Showing 129001 words to 132000 words out of 557259 words

Chapter 44 - πƒπ”ππˆπ˜ATA BOOK1 AND 2 HAUSA NOVEL

HUGUMA   

03 Nov 2025

562

Saqon ya shigo mata sanda take daura agogon hannunta ne,tun taga sunan tasan shine,bata bi takai ba sai data gama daurawar,ya qara barima a kunnenta tayi Rolling mayafin Turkish dress din,ta kuma jawo kimono din kayan da suke zuwa tare da shirt me dogon hannu da skirt din ta aza saman kayan sannan ta dauki wayar ta bude tana maida masa amsa

"What's the adress?.....zan taddaka har inda kake don farincikinka".

Sai data maimaita karanta saqon kusan sau hudu,tana mamakin yau itace da kanta zata turawa wani d'a namiji saqo da yayi kama da wannan?. Ji tayi kaman ba zata iya turawar ba,ta aje wayar saman madubi tana furzar da iska daga bakinta

"No way out" Taji zuciyarta na gaya mata,dole ta tura muddin tanason cika mission din. Tana so ta rabu ne da mikail.....ba kuma zata iya barinsa salin alin ya wuce hakanan ba,sai ta miqa hannunta ta sake bude wayar,ta danna send sannan ta maida wayar ta ajiye.


*D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

PAGE 69


Bayan maimaita karanta saqon da yayi,har sai data kaishi ga murza idanun nasa don ya tabbatar daidai ya gani ko kuwa akasin hakan?.

Jikinsa har rawa yake wajen maida mata reply,har bai lura da yadda Muhammed jadda ya zuba masa idanu ba yana karantar yanayinsa.

"Mr mika'il" Ya kirayi sunansa da husky voice dinsan nan dake ratsa zukata su kuma maida hankalin mutum zuwa jikinsa.

"Yes.....yes sir" Ya fada adan daburce yana qoqarin tattara masa nutsuwarsa bayan ya tabbatar da isar saqon zuwa wayarta. Bawai address kawai ba,harda code da zata samu zarafin bude office dinsa ta shiga ta zauna tayi tsimayensa.

Murmushine ya subuce mata da ganin yadda ya bata komai in details. Ba wani shakka ko kokwanto. Wato shi namijin bariki akan mace susutacce ne?.....sannan fiye da rabin maza ta fuskanci ba kasafai suke iya mallakar kansu ba idan batu ake na mace. Wani zaka hangi fuskarsa cike da kamala amma muddin aka raba masa mace a nan dukka rauninsa yake bayyana. Bai tsoro shakka ko kwanton ita din fa baquwa ce cikin rayuwarsa gaba daya?.

"Good job mika'il" Ta fadi murya can qasa tana forwarding ma JIB komai.

"Kana tare damu?" Muhammad jadda ya sake jefa masa tambayar yana dage girarsa dukka biyun

"Yes.....yes sir" Ya fadi yana sakar masa murmushi don ya amintar dashi. Idanu yadan tsareshi dashi kaman meson karantar wani abu,wanda duka duka cikin mintuna biyar ya dauke idanun yana cewa

"Bismillah" Tare da maida idon nasa saman farar takardar gabansa da daya daga cikin ma'aikatan ya gabatar.

Sai da yayi namijin qoqarin daidaita nutsuwarsa sannan ya fara gabatar masa da komai daki daki.

Sai data buda qaramar handbag dinta ta tabbatar ta sanya komai a ciki sannan ta fiddo dubu biyu a ciki ta miqawa huda dake tsaye a gabanta

"Masu kamfanin pure water zasu kawo ruwa....ki basu wannan idan sun kawo.....naso saikun wuce islamiyya kafin na fita.....amma it's urgent.....kiyi qoqari ku fita da wuri kada kuyi latti"

"A dawo lafiya" Ta fadi bayan ta karbi kudin. Qasan ranta fal farinciki,a yau din zatayi hira da hameed yadda ranta keso,don zata saitawa su nadra hanya zuwa islamiyya ne ita kuma ta baje kolin soyayyarta yadda ranta yakeso.

Gaban haneefa ta qarasa tana sakin murmushi,itama haneefa din murmushi ta saki,hannunta ta dora saman sumarta data cirewa dankwali. A kullum fuskar haneefa ba wanda take tuna mata dashi sai umminsu. Akwai shaquwa da sabo me tsanani tsakaninsu.......amma duk da haka saida mutuwa tayi aikinta ta raba tsakaninsu.

"Ayimin addua auta....zan kawo miki abun dadi"

"A dawo lafiya yaa sabreen........amma yau kam sabuwan teddy nakeso ki sayamin"

"Ke kuwa ki rasa abinda zaki zaba sai Teddy?" Nadra ta fada tana qyalqyala dariya

"To madam tsokana.....ba ruwanki" Sabreen tayi hanzarin katse nadra data wuce daki tana ci gaba da dariyar tsokana din hadi da yiwa sabreen a dawo lafiya.

Tana takawa don fita daga layinsu ta isa bakin titi amma tunanin qannen nata ne a ranta. Batason ko kadan yadda kullum sai ta fita ta barsu,wani lokaci su fita tare saidai su rufe dakin,harma wasu lokutan su rigata dawowa. A yanzun huda tafi tsaye mata a rai,tunda har ta cika shekara sha biyar ta shiga ta sha shida tana da buqatar sanya idanunta a kanta,don mataki ne da komai daga nan yake farawa daga rayuwar yarinya. Duk da inda ace ita din me gata ce,ita dinma tana buqatar kulawa ne tare da qarasa rainon tarbiyyarta.

Ko kusa ko alama bata lura dashi ba,don tayi nisa a tunaninta,sai muryarsa taji daga gefanta.

"Um uhmmm......sai ina kuma haka?" A nutse ta waiwaya tare da sake rage yanayin tafiyar tata tana kallonshi.

Tsaf yake kallonta,ya turo hula gaban goshinsa yana mata wani irin kallo. Idanunta ta dauke don bata buqatar yanayin kallon da yake binta dashi. Ta sani haushinta yakeji qwarai,tun waccar ranar data hanashi kudi. Wannan duka ba damuwarta bane,don idan da sabo ta saba,sai ta watsar da wannan batun kamar kullum tace dashi

"Barka da warhaka kawu.....an yini lafiya?"

"Ras na wuni.....ko kin dauka zan mutu ne saboda kin hanani kudinki?,to kisha kuruminki 'yar nan......cikin satinnan da yardar me duka arziqi zai fashemin......sunana zai fantsama a duniyar masu arziqi......daga sama'ila zan koma alhaji ismai'il sha maka Allahu". A mamakance take kallonsa,tadai sani bashi da wata sana'a data wuce caca,kuma muddin ka jishi yana lissafin maquden kudade irin wannan to wata caca za'a buga kuma yake sanya ran zai cinye.

"Allah ya bada sa'a.....amma dai kawu.....caca"

"Akul naji bakinki.....dani dake ai dan juma ne da dan jummai... Ke har gwara ni duk tsiya".

Kanta ta dauke tana hadiye wani abu daya tsaya mata a wuya,bata sake tanka masa ba sai ta fara takawa tana barin wajen. Har tayi taku hudu qwarara ya qwala mata kira da ainihin sunanta

"Aminatu" Dakatawa tayi don ba zata iya ci gaba da tafiya ba,ba'a canzawa tuwo suna,duk duniya kawu sama'ila ubanta ne.

"Ke wato baki jin ko dar idan an miki gugar zana ko?,to miqomin wani abu nan,ki rubuta shi a lissafi duka cikin satin nan zan biyaki" Ya fada yana miqa mata hannu tamkar ya bata ajiya. Idanu ta xuba masa,sai kuma ta sanya hannu tana sauke jakarta daga kafada,ta zuge ta fidda dubu dubu guda hudu ta miqa masa.

Karba yayi yana juyasu alamun a raine suke a wajensa,sai ya yatsina fuska

"Ki rasa abinda zaki ban sai wannan?,kai Allah ka dawo mana da arziqinmu za'a sha kallo wallahi......" Daga haka ya juya yana cusasu a aljihu tare da barin gurin bai kuma sake bi takan inda zataje din ba.

Kasa ci gaba da tafiya tayi har sai daya bacewa ganinta,ta kada kai ta na yin gaba kamar kullum zuciyar nan cike da nazarin rayuwa . Tun daga rasuwar mahaifinsu har ta mahaifiyarsu bai taba miqo komai yace musu gashi ba wai don su rayu.....amma ita ba zata iya qirga ko lissafa adadin sau nawa ya karba daga hannunta ba,kuma a raine,ba godi bare na gode.

Ya riga ya bata shaidan da zata nuna na cewa shi take nema,wannan ya sanya bata samu matsalar shiga kamfanin ba tun daga gate din farko gate na biyu,ta zarce zuwa main entrance,ta ratsa reception da sauran guraben da kamfanin yake dashi kai tsaye kuma ta isa ga office din.

Tayi amfani da code din ya kuma bude mata successful. Ta tura qofan a hankali kamar me tsoron shiga qaramin murmushi na sauka saman fuskarta

"Quda a wajen kwadayi akan mutu" Ta furta qasa qasa tana sanya qafafunta cikin office din. Har ta fara takawa sai kuma ta tsaya cak tana wurga idanunta sassa sassa na qawataccen office din da aka narka kudi akayi masa wani irin lafiyayyen tsari me daukan hankali. Tabbas tasan babu yadda za'ayi guri irin wannan ya rasa CCTV camera,indai kuma hakanne ta yaya zata iya gudanar da komai ba tare data samu wata matsala ba?.

Dan wani abu cikin kunnenta ta matsa,muryar JIB ta bayyana,sai ta danja da baya kadan ta raba qafa tsakanin office din da veranda din da jerin gwanon office din yake don bataso ta fito gaba daya ko ta shiga gaba daya don kada camera din ya samu damar nunata

"Ni dakai duka bamuyi tunanin CCTV ba jib?".

"Ya salam" Ya fadi yana aje wani numfashi

"Haka ne......wasu lokuta dama kece ke mana hasshen irin wadannan abubuwan......ba matsala bane,manyan kamfanoni irin wadannan akwai irin cameras din da suke amfani dasu,katseshi ba zaiyi wahala ba nasan takan irinsu sosai......yanzu ki tsaya daga nan inda kike...kafin ki shiga ki gano mana daga wanne saiti camera din yake shikenan kawai"

"Okay....."

"....karki datse connection daga nan har mu gama aikin"

"So kaji komai tsakaninmu kenan bayan sirri ne?" Ta fada cikin dan salon zolaya da wani lokaci takeyi masa. Dariya ya qyalqyale da ita kadan yana fadin

"Tuba nake....Allah yabar soyayya". Sai kawai ta saki murmushi kadan tana tura qofar hadi da sake qarewa office din kallon tsaf.

Cikin qasa da minti goma ta gano komai suka kuma katse sadarwa da tsaida aikin camera din. Da dan hanzari ta ajjiye hand bag dinta. Tanaso tayi komai ne ta gama kada damar ta subuce mata yazo ya shigo.

Sai data tattara dukka hankalinta da nutsuwarta ta karanci inda komai yake ajiye a office din,gudun kada ta taba wani abu ta kasa maidashi daidai inda yake hakan ya nuna masa alamar tayi masa bincike. Hatta da biro dake ajiye qwaya daya tal saman teburin sai data karanci a yadda yake ajiye din,ta dauka ta kuma gwada maidawa ta tabbatar ya zauna kaman yadda aka ajiyeshi. Wayarta ta fidda,ta sake yiwa office din qaramin video komai da komai sannan ta maida wayar jakar,ta kuma shiga aikin bincika komai daki daki.

Baya ga abinda suke nema taga abubuwa da yawa cikin office din,irinsu condom dake nuna mata lallai riqqaqqen dan bin mata ne,taaba irin masu tsadar nan da sauran abubuwan maye. Abinda ya sake darsa mata mugun tsanarsa kenan,wutar kuma ta tabashin ta hanyar kwakwashe masa komai tana sake ruruwa cikin ranta. Ya zama dole ta durqusar dashi,durqusarwar da bazai sake tashi ba.

Maida komai tayi kaman ba wani abu daya faru a office din,ta tattare duk abubuwan da take nema din tayi musu ajiya ta musamman cikin jakarta. Hatta da wani qaramin ledar cake da akaci aka barshi sai data tabbatar ta maidashi yadda yake,ta gyara rolling dinta da kyau tana sauke numfashin samun nasarar kammala komai ba tare daya dawo ba.

Maqoshinta taji ya bushe tana da buqatar ruwa,sai ta taka tana nufar kyakkyawan fridge din dake girke waje daya.

*D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

PAGE 70


Turus tayi tana kallon yadda aka maqare gidan farko na fridge din da wasu kalan kwalabe da bata saba ganin irinsu ba. A hankali take dubasu har ta fahimci kwalaben na meye?.

Kwalaben giya ne tabbas,ta maida idanunta ta lumshe tana furta

"Innalillahi" Can qasan harshenta. Sai kuma taja jikinta baya a hankali tana matsawa daga jikin fridge din don batajin zata iya shan wani abun sha daya fito daga fridge din komai halascinsa.

Zuciyarta ke qara bugawa da tsanarsa haushi da kuma takaici. Shikam mikail dame zaiji?,abubuwan ai sunyi masa yawa,sun masa yawan da batasan wanne a ciki zai iya dauka ba. Kaman ana son bata amsar tambayarta sai qofar tayi qaramar qara alamun ana budeta ne,ba jimawa ya bayyana cikin office din yana dubanta da murmushi

"Am so sorry dear......ina fata banyi keeping naki da yawa ba......boss ne idan ya tashi aikinsa tamkar engine.......baya gajiya,na samu na kubota da qyar".

Idanunta ta dauke daga kan files din da yake rungume dasu,wanda ta tabbatar a cikinsa sauran bayanan da take nema suke. Ta kalato dukkan dauriyarta ta jefeshi da qaramin murmushi

"You deserve it ai....."

"Wow......serious?" Ya fada da wani irin zumudi da zakwadi yana qarasowa gabanta dab da ita ya zauna har yana neman hade gwiwoyinsu guri guda. A dabarance ta miqe da sauri,sai ya bita da kallo. Taji a jikinta yana kallonta ne don haka ba tare data juyo ba tace

"Bari nayi fitsari kadan"

"Oh....okay to dear" Ya fada yana dora files din saman table din cikin ransa yana qissima yadda a yau din zai gwangwaje,a yau din zai kashe duk wata qishirwa tasa dake damunshi a rai.....a yau zaiyi morewar da bayajin ko daren amarcinsa zaiyi wannan.

Gaban madubij toilet din ta tsaya tana sauke numfashi idanunta akan fuskartata. Muryarta can qasa tace

"Please jib.....muyi komai mu gama da sauri......banason ganin fuskarshi kwata kwata"

"I know.....zanyi iya qoqarina......amma please kada kice zakiyi halin hawainiyar nan taki" Dan murmushi ta saki,yasan halinta sarai,koda nawa aikin zai basu idan ta motsa mata tana iya cancel dinsa

"Zanyi qoqarin nima" Ta amsa masa tana kunna famfo sai ta bige da daura alwala.

Mutum hudu ke biye dashi sanda yake takowa cikin veranda din idanunsa saman takardar dake hannunsa yana sake karanta abinda take dauke dashi. Can qasan zuciyarsa akwai wani kokwanto da mamaki,kusan zaman yau da suka fara yi da mikail wanda ba'a qarqareshi ba saboda quracewar lokaci ya karanci kamar hankalinsa ba gurin yake ba sam sam. Yana karance da kuma bibiye da motsinsa. Duk muhimmanci da girman takardar a wajen kamfanin gaba daya amma har ya iya mantota cikin dakin taron,wannan ya sanya ya yanke biyoshi da kanshi ya kawo masa don ya sake alamta masa muhimmancin takardar.


"Wait here" Ya fadi a nutse ga mutanen dake bayanshi yana sanya code na qofar office din Mikhail din ta bude ya murza handle din yana turawa can qasan ransa yana jin kamar bai kamata yayi hakan ba ba tare daya nema izinin shigar ba. Duk da kowanne office a qarqashinsa yake amma bai shiga office din kowa,hakanan baya taba bada damar a bude maka office muddin baka nan,amma haka kawai yau din yaji yayi hakan.

Sanda ya murda handle din yake shigowa da sallama cikin husky and deep voice nashin nan,dai dai sannan itama ta bude qofar toilet din ta fito tana qoqarin maida rolling na mayafinta.

Idanunsa kan mikail daya miqe a rude cike da tsananin mamakin ganin boss din nasa yau da kanshi a office dinsa gabansa yana faduwa,yayin da nata idanun suke kan fu'ad fuskar fu'ad din tana dubansa qasan ranta tana jin kamar tasan wannan fuskar.

Baikai ga lura da ita ba ya miqa masa takardar

"Keep it......." Ya furta da wani irin yanayi idanunsa cikin tsakiyar qwayar idanun mikail wanda hakan kadai ya isa ya gaya masa wani gargadi yake aika masa da kuma muhimmancin da takardar ke dashi

"In sha Allah sir" Ya amsa yana karbarta da hannu biyu. Juyawa yayi da zummar ficewa a office din,dai dai sannan idonsa ya sauka a kanta. Idanunasu suka gauraya waje daya,sai tayi saurin zare dubanta daga kan fuskar tashi gabanta yayi wani irin faduwar da batasan meye dalili ba.

Dan zuba mata ido yayi na sakanni tamkar zaiyi magana,sai kuma ya fasa,ya juya ya kalli mikail sannan ya maida dubansa kanta sai kuma ya juya yana ficewa a nutse daga office din.

Wata wawiyar ajiyar zuciya ya sauke. Allah ya sanya ba zuwa yayi ya samesu cikin wani yanayi ba da dukka sauran gaskiyarsa da yakeson tabbatarwa boos din a yau babu ita.

Yasan an jima ana kai masa tsegumin halinsa,amma kasancewar shi din ba mutum bane me daukan qananun maganganu ya sanya abun bai wani tasiri ba.

A yadda yake jinsa a dan rude sai yaji yana buqatar giya don daidaita nutsuwarsa. Ya tafi zuwa fridge din yana fadin

"Boss......bashi da sauqi kwata kwata,idan har wani kuskure ya faru tsaf zaka rasa aikinka,a wajensa wannan din ba wani abu bane me wahala".

Batace dashi

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login