Showing 33001 words to 36000 words out of 557259 words

Chapter 12 - πƒπ”ππˆπ˜ATA BOOK1 AND 2 HAUSA NOVEL

HUGUMA   

03 Nov 2025

418

tuhumar kansa tare da ganin tsananin baike da wallensa. Wannan tunanin kadai ya qara masa qaimi,ya taka qafafunsa cikin azama da qwarin gwiwa ya soma rufa mata baya lokacin da takeji a ranta ta kammala siyan duk wani abu da suke da buqata ita da 'yan uwanta,wanann ya sanya ta nufi gurin biyan kudin kai tsaye

"Inda zan baka shawara......zaifi kyau ka koma ka tafi sabgaka...."

"Saboda ke kike nema na bani ke nemanki ba?,saboda nine mai laifi bake bace?" Hankali kwance ta maqale kafada tana sakin siririn murmushi

"A'aha.....ba don dukka wadannan dalilan bane suka sanya ni na baka wannan shawarar ba......na baka ita ne don gudun kada ALLURA TA TONO GARMA"

"Ni dake zanga wanda allurarsa zata tono garma......"

"Ba laifilaifi malam naseer....." Abinda tace dashi kenan tana ci gaba da tattaki a bayanta. Yau yanason ganin qarshen gudun ruwanta......yanason yasan ita din wace?......da waye take tare?,su waye suka dauki nauyinta?.

Waye ya turota?,maqarqashiya ce ko kuma hadin baki?.

Hakanan yaci gaba da rufa mata baya tamkar me tsaron lafiyarta ko wanda aka bashi aikin kula da ita. Har cikin zuciyarsa yakejin yau zai nuna mata shi waye,zai kuma tabbatar mata tayi mahaukacin gangancin kuskure data shiga hanyarsa.

Mutum biyu suka samu ana lissafa kayansu jikin qaramar na'urar dake da alhakin qididdige fitar kaya cikin katafaren shagon.

A hankali ta tsaya daga bayan matar wadda bata iya ganin ainihin fuskarta,saidai shigar atamfar chiganvy gold mix match da wani irin danyen lafiyayyen lace da aka yiwa qawataccen dinkin buba da zani ya fito da kamalarta da kuma cikar siffarta. Tsaye yake daga gefanta,matashin da duka duka shekarunsa ba zasu haura ashirin da takwas ba. Ya bata dukka hankalinsa yana sauraren maganar da takeyi dashi cikin muryarta dake bayyanar da tsantsar kamalarta da cikakkiyar nutsuwar ruhi data halitta. Yanayin yadda ya rusuna ya bata hankalinsa yana saurarenta kadai zai bayyana maka zallar ladabi da kuma ganin girmanta da yakeyi,akwai kuma tag idan ka lura sosai daga gaban aljihunsa dake bayyanar da cewa shi din ma'aikaci ne a wani guri na daban.

Mai matsakaicin tsaho ce,hakanan me jiki ce saidai ba qiba me yawa cancan ba,ta lullube saman kanta da 4D Vail me asalin kyau da aka zubawa duwatsu masu daraja akayi adon jiki dasu.

Sassanyan qamshinta ya dinga tasowa a hankali daga jikinta zuwa hancin sabreen dake tsaye daga bayanta tana kallon tulin kayan siyayyar da aketa jera mata cikin ledar dake dauke da tambarin store din.

Hannunta dake dauke da wasu kyawawan banguls masu sheqi ta miqawa ma'aikacin gurin tana cewa

"Bansan me yasa suke son mu'amala da wannan katin bankin ba,duk sun lalace da lamarin cashless" Murmushi ma'aikacin ya saki cikin tsananin girmamawa

"To ai hajiya yafi sauqin sha'ani ne" Kai ta gyada a hankali tana furta

"To Allah ya kyauta". A nutse ta maida dubanta ga saurayin,tun kafin tace wani abu ya sake matsowa a ladabce yana bata hankalinsa

"Ka kiramin wancan yawalen da kuma wancan acicin suzo mu wuce kafin rana ta sake dagawa"

"Okay to in sha Allah" Ya amsa mata yana zaro wayarsa daga gaban rigarsa,yayin da ta fara takawa cikin nutsuwa tana ficewa daga gurin hadi da gyara yafen mayafinta dake qoqarin zamewa.

Wucewar tata ya bawa sabreen damar matsowa gaba don a lissafa mata nata kayan

"Ji mana.......zaki dawomin da duk abinda kika san kin sace ko kuma saimun dangana da hukuma?" Hannayenta ta goye a qirjinta tana kallon qofa yadda mutane ki shige da ficensu hankali kwance. Yana da ban mamaki......saidai ita din ta fishi abun mamaki. Inda yasan meta taka a kansa......inda tasan cewa kafataninsa.....zahirinsa da badininsa a tafin hannunta yake da baiyi gigin matsawa rayuwarta ba har ya matso gareta har haka ba.

A nutse ta waiwayo ta zube masa farare tas din idanunta masu matuqar jan hankali da fusgar tunanin me tunani

"Kana sha'awar yin gaba da gaba da hukumar ne?" Ta masa tambayar idanunta a tsaye car tsakiyar nashi. Idan ya kira kansa gogaggen cikin duniya baiyi qarya ba.....muddin kuwa ya kasance hakan yana ganin mugun ganganci ne zaiyi ya gaza samun fikirar karantar mutum daga yanayin kallo zuwa lafuzan bakinsa ba.......

"Kina tunanin abune me wahala a gareni?" Ya amsa mata yana mamakin yadda wannan mugun kwarjinin nata yake taka masa burki,kaifin idanunta ke hanashi daukan mataki tare da aiwatar da abinda yayi niyya.......abinda zuciyarsa ke shawartarsa.

"Ko daya....daidai ne kuma" Ta amsa masa tana dauke duba da hankalinta daga kanshi tana maidawa ga ma'aikacin wanda ya kammala lissafin yana gaya mata adadin abinda zata biya.

"Okay" Ta furta hankali kwance tana maida dubanta ga daya daga cikin ma'aikatan dake taimakawa da wadanda sukayi siyayya me yawa kamarta

"Ko zaka fitamin dasu gate na biyu?"

"Okay hajiya" Ya fada yana ajjiye qaramar calculator dake hannunsa yana qarasowa gurin tare da jira a gama sanya dukka kayan cikin leda.

Sake Waiwayowa tayi gareshi karo na biyu. Kallon da tayi masa ta fahimci yakai matakin qarshe a iya haqurinsa

"Malam naseer......ka shirya biyan duka bill na siyayyar sabreen ko kuwa tunda kai ka kawo qafafunka duk da gargadinka da tayi?"

"Sabreen?" Ya maimaita sunan yana kallon idanunta. Kiran sunan sabreen da tayi a maimakon basma shi ya batar masa da tunani cikin taqi qanqani.

"Zai biya duka bill din.....na gode sosai" Ta fadiwa ma'aikacin

"Naga uban wanda zai sakani biyan kudin nan......na fahimci na sakar miki fa da yawa" Ya furta da zafi sannan a zafafe ya biyo bayanta. Ya tsammaci zata nemi guduwa ko ta gudu dinma,amma ga tarin mamakinsa tun bai qarasa isowa gareta ba taja cak ta tsaya tana sauraron isowarsa.

"Ka samu aminci game da haramtattun kayanka da aka aiko maka dasu ta cikin jirgin ruwan dake tsakanin River Benue da riba niger?.......ko kuma ka shirya aci kasuwar wannan sirrin da jami'an tsaron dake neman kayan tamkar yadda mutuwa ke neman ruhi?".

Kamar wanda aka sanyawa sasari akan tsaida haka yaja wani wawan burki. Kallonta yakeyi da madaukakin mamaki. Wanne irin hadari ne da ita har haka?. Wanne nisan ji da gani ne da ita?,nisan binciken da ya bata damar gano birnannen sirrinsa da ko matarsa da suke kwana daki daya su tashi daki daya bata sani ba?.

"Ka biyasu kudin siyayyarsu duk yadda suka buqata,na barka lafiya Alhaji Naseer" Ta qarashe maganar tana takawa hankali kwance tana fita kwata kwata daga wajen.

"Malam qaraso ka bada kudin......ta atm ne ko cash zaka bada?" Muryar ma'aikacin ta katseshi daga bin burbushin hanyar data wuce da kallo ya juyo zuwa wajen biyan kudin yana sauke wani irin gauron numfashi me nauyi da zafi cikin tsananin mamaki da tsoro.

*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*

*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*

*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*

*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*

*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*

*ZAFAFA BIYAR*

*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*

*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*

_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_

_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_

_K'ALBIM Mamuhghee_

_AJIYA A DUHU Billynabdul_

_DUNIYATA Huguma_

_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_

*hudu 2k*

*uku 1500*

*Biyu 1k*

*Daya 500*

_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_

*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*

*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*

*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*

*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*

*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*

*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*πŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺ

89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf

*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*

*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*πŸ₯°πŸ₯°


*D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

*Arewabooks@:Huguma*

PAGE 21

https://chat.whatsapp.com/DT97XBDyEfyEwniN0a09Cz
__________________________
*_ALBISHIR A GAREKU!!_*

*_SHIN KUNSAN UMMUMAHNOOR LUXURIES TA TANADAR MUKU INGANTATTUN KAYAN ADO NA FITA KUNYA KUWA?_*

*_KAMAR SU_*

Atamfofi
Laces
Shadda
Materials
Takalma
Jakunkuna
Mayafai
Trolley
Sarka da dan kunne
Oil perfumes

*_karki tsaya sanya har ayi babu ke,maza garzaya ta nan_*

Numbers
08034469681
08135142610

Handles
Instagram @ummu_mahnoor_luxuries
TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries
Facebook ummu_mahnoor_luxuries

*_inganci da kwalliya shine muradinmu_*
____________________________


Sanda take sallamewa saita samu kanta da zama sosai a inda ta idar da sallar tana irga tasbihi da yatsun hannunta,yayin da kunnuwanta kadan kadan ke jiye mata tasbihin matar dake yinsa can qasa qasa,saidai lokaci lokaci yana qwacewa ya fito,har zuwa sannan bata waiwaya ko sau daya ta kalli fuskarta ba,amma daddadan turarenta bai fasa silalowa zuwa cikin hancinta ba.

Wayarta ta matsa haske ya bayyana ta duba lokaci. Tasan ko busari bai iso ba to dab yake da isowar,ta maida wayar ta ajiye tana kallon sararin cikin masallacin da babu kowa saisu uku. Daidai sanda zata dauke idanunta dai dai sannan taji matar dake gefan nata taja wani irin qaqqarfan salati numfashinta yana yayyankewa.

A tsorace ta waiwaya gefan damanta... Hannuwanta dukka biyun na tallafe da qirjinta,tana kuma daga kanta sama tare da qoqarin maimaita

"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" Saidai tana kakkamota ne da qyar saboda yadda numfashin yake son qwace mata.

Da hanzari ta miqe,hanzarin daya sanyata cilli da wayarta dake saman cinyarta. Jikinta dukka yana rawa a gaggauce ta matsa jikin matar

"Lafiya?,me yake faruwa?" Ta furta cikin matuqar tsoro da kuma rudanin ganin yadda take kaman shirin rasa numfashinta.

Bata iya amsa mata ba,wannan ya sanya sabreen zama sosai ta tallafeta da kyau zuwa jikinta tana sake maimaita tambayarta a rude

"Ina ganin kaman asthma attack ne" Mace guda dayan data rage a cikin masallacin ta furta bayan ta iso wajen itama tana dubanta

"Asthma?" Sabreen ta furta a gigice tana jin wani abu yana dukan zuciyarta. Shine ciwo guda daya da kullum taji sunansa sai zuciyarta ya tsinke,ciwo qwaya dayan da kullum takewa mummunan kallo,ciwo guda dayan da yayi silar wasu jigo na rayuwarta,har ila yau ciwo qwaya daya da yake wujijjiga rayuwarsu.

Da sauri ta finciko jakarta bayan da tunaninta ya dawo,ta zugeta da hannu daya daya hannun yana tallafe da ita,ta daga jakar ta zazzage duka tarkacen dake ciki,cikin matuqar sa'a ta hangi inhaler dihta.

A gaggauce ta dauka ta kara mata,hannuwan matar dukka rawa suke sanda ta dora nata hannun saman na sabreen kamar tana son tayata matsa inhaler din,kamar tanason nuna mata tsananin buqatarta da takeyi.

Cikin mintuna qalilan ta fara samuwa,saidai har yanxun bata daidaita yadda ya kamata ace ta daidaita din ba. Oily eyes dinta sun cika taf da qwalla

"Kamar asibiti tafi buqatar a kaita" Ta kasa haquri har sai da bakinta ya furta hakan

"Zaifi kyau dai gaskiya don da alama tana buqatar iska sosai".

Dai dai sannan wayarta data watsar ta dauki ringing. Matar ce ta matsa ta miqo mata,ta sanya hannu ta karba tana fadin

" Na gode" Tana duba me kiran.

Busari ne,ta latse wayar tana karawa a kunnenta

"Na qaraso,ina dab da bakin masallacin"

"Ka karba kayana wajen me gadi,gani nan fitowa asibiti zamu wuce" Bata tsaya sauraren abinda zai fada ba ta katse kiran.

Idanunta ta mayar saman fuskar matar. Wani abu taji ya taba zuciyarta,sai takejin kamar umminta ce ta dawo,sai takejin tamkar lokacin data rasa umminta. A duk sanda take mutum me dauke da irin ciwon tsananin tausayinsa yake kamata,duk da itama abar tausayin ce. Duk sanda taga babbar kaman haka yana fafutuka da wannan ciwon sai ta dinga tuna umminta.

Su biyun suka tallafeta don taji qwarin jikinta,suna takowa a hankali da ita har suka fito zuwa inda Kekenapep din yake

"Zan samu face mask a wajenka?" Ta tambayi busari.

"Eh hajiya" Ya amsa mata da sauri yana bude aljihun motar ya fidda shi sabo fil ya bata.

A kusa da ita ta zauna tana riqe da face mask din,saita sauke idanunta qasa tana jujjuyashi.

"Zan saka miki wannan saboda iskan mota,motan bana gida bane". Idanunta saman fuskar yarinyar,har zuciyarta tana jin qauna da jinjina taimakonta a kanta,ta lura tana d'anjin wani nauyi da kuma rashin sakewa. Qaramar yarinya haka me zuciyar taimako?,sai abun ya qayatar da ita.

Mintuna ashirin daidai suka qarasa private hospital din,wanda a nan file nata dana qannenta dukka yake. Tuntuntuni ta sallama asibitin gwamnati,yana daya daga cikin muhallan da suka samarwa rayuwarta gibi,yana daya daga cikin guraren da suka dasa qaton tarihi a rayuwarta,suka kuma ajiye mata wani tabo na har abada,shi ya sanya daga sanda ta samu dama ta nisanta kanta da dukkaninsu daga asibitin gwamnati.

Private hospital ne daya amsa sunanshi,babu nau'in wata kulawa da mara lafiya baya samunta,saidai kuma kudi ne zasu fita sosai daga aljihun majinyaci ko ahalinsa.

Private room suka bata,cikin mintuna goma sha biyar kacal suka bata dukkan taimakon daya dace,bata samu nutsuwa ba sai da suka shafe awa guda taga bacci sosai ya dauketa tana sauke numfashin a hankali ta cikin oxygen din da suka maqala mata saboda yadda taso galabaita sosai.

Zama tayi kawai gabanta bayan taja kujera,ta maqale hannunta a qirji bayan ta zube idanunta a kanta tana dawo da bayanan da likita yayi mata a kanta.

"Ta samu mummunan attack ne,tana samun kulawa sosai to amma kuma kaman yanayi ya nuna ba'a kiyaye wasu dokoki na masu ciwon,sannan kuskure ne ta dinga fita hakanan ba tare da inhaler ko wani a kusa da ita ba".

Idanunta ta qanqance sosai tana ci gaba da nazarin maganganunsa. Hakanan sai taji ranta yayi matuqar baci,indai har mace me irin wannan shekarun bata samu kulawa ba sai yaushe?,indai har ba za'a kula da dokokin da aka bata ba meye amfanin makusantanta?. Dukkan alamu sun nuna,tun daga suturar jikinta da komai nata ma cikin wadata da sukunin rayuwa take ainun,to meye zai hana su su bata kulawa su ahalin nata?.

Idan zata iya tunawa mutum daya ne ta gansu a tare a tsaye cikin store din,har tana bada umarnin a kira mata wani data kira a cici da kuma yawale. Yawonsu kenan yafi musu kasancewa da ita?,yanzu haka fa mahaifiyarsu ce amma sun gwammaci tafiya yawo akan su bata kulawa?.

Iska me zafi ta sake fesarwa ranta yana sake tunzura musamman bayan data duba agogon hannunta. Aqalla awa daya harda rabi da barowarsu store din amma har yanxun basu biyo address na asibitin data barwa wancan matar sun biyo bayan baiwar Allahn ba?. Sake juya wayarta tayi su huda suna fado mata a rai. Ta tabbatar zuwa yanzun sun dawo gida,suna can kuma zaune su daya a daki. Karon farko da taji kaman ya kamata ta siya waya ko qwaya daya ce ta ajiye cikin dakin saboda lalura irin haka,ko ba komai ba zata barsu cikin zulumi ba,zata kira taji lafiyarsu suma suji lafiyarta,duk kuwa da cewa komai runtsi a gida takeyin magrib.

Daidai sanda tunaninta yakai nan taji an murda handle na qofar. Kyakkyawan matashin ne ya fara bayyana. Dogo me matsakaicin haske. Kai tsaye idan kace masa kyakkyawa bakayi kuskure ba,yana da cikakkiyar suma me santsi tun daga kansa zuwa habarsa.

Yana sanye da dakakkiyar shaddar getzner Neautaral color daketa yauqi da sheqi. Yanayin dinkin da aka yiwa shaddar yayi masifar dacewa da structure na jikinsa. Dinkin zamani dake nuna zallar gogewa da wadatar arziqi na wanda suturar ke kwance a jikinsa. Yadda shaddar ke walqiya hakanan hular kansa,wadda koda ba'a gaya maka kudinta ba zakasan cewa bada qaramin zare aka saqata ba. Qafafun sanye cikin takalmin Batozzi,hakanan cikin qasa da second biyar dakin ya gauraye da sassanyan qamshin turarensa.

"Hamma mun sameta,gata tana bacci" Ya furta da kwantacciyar muryarsa da alama kuma yana magana ne da wani a wayar dake manne a kunnensa,dukka hankalinsa da idanuwansa suna kan matar dake kwance cikin mazari yana d'okin isa gareta.

"Okay hamma......in sha Allah" Ya sake fadi da sauri sannan ya jefa wayar a aljihunsa yana isa inda take kwancen ba tare daya damu ya kashe wayar ba.

Rusunawa yayi sosai a gabanta yana riqe da hannunta da dukka hannayensa biyun. Yayi wani irin laushi,don idan ka kalli hannunsa da kyau kana iya ganin yadda suke danyin rawa.

Dauke dubanta tayi daga kansa

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login