Showing 12001 words to 15000 words out of 557259 words
ba......"
"Ubanka da uwarka,shegen yaro me tsaurin ido,kaci ubanka" Ta fada har tana zullo tare da watsa masa daquwa. Ta jima da tsanar dama wannan kamewar tasa,ta jima da tsanar yadda yake da dauke kai da rashin hayaniya akan komai da zatayi masa,duk yadda takai ga tama masa wajen bashi baqin kashi da baqar wahala don ya magantu dukka ya shanye sai a yau din.
Cikin qasa da minti guda launukan idanunsa suka sauya,baice qala ba amma kunnuwansa suna suna iya jin zafafan muggan kalaman da take jifanshi dasu. Ya tako a nutse ya iso gaban saddiq dake durqushe a gabanta ya sanya hannu ya damqi hannunsa ya tasheshi tsaye,abun sai ya masa kamanceceniya da sanda saddiq din ke tsananin roqon mahaifiyarsu akan kada ta tafi ta barsu.
Bai waiwayeta ba,bai kuma dakata ba ya durfafi qofar fita daga falon kanshi tsaye,ba tsoro ba shakka ba kuma shayi
"Ina zakaje,bance ba zakuje makaranta ba?" Ta furta da qaqqarfan sauti. Bai dakata ba bai kuma waiwayo ba ko ya nuna yasan tanayi har ya fice daga falon. A yau ta rushe dukkan wani ragowar kara da dagin qafa da yakeyi mata. Baya wasa da kalmar UBA sam a rayuwarsa,IYAYEN MA guda biyu,abba da Abbey.
https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997
________________________
_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_
_K'ALBIM Mamuhghee_
_AJIYA A DUHU Billynabdul_
_DUNIYATA Huguma_
_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_
*hudu 2k*
*uku 1500*
*Biyu 1k*
*Daya 500*
_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_
*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*
*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*π³πͺπ³πͺ
89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf
*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*
*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*π₯°π₯°
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
*Arewabooks:Huguma*
https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997
PAGE 09
Ko Faruqee baisan da zuwansa makarantar ba sakamakon banbancin abinda kowannensu yake karanta,har sai sanda aka fito break.
Har a sannan ranshi a jagule yake,bacin rai kowanne second yana sake motsa zuciyarsa. Faruqee ya sameshi daga bayan makarantar zaune qasan bishiya saman rairayin dake wajen,hannunsa riqe da busashen siririn reshen bishiyar yana tona qasa dashi,ya kafe qasar da idanu kamar me nazarin samar da wani abun amfani daga gareta. Ta gefansa ya zauna,yayi masa tambayar duniya akan ya akayi ya taho makarantar amma ya gaza cewa komai. Na Faruqee ba,tunda ya shiga class din baiyi manana da kowa ba,don bayajin koda ya bude bakinsa akwai wasu kalmomi da zasu iya fita daga cikinsa. Dole Faruqee ya haqura ya kuma tayashi zaman shurun,don dukkansu dama babu me 'yanci ko damar yin break,to inama kudin?,dukka dana transport din da komai ta hada ta kalmashe.
Sai a hanyar komawa yaji komai daga bakin saddiq. Qwafa yaja yana girgiza kai
"Duk yadda kake tunanin matar nan ta wuce nan,duk kuwa yadda zan fasalta maka,ta samu sassauci ne daga garemu shi yasa take abinda taga dama,ace mutum ya shiga shekara ta sha biyar,kana girma amma baka da 'yanci?" Shikam baima iya cewa komai ba har zuwa sanda qafafunsu suka maidasu gida.
Sai da suka gilma ta gaban gidansu kafin su cimma gidan RIQOnsu a yanzu,idanunsa zube bisa fuskar gidan dake garqame da kwado. Take yaji wata matsananciyar kewar gidan da kewar Abbie da jadda suka saukar masa. Duk da suna rayuwa ne cikin matsakaicin matsayi na rayuwa,amma rayuwarsu rayuwa ce me 'yanci da kuma dadi. Duk da suna rayuwa da maama cikin wani baqon hali da murdaddiyar dabi'a.......hakan yafi musu sauqi a kan rayuwarsu ta yanzun cikin gidan RUQO.
Ya janye idanunsa sanda ya dubu daidai wajen da mahaifinsa ya dogaro da qyar ya biyo bayan maaman yana cike da fatan zata dakata daga aiwatar da qudurinta nayin nesa da rayuwarsu,wani zafin akan na dazu ya sake yunqurowa ya mamaye zuciyarsa.
Daga saman balcony din da zata sadaka da ainihin falon suka sameta a zaune ta hakimce. Faruqee ne a gaba,musaddiq yana biye dashi,sai me babban suna da ko qaunar hada idanu da ita bayayi. Zuciyarsa yadda take a zafafen nan tana ayyana masa abubuwa masu dama a kanta.
"Idan ka kuskura ka qaraso na saina sanya an maka dukan tsiya......baka isa ka shigamin gida ba tunda kai din tantiri ne mara kunya.....nan gaba kadan shaye shaye zaka farayi da daba,kaga kenan ka samu hanyar da zaka hallakani a banza" Ta fada tana miqewa tsaye.
Dukka su hudun sukayi carko carko suna dubanta da jin kuma wani sabon bala'in daya tunkarosu kuma bayan na dazu da safe.
"Kai har ka isa na fadi magana ka sabamin bare ka maidamin?,don an zagi uwarka da ubanka,su su waye da ba za'a zagesu ba?,wato gaka kai me zuciya ko,to an zagesu din na kuma zagi banza da wofi".
Da qarfi ya damqi hannun saddiq ya kuma soma ja da baya yana janye jikinsa daga wajen
" Yauwa gwara daka fahimta,don wallahi kabar gidan nan kenan,tun yanzu kana tsayarmin ina ga nan gaba idan ka gama zama balagagge?".
Da sassarfa Faruqee da har ya isa bakin qofar falon ya soma saukowa yana takowa zuwa garesa ganin suna nufar gate din fita daga gidan yana qwala masa kira da niyyar tsaidashi
"Aisai ka bishi kaima don ubanku,na fiku iskanci qananun balagaggu" Ta furta tana komawa saman kujerar ta zauna
"Bar nan gurin" Ta kwatsawa musaddiq daya mace a wajen saboda tsoro da mamaki tsawa,baiyi wata wata ba ya juya shima yabi bayan 'yan uwansa.
Bai iya tsaidashi ba har sai da suka isa qofar gidansu dake garqame. Sai sukayi carko carko suna kallon kallon shi dashi. A yadda ya hangi kwantaccen fushi da bacin rai akan fuskar me babban suna sai ya rasa da wadanne kalmomi zai iya shawo kan me babban suna?,wacce kalma ce zatayi masa aiki?.
"Kayi haquri kazo mu koma,tunda gidan abba ne ba nata ba bata isa ta hanaka zama ba,yau ko kasheni zatayi saidai ta kasheni" Wani irin kallo ya yiwa Faruqee,ga mamakinsa murmushi ya gani ya subuce masa.
Da wani irin zafi ya waiwaya ya dauko dutsen dake yashe gefan malalen simintin dake gaban gidan nasu,har tsoro ya kama Faruqee yaja da gefe,sai yaga ya doshi qofar gidan,ya kama kwadon dake jiki ya fara bugeshi baji ba gani.
Tsakiyar azahar ne,wannan ya sanya ba yawaitar jama'a a layin bare a samu me dakatar dashi. A yanayin da yakejin zuciyarsa da kansa a ciki,bayajin akwai ma wanda ya isa ya dakatar dashi din sai MUTUM DAYA TAK A DUNIYA.....ALHAJI HAMZA KIBIYA.
Zare kwadon yayi ya watsar gefe,kansa tsaye kuma ya soma cusa kai cikin gidan ba tare daya damu da yana datti ko qurar data lullube qofar ba.
Wannan shine mafarin komowarsa gidansu......tushensa......asalinsa da yaji yafi masa kwanciyar hankali sau dubu akwan kwanansa cikin babban bedroom din gidan alhj hamza dake dauke da wuta 24/7 da kayan alatu na rayuwa.
Tun a asalin halittarsa shi jajirtacce ne tsayayye da bai yarda da faduwa ba......sanda komai ya dinga faruwa kuma daki daki,sai zuciyarsa ta qara qeqashewa ta kuma tsaya kyam......ya karantawa kansa da kansa cewar shine uwa kuma uban kansa da dan uwansa sadiq.......shine gatan kawunansu,ya fidda kowa daga cikin zuciya rayuwarsa dama hasashensa. Wannan ya sanya tun rana ta farko da suka dawo gidan bai kuma karbar koda ruwa daga gidan alhj hamza ba. Duk da yadda ran Faruqee ke baci da yadda yake wofantar da komai da ya kawo musu din kuwa koda ruwan sha ne. Da kansa ya tsaya,sadiq na debo ruwa shi kuma yana wanke komai da yayi saura na gidan wanda zasu iya amfani dashi. Cikin kwanaki uku kacal ya fara Qwadago.
Duk wani aiki da zai samar masa kudi......komai wuyarsa kuwa muddin halas ne yana karba yayishi hannu bibbiyu. Da wannan din ya dogara.....da dan abinda yake samu din ya dauke musu abinci dama abin sha......idan faraga ta samu harda kudin transport na makaranta koda na zuwa kadai ne banda na dawowa.
Sauyawar yanayi da kuma tsarin rayuwarsa ya sake canxashi gaba daya. Yana tsananin son karatu kowanne iri ne,na addini dana boko gaba daya
*_TURQASHI_*
*_BIGI SAI BIGI_*
*_BABBAN GORO SAI MAGOGIN QARFE_*
*_TASTED AND TRUSTED_*
*_TASTED AND TRUSTED_*
*_TASTED AND TRUSTED_*
*_Kina da burin samun ingantaccen TURAREN WUTA me TSANANIN KAMA GURI?_*
*_TURAREN WUTAR DA ZAKI SANYAWA DAKI AMMA HATTA DA LABULAYE KAYAN SAWAN DAKE SAQALE A DAKIN SU KAMA DA QAMSHI?_*
*_TURAREN WUTAR DA KUJERUNKI ZASU KAMA QAMSHI DARAM?_*
*_KI BANKADA LABULAYENKI KIJI SASSANYAN QAMSHI?_*
*QAMSHI IYA QAMSHI 24HR*
*HUMRA ME TSAYAWA A ZUCIYAR ME GIDA*
*NASAN ZAKI TAMBAYI KANKI A INA ZAN SAMU WANNAN?*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER*
*_tayi muku tanadin abubuwa da yawa irinsu_*
Khumra
Turaren wuta
Kulaccam
Lablab
Oil perfumes
Original musk tahara
Multipurpose spray
*karki kuskura kada kiyi ganganci ayi babu ke,kai tsaye tuntubeta ta wannan number*
08032119803
Ko ki lalubeta ta nanππΎππΎππΎ
*Instagram handle_incense by kabo daughter*
*Facebook_kabo daughter*
*Twitter_kabo daughter*
________________________________
_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_
_K'ALBIM Mamuhghee_
_AJIYA A DUHU Billynabdul_
_DUNIYATA Huguma_
_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_
*hudu 2k*
*uku 1500*
*Biyu 1k*
*Daya 500*
_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_
*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*
*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*π³πͺπ³πͺ
89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf
*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*
*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*π₯°π₯°
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
*Arewabooks*
https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997
PAGE 10
Baya wasa da islamiyya,amma wahala da nauyin kansa dana saddiq ya sanya ya sallamawa zuwa islamiyya. Duk da haka bai sare ba,ya lalubi makarantar magariba ta manya ya soma zuwa don karantar litattafan addini,duk kuwa da nisan zangon tafiya dake a tsakaninsu.
Su kansu ba 'yantattun 'ya'ya bane cikin gidan mahaifinsu......amma duk da wannan ya gaza barin me babban suna yakuma qyaleshi kamar yadda ya fuskanci yana da muradin hakan. Duk da basu da 'yanci ko fada aji a gidan......amma hakan baya hanashi dauko abinci daga cikin nasa kwanon data qayyade musu cikin gidan ya kawo don suyi tarayya suci tare,amma koda wasa me babban sunan bai taba dangwala yatsarshi a ciki ba.
Abun yana ma Faruqee zafi da ciwo matuqa,har daga qarshe hakan ya sanya suka samu sabani
"Don mama tayi maka laifi ai ba abincinta bane,abincin abba ne wanda har yanzu a nasa zaton kuna cikin gidansa ne cikin aminci bisa kulawarta,iyakarta da abincin nan tazo ta diba itama taci,don ko dafawa ba ita ke dafawa,larai ce......kuma ita ke qaramin yawan abincin a boye ba tare da saninta ba,to indai bawai nima gaba da fushi kakeyi dani ba banga abinda zai hanaka ci ba.....idanma kai ba zakaci ba....kada ka sake hana saddiqu yaci,kai ka zauna haka can ta matse maka". Busashen murmushi ya saki yana jin yadda cikinsa ke qugin yunwa,don yau ba wani abun kirki ya samo a aikin ba,wannan ya sanya basu wani qoshi ba wunin ranar sur.....ga kuma tafiya makaranta a gabansu gobe juma'a.
Yadda Faruqee yayi fushi ya kuma dauki zafi da abun ya sanya yake barin saddiq din suna hadaka dashi. Shikam yasan bazai taba iya sanya abincin cikin bakinsa ba. A duk sanda yayi yuqurin hakan sai maganganunta su dawo musu kar kar cikin qwaqwalwa
"Tunda uwarka ta zube ku ta tafi ta barku,banga uban da zai iya zama daku ba......uwarku ma ta barku ballanta wani?" Aduk lokacin da zai tuna da irin wannan maganar a take yakanji komai ya fita a kansa ne,tsananin baqinciki ya mamaye walwalarsa,wata irin wuta me zafi na taso daga qasan zuciyarsa da ruhinsa dangane da imaninsa. Ta wani fuskar da mama da sauran 'yan unguwa dake jifansu da muggan kalamai sai yaji sam baya jin zafinsu ko kadan,da uwa da uba da kuma dangi ake ado,su kuma basu da ko guda daya!. Ya tabbata lallai su din cikakkun marasa gata da galihu ne,kuma kowanne suna aka kirayesu dashi sun cancanta.
Yayi imani inda har jadda tana raye.....koda sunfi kowa talauci da matsin rayuwa......to babu shakka zasu zamo na sahun gaba gaba wajen zama yaran da sukafi kowa samun gata na kulawa da soyayyar kaka. Saidai Allah baya barin wani don wani yaji dadi,ya tabbatar haka ubangiji ya tsara musu tasu DUNIYAr,haka kuma yaso ganinsu a cikinta.
A wannna tafiyar abba yayi nisan kiwon da ya jima baiyi irinsa ba. Yana rayuwa bisa yaqinin lallai gidansa da marayun Allahn daya dauka riqo suna lafiya,tunda duk sanda zaya kirata hakan take gaya masa,sannan lokaci bayan lokaci tana hadashi da musaddiq,shima kuma
"Lafiya qalau muke abba" Shine amsar da yake bashi bisa jagorancin mummunan gargadi da idanuwa da maman take aike masa duk sanda suke wayar. Faruqee ne bata taba yarda ta bawa wayar ba,sai a wani yammaci da abban yace ya jiyo muryarsa ta hadasu.
"Lafiya amma ba qalau ba amma.....muna buqatar ka dawo a kusa abba" Bata iya barinsa ba ta fusge wayar daga hannunsa cikin hanzari ganin yana niyyar sauka daga layi.
Maganar ta tsayewa abban a rai,ta kuma sanyashi yaji dukkan hankalinsa yana tarkatowa yana yowa gida. Duk kuwa da akwai sauran abu daya tsara zaiyi a can din,amman sai yaji komai ya fita a kansa tahowarsa gida ce abu na farko da yake kwana yana tashi dashi.
*******Kusan dukkansu jan qafafunsu sukeyi,zafin rana yunwa ga gajiya dake tattare dasu. Akwai nisan tazara me dan dama tsakaninsu da makarantar wanda suke shanyeta a qasa daga tafiya zuwa dawowa. Babu ranar hutu a garesu idan ba asabar ko lahadi ba. Ga me babban suna kuwa,baya gane asabar ko lahadin cikin rayuwarsa da DUNIYARSA. Rayuwar tasa gaba daya a birkice take,bashi da wata dogon hutu daya wuce makaranta zuwa neman kudin abinci.
Yayi wani irin duhu,dukkan hasken fatar nan da suka gado babu shi,ya rame daga ainihin halittarsa zuwa wata halitta ta daban.
Tun daga nesa ya soma hangen wani abu da yayi matuqar girgiza hankali da kuma tunaninsa,ya sanya dukkan wani tunani nashi ya fara sauka daga kan layi,ya kuma daina gane me Faruqee daketa faman bashi labari yake fadi.
Wata qurace take tashi daga wani sashe na gidansu gami da qarar zubewar bulalluka. Gefe guda akwai tsaiwar tsirarun mutane da kuma yara wadanda basa raina abun kallo,hakanan basa bari abun kallon ya wucesu kamar qanqantarsa.
Zame hannunsa yayi daga jikin na Faruqee,a gaggauce da kuma hanzari ya soma tattaki har zuwa inda aikin ke gudana.
"Gidanmu ne fa.....me yayi ake rusheshi?" Ya furta bayan ya tabbata ya tsaya gaban mutanen dake gabatar da aikin futu futu cikin qasa da qura.
Dukkansu suka waiwayo suna dubanshi,kafin daga bisani wani dan tsamurmurin mutum dake sanye da milk riga da wando na shadda,da kuma babbar riga ta koriyar shadda gami da baqaf hula daya karkatata gefe ya qaraso gabansa yana dubansa. Bakinsa cike da gashin baki,kai kace daya daga cikin qabilun da suka shude ne shekaru aru aru.
"Yaro me kake cewa?" Ya fadi yana saba babbar rigar da a zahiri an tafka babbar asara wajen ware shaddar aka masa rigar da ita gaba daya,don kuwa yadin ya masa yawa,alamu ma suna nuna kamar rinjayarsa takeyi
"Gidanmu ne nace,me yasa kuke rushe mana gida?" Ya sake jefa tambayar ga mutumin yana tsareshi da ido da zummar jin ba'asin maganar.
Qaramar dariya yadan saki yana sosa gashin bakinsa da alama qaiqayi yake masa.
"Yaro man kaza......kai!bakasan tsohuwarka ko ince uwarka ta karbi rabin kudin gidan daga hannun matata ba sanda zata bar garin?". Fuska da idanu gaba daya me babban suna ya yamutse yana duban mutumin cike da zallar mamakin da kwanyarsa ta gaza dauka.
" Ko da yake ma.ba fahimta ai zakayi ba,wannan zancan na babanka ne inda yana raye,ba abinda zaka gne yaro" Yana kaiwa nan sai ya juya yana dubaΓ± mgainan
"Kuyi ku raba ku zagaye mana haqqinmu" Da hanzari yasha gaban mutumin jin kalaman da yake sake maimaitawa
"Kada su sake taba mana gida,don nan vidan ba gudan mamata bane da zata saidashi,gidan mahaidinmu ne daya ginashi da guminsa,ta nemeta ta biyata kudinta amma mu ba ruwanmu" Tsaiwa yayi yana qanqance idanu hadi da duban me babban suna
"Kai wannan yaron da alama zakayi tsaurin idanu,da alama dai abinda ake fadi a kanka gaskiya ne......to ai ko kai yanzu ba zakace ga inda uwar data haifeka take ba,tunda ta bazama yawon duniya ta watsar daku.....". Kalmar ta sokeshi qwarai kamar kowanne lokaci. Duk a iya adadin fadar da akeyi bai taba yunqurin kare musu jifan da ake musu da kalmar ba,amma a yau din sai yaji koda sau daya yana da sha'awar huce musu wannan takaicin shi da saddiq.......yana da marmarin maida martani koda sau daya ne tak......amma baya sha'awar bata kariya ko wanketa daga muggan kalaman mutane a kanta,don bashi da abun cewa a kanta,kwata kwata dukkan wata soyayya qauna ko tausayi na fil'azal a tsakaninsu yanxun baya jin akwai burbushinsa,abinda ya sani kawai ya kare kansa ya kare saddiq dinsa
"Ba abunda ya shafemu da inda taje ko inda take.......kaman yadda ba ruwanmu da karbar kudinku da tayi don nan gidan mallakin mahaifinmu ne mallakinmu......abinda muka sani kawai shine mu din halastattun 'ya'yane da aurar ya samar......"
Daya daga cikin ma'aikatan wanda kuma gidan su yake ta qarshen layinsu wanda ke tsaye gaban tsani ne ya bushe da dariya
"Dame kwado yafi gaya ku da shegun?,dame kuka fisu?" Yana kaiwa nan ya dauki qatuwar gudumar da suke dukan saman ginin da ita ya soma taka matattakalar tsanin yana hayewa da zummar ci gaba da aikinsa na ragargazar ginin da mahaifinsu ya kwashe lokaci