 - πƒπ”ππˆπ˜ATA BOOK1 AND 2 HAUSA NOVEL

HUGUMA   

03 Nov 2025

431

juyawa zuwa dakin nasu da gaggawa tare da mantawa da niyyar fita zuwa tsakar gida da takeson yi.

Zama tayi sosai saman gadon daga gefe. Locker gadon dake hannun damanta wadda ba kasafai ta fiya budeta ba ta bude. Tarin tarkace ne a idanun mai kallo,amma a wajen sabreen wasu ajiyayyun abubuwa ne dake da tarin muhimmanci da amfani a wajenta a mabanbantan lokuta. Har ma idan ka tambayeta a wani lokacin tana iya ce maka SUNE SABREEN.

mitsitsiyar akwati ce wadda bata fi girman akwatin sanya zobe,ta saka hannu ta daukota sannan ta bude. Wani qaramin layi ta ciro ta rufe akwatin ta maidata,sannan ta dauki wata farar qaramar Samsung's ta bude gefanta ta zura layin ta maida wajen ta rufe sannan ta danne madannin dake gefen damanta. Take ta kawo haske,bayan bayyanar tambari da sunan kamfanin komai ya dawo daidai yadda ya dace.

Batakai ga danna komai ba saqonni suka fara turmutsutsun shigowa. Tsai tayi da idanunta tana kallon notifications din har suka gama jerin gwanon shigowarsu suka qare. Kaman ta sharesu ta isa kai tsaye ga abinda zai sadata da mashkur sai kuma ta sauya tunani.

Ma'ajiyar saqonnin ta shiga,ta fara bin sunayen mutanen da suka aje mata saqon daya bayan daya don bata jin tana da isashen lokacin da zata tsaya budewa da karantawa.

Kamar yadda ta zata,ta samu saqonnin mashkur da yawa fiye dana kowa,saita wuce kowanne saqo ta tafi saqon daya tura mata na qarshe kwanaki biyu da suka wuce.

Sallamarsa kadai ta amsa,ta tura masa ta maida wayar ta aje saman locker tana bin fuskar wayar da kallo,zuciyarta na shirya mata yadda komai zai tafi.

Ta jima da ajjiye mashkur saboda yadda zalamarsa ta fito a fili. Ta jima da ganin ta barshi a gefe saboda yadda halinsa yasha banban dana kowa cikin mutanen da ta taba tarayya dasu cikin rayuwarta. To amma yanzu silar matsalar aisha tana ganin wannan shine right time da zata koya masa darasi shima yabi sahun sauran mazan da suka shude cikin rayuwarta.

Agogon dake manne saman kanta ta kalla tana qoqarin dawo da nutsuwarta waje guda. Zuciyarta ke wani irin rawa tamkar dai ta soma gajiya da al'amuran da suke tunkarota cikin rayuwa. Wasu su shude,wasu kuma suna ci gaba da fuskantarta da babbar BARAZANA.

kamar mintuna goma sha biyar sun qaru akan lokacin dawowarsu daga islamiyya na ainihi. Aje dubanta tayi saman hijabinta na sallah,saita miqa hannu ta dauka tana miqewa da zummar duba inda suka maqale. Bata wasa da duk wani abu da ya shafesu musamman fita da dawowarsu gida. Duk da su din kwata kwata basu san ko ina ba idan ka dauke hayoyi da layukan dakan sadasu da makarantarsu.

Kaman jira akeyi tayi taku uku daidai wayar ta dauki ringing. Duk da ta jima bataji ringing din wayar ba amma babu abinda ta manta daga sautinta.

Taku ukun ta sakeyi ta dawo tana duban wayar bayan zuciyarta ta gama ayyana mata waye din me kira

"Mashkur" Kaman yadda ta aje number dinsa. Siririn murmushin da bata shirya ba ya subucewa labbanta. Tana tsaye tana ci gaba da duban wayar har ta qaraci burarinta ta yanke. Bata da niyyar daga kiran kwata kwata a yanzun,don ba tsarinta bane samun komai daga wajenta cikin sauqi ba. Ta yardarma kanta tana da tsada,tsadar data sanya kowanne namiji da zai ratsa ta cikin DUNIYARTA yarda da hakan,ya kuma bita da tsarinta a yadda ya sameta.

Kaman yadda ta zata bazai kira sau daya ya bari ba haka taji wayar ta sakeyin qara,salin alin ta koma ta maidata silent,sannan ta jawo Locker ta wurgata ta rufe ta kuma soma takawa hanyar falonsu tana zura hijabin saman wuyanta. Shimfidadden kwarjinin dake boye bayan fuskarta ya sake bayyana sosai tamkar ta sanya hijabin ne don ado ba domin biyan buqatarta ba.

Slippers dinta masu taushi ruwan hoda dake daga bakin qofar da zura ma fararen qafafunta,ta murda handle din qofar ta bude ta tura ta fito.

Fayau tsakar gidan nasu yake da wadataccen filin nan da baya rabo da tsafta duk da iyalin da gidan ke qunshe dashi. Kamar kowanne lokaci kamar kuma yadda suka maidata ABUN KALLO. Kowanne motsinta yana saman idanun mafi yawa daga cikinsu,bawai don su bata kulawar data dace ba....bawai don suyi mata gyara idan tayi kuskure ba......badon kulawa ta qauna ba.......saidai don wani radin kansu da biyan buqatar qashin kansu.

Tana da wani irin kaifin nazarin fahimtar meke kai kawo a kewayenta. A zaune take ko tafiya take?. Wani yanayi da a baya baya cikin dabi'unta,kuma bata dashi,amma yanayi da salon rayuwa ya tilastata kasancewa hakan.

Dab da rijiyar gidan wadda daga ita sai hanyar da zata sadaka da ainihin farfajiyar gidan ta ganta. Tsaye gaban rijiyar dauke da cup da alama ruwa ta gama sha.

Sanye take da atamfa classic da aka yiwa dinkin zamani riga da skirt daya zauna daidai jikinta. Kanta ba dankwali wannan zai baka damar hango baqar sumarta me sulbi da suka gada ainihi daga mahaifinsu.

Idanunsu cikin na juna na wasu sakanni,sai ta fara janye nata duban daga kanta tana ci gaba da nufar soron.

HADIYYA......Idan har a baya za'a gaya mata rayuwa zata ajeta a bigiren da suke kai a yanzun ita da ita zata qaryata......idan har a baya za'a gaya mata rayuwarsu zata koma kaman yadda take a yanzun zatace mummunan mafarki ne mara ma'ana....wanda bashi da tushe ballantana makama.

Hadiyya 'yaruwar haihuwarta,wanda mahaifi yayi silar zamowarsu jini daya......hadiyyan da suka taso qarqashin rainon mahaifiyarta......cikin daki guda saman shimfida guda,duk da murdadde kuma zazzafan kishin da mahaifiyarta ke bazawa.......amma hakan bai sauya komai ba na kusancinsu.

Sai gashi a yanzun sunyi irin rabuwar hannayen riga. A yanzun haka tana nata karatun cikin makarantar koyon aikin jinya bisa daukar nauyi da kulawar yayan mahaifiyarta......yayin da tata rayuwar tayi matuqar shan banban da ta hadiyyan.......take neman ta nutse cikin neman dauki da tallafin data gaza me kawo mata,har sai da tayi wani irin wawan tsalle da batasan zata sauka a daidai ko kuma garin saukar tana iya gamuwa da karaya da tarin raunukan da zasu zamewa rayuwarta tabo?. Takai qarshen tunanin sanda takai bakin qofar farfajiyar gidan ta farko,saita aza tafin hannunta saman fuskarta tadan shafi fuskar. Tasan bawai kuka takeyi ba,don a yanzun batajin cikin qwayar idanunta akwai sauran ruwan hawayen da suka rage da zasu bata hadin kan yin kuka. Kawai huci da dumin da fuskarta ya dauka takeso taji ya huce,idanunta sake mata dan zugi zugi tanason rage musu adadin iskar dake shiga cikinsu.

Karo sukayi da huda sanda take shirin fita shigowa su suna shirin shigowa. Suka ja baya dukkansu hudan tana dan riqe goshinta

"Ke kuma ina kuka tsaya haka dukka ku ukun har ana shirin kiran salla?" Ta jefa mata tamabayar tana tsareta da ido. Kafin huda tace komai haneefa ta tsinke da dariya

"Anty.......yaa nadra muka tsaya jira......bata bada hadda ba sai malam ya tsareta" Idanunta ta mayar kan nadra wadda fuskarta ke a daure

"Garin yaya?,kin soma wasa da haddar ne?" Kai ta girgiza da sauri,tana shirin magaa hudan ta rigata

"Kallo suka tsaya yi jiya da daren bayan kin kwanta" Fuska a daure ta sake maida kallonta a kansu

"Ashe?,yau zaku jawa kanku,sai na tsinke kowanne cable na kallo dake dakin nan"

"Ah wai.......ni abunnan yana dauremin kai?,wai lalatacce shike tarbiyya" Murya bibo ta ratsa kunnuwanta sanda take dubansu nadra.

Dukansu ido suka azawa bibo din lokacin da take kutsowa cikin gidan. Kaman yadda suka fita ne dazu,ita da daada,saidai kaman dazun ma daada ratsewa tayi ta wuce abinta ba tare data tsaya yiwa bibo tayin su wuce ba kamar dazun.

Motsawa kadan huda tayi wanda motsinta kadai ya sanar da SABREEN abinda take shirin yi. Yatsarta ta kada mata sautin da ya sanyata tsaiwa can tare da hadiyar wani abu me tauri a wuyanta



*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*

*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*

*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*

*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*

*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*

*ZAFAFA BIYAR*

*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*

*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*

_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_

_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_

_K'ALBIM Mamuhghee_

_AJIYA A DUHU Billynabdul_

_DUNIYATA Huguma_

_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_

*hudu 2k*

*uku 1500*

*Biyu 1k*

*Daya 500*

_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_

*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*

*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*

*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*

*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*

*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*

*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*πŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺ

89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf

*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*

*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*πŸ₯°πŸ₯°


*D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

*Arewabooks:@Huguma*
https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997

PAGE 26
__________________________
*_ALBISHIR A GAREKU!!_*

*_SHIN KUNSAN UMMUMAHNOOR LUXURIES TA TANADAR MUKU INGANTATTUN KAYAN ADO NA FITA KUNYA KUWA?_*

*_KAMAR SU_*

Atamfofi
Laces
Shadda
Materials
Takalma
Jakunkuna
Mayafai
Trolley
Sarka da dan kunne
Oil perfumes

*_karki tsaya sanya har ayi babu ke,maza garzaya ta nan_*

Numbers
08034469681
08135142610

Handles
Instagram @ummu_mahnoor_luxuries
TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries
Facebook ummu_mahnoor_luxuries

*_inganci da kwalliya shine muradinmu_*
__________________________


"Ku wuce muje" Sabreen tace dasu,suk sai sukayi gaba tana biye dasu a baya. Nadra ta hadawa kayan duka ta wuce musu dashi daki. Ita tayi tsaye dasu kowacce ta gama buqatarta suka daura alwala suka wuce daki.

Sallah sukayi bayan sun sauya uniform. Har a sannan tana ankare da yadda huda din keta hadiyar zuciya. Ta sani muddin tace zata saki huda tayi abinda takeso zaman bazaiwa kowa dadi ba......tafi huda zuciya nesa ba kusa ba......tafi huda dabi'ar take yanke.....amma me?,daga baya ta fahimci me irin wannan dabi'ar ba kasafai yake nasara ba.

Sai data kammala sallar magariban sannan tabi takan wayar. Ta samu miscal biyar hade da wasu saqonnin daga gefe. Tabi number tasa da kallo,sai a yanzu takejin ta shirya saurararsa. Kamar yasan tana riqe da wuyar saiga wani sabon kiran ya sake shigowa,don haka ta miqe a nutse ta koma daki tana matsawa daga inda su nadra dake cin abincin dare suke.

"Laifin me nayi dana cancanci wannan uqubar fateema?" Numfashi ta saki wanda sautinsa ya isa har kunnensa

"Ki gayamin ko meye nayi a shirye nake da na nema afuwa" Shuru ta sakeyi tamkar bata layin,saidai tana sauraren dukka maganganunsa

"Fateema" Ya sake kiranta da sunan da shine nasa STAMP din,sunansa ne shi daya,duk duniya shi ta mallakawa wannan sunan

"Naam" Ta amsa a karon farko tunda ya fara maganar

"Kinsan irin rayuwar dana tanadar miki?,kinsan irin gatan da nakeson miki?,kinsan yadda nakeson maidaki tauraruwa a cikin mata?,kinsan yadda nakeso ki koma tamkar sarauniya?"

"Dukka wadannan dama abinda ka lissafa basu nake da buqata ba"

"Me kike da buqata fateema......ki gayamin,a shirye nake na mallaka miki su......"

"Zamu iya haduwa?" Ta jefa masa tambayar

"Ko a ina nake a duniya a yanzun haka kika ce kina buqatar ganina zan wanzu a gabanki" Maida idanunta tayi ta lumshe sannan ta budesu

"Mu hadu yanzu fateema?,ko dan kadanne inaso naga fuskarki"

"Alright" Ta amsa masa a taqaice,abin da yazo masa a bazata,don haka a rude yace

"Venue?"

"Zan gaya maka,i will call you" Bata sake bashi daman cewa komai ba ta yanke kiran.

Wayar ta riqe a hannunta tana juyata a hankali bayan ta zubawa guri daya idanu. Lissafi ne fal Qwaqwalwarta,dole kafin ta samu abinda take nema saita yi haquri ta sake masa,dole ta dinga bashi mabanbantan gurare har zuwa sanda tsarinta zai fada aikinta zai cimma nasara.

A nutse ta miqe tana wassafa yadda zata fita yau din da dare,abinda sam ba dabi'arta bane saiya zama mugun dole,ba kuma zata iya tuna lokaci na qarshe da hakan ya taba faruwa da ita ba,amma yanzun dole ta fitan,tanason ta amintar dashi sosai a kanta.

Kai tsaye ta wuce ma'ajiyar kayanta tana duba suturar da zata dace da ra'ayinta a wannan lokacin. Da idanu ta gama qare musu musu,daga qarshe ta tsaya saman wasu Turkish dress masu strip skirt long sleeve shirt da doguwan kinomo sai madaidaicin veil da zai lullube saman kanta.

Sam bata da ra'ayin sutura me matse jiki duk kuwa da yadda mutane da yawa suke kallon ita tafi dacewa da irin wannan shigar.

Tsaf ta shirya cikin kayan kalolin navy blue da gray color. Sanda ta gama nada veil din a kanta sai data sake duban kanta sosai ta cikin madubin. Tayi wani irin sassanyan kyau me matuqar daukar hankali. Ta miqa hannu a nutse ta dauki turarenta ta feshe jikinta can qasan ranta tana jin fargaba kadan kadan kan haduwarta da mashkur,saidai kuma wani sashe na zuciyarta yana qarfafa mata gwiwar ba komai,wannan ne haduwan farko,nothing will happen.

Asalin wayarta ta jawo tana lalubar number JIB. bugu daya tak ya dauka,tadan motsa bakinta a nutse

"Ina fatan kana available kuma free"

"Ko ba hakan bane ai ya zama dole nayi creating time wa ke.....me kike buqata?"

"Connection" Ta fada a gajarce

" A daren nan?"

"Haka abun yazo,mashkur......mashkur alqali abdulkreem"

"Done.......wancan aikin ya kusa kammala......akwai ragowar information dana kasa accessing.....but...."

"Karka damu.....mu sanya wancan a mala.....wannan din shine yafi muhimmanci a yanzu"

"An gama.....bani code......let me write it" Ya fada yana dan riqe wayar kadan kafin yace

"Okay.....karanto" A nutse ta karanta masa wasi gajerun lambobi guda uku sannan ta katse kiran. Ta jawo locker madubinta ta ciro Bluetooth tayi danne danne saman wayar tata ta bada wasu sakanni sannan ta maqala a kunnenta. Saita aje wayar,ta dauki wancan Samsung din ta kunnata sannan ta fara yunqurin kira.

Bugu daya tak tayi aka daga,ta kalli wayar da mamaki sanda yake cewa

"Am ready to go princess......ina zaune a mota nida driver a parking lot na gida"

"Yayi.....but if possible ka taho kai daya mana"

"An gama" Ya amsa mata cikin farinciki hankali kwance.

Tana kammala saka takalma huda na shigowa dakin. Kallo daya tak tayi mata taga yanayinta ya sauya. Hudan tadan ritsata da idanu tana dubanta,saidai tun kafin takai ga tambayarta ta bata amsa

"Zan dan fita kadan amma yanzu zan dawo" Iya abinda ta gaya mata kenan ta fara takawa zata fice.

A jikinta taji yarinyar kallonta take,a jikinta taji tana tsaye ne kawai har yanzu,don haka ta tsaya cak sannan ta waiwayo. Ido suka hada,sai a sannan hudan ta kauda kanta. Iya hakan ya gayawa Sabreen maganganune sosai cikin zuciyarta,wataqila girma da kimarta kadai zai hanata ta furta mata su. Taku hudu tayi ta iso gaban hudan

"Dole ce ta saka zan fita huda......amma bazan wuce awa daya ba,idan na dade biyu"

"Amma anty...." Hudan ta furta fuskarta fal damuwa.

Yatsanta ta dora saman lips tana duban hudan,sai kuma daga bisani ta dauke yatsan tana aza dukka hannuwanta saman kafadarta,ta kuma zaunar da ita saman stool na madubin dakin

"Ke daya ce tal cikin mutanen da sukasan wace Sabreen gaba daya baya,kada kiyi tunanin na canza......ban canza ba huda.....kuma har abada bazan canza ba.....nayi alqawari......mommu da abba dake qarqashin qasa bazan bari suyi kaico dani ba" Kai ta gyada a hankali tana kallon Sabreen kamar yadda itama ita din take kallo. To amma a hankali tana rasa wannan yardar wanda tasirin maganganu daga kowanne saqo da lungu na layinsu dama unguwarsu ke kai kawo a kunnuwanta

"Don't lose hope huda......alqawari na.....bazan karyashi ba,ki kula da nadra da haneefa" Ta fadi mata daga qarshe ta juya tana fita a dakin. Nata ruhin yana motsuwa.

Har abada ba zata

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login