Showing 462001 words to 465000 words out of 557259 words
kauda abbanku daga duniya?" Tambayar da tazo daga qasan zuciyarsa kenan,ta kuma sake taso masa da wani irin bacin rai.
β
A hautsine take duban mahaifin nata bayan ya gama gaya mata hanyar mabudin arziqinsa da yake hannunta,bisa tsari da kuma dokar da fu'ad ya bayar.
"Yanaso yayi humiliating dina ne abba......ta yaya zan fita gaban 'yan jarida na tonawa kaina da kaina asiri?....hakan kuma ba yana nufin na wanke kaina da kaina bane?,tamkar kenan na bawa shari'a daman yankemin hukunci da daukan mataki a kaina ta sassauqar hanya?" Ta fada tana jin cewa aikata hakan wani abune da bazai yuwu ba.
"Kina tunanin kina da wani sauran amfani a wajena ne fareeda muddin dukiyar dana kwashe shekara da shekaru zata salwanta ta sanadinki?......ruwanki kimin hanyar dawowar arziqina nasan hanyar xa zaki samu Sasaaucin hukunci.....ruwanki kiqi ni kuma da hannuna zan miqawa hukuma ke......daga rana irin ta wannan lokaci kuma ki tabbatar na cireki daga jerin 'ya'yana.....sunan.Khaled mustapha kuma ya saraya daga wuyanki.....na haramta miki amfani dashi haramtawa na har abada".
"Bazanyi abinda yace ba daddy.....hakanan kaima dukiyar ka zai dawo hannunka" Ta fada tana rarumar wayarta.
Number maamah take nema,hanya guda daya tilo da take tunanin zatabi don samun warwarewar komai.
Daidai lokacin da mota ke tsula gudu da ita saman kwalta,hankalinta yayi nisa yayi kuma zurfi a tunanin tun sanda ta baro wajen boka. Kora yayi mata fata fata akan kada ta sake zuwa masa muddin da maganar data shafi taurari biyu ne sabreen da fu'ad. Ya gama aiki a kansu har abada saidai ta nemi wani.
Sanda ta lallabashi da batun wata buqatar daban tazo da ita ba irin ta baya ba.....buqatarta dankwafar da cikin sabreen yayita zama a mararta ba tare daya girma ba bare a haifeshi,wannan kuma zai zama silar da zai zama karo na farko kuma na qarshe data samu ciki da fu'ad din,a sanya masa shakka kan qaryar ciki tayi dama tun asali.....maganar rabuwarsu kuma ita zataji da sauran.
Har ya soma buga qasa yayi wani zabura da saida qoqunan gabansa gaba daya suka hantsila,yaja baya yana gurnani da wasu surutai kafin daga bisani ya dubeta.
*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
π π π π π π π π
_Zafafabiyar_
ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2
β±§Ιβ²Ιβ₯β³
ππΌππ 131
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
131
"Kinsan aikata hakan daidai yake da kiran mutuwarki da kuma gaggauto da ajalinki tu lokacin mutuwarki baiyi ba?" Sosai abun ya daure mata kai itama,tana kuma buqatar qarin haske.
"Kamar yaya?,ban fahimta ba?". A fusace yake.magana wannan karon fiye da fusatarsa ta dazu.
"Wannan yaran da suke cikinta......bake bama......duk wanda keda qudurin cutar dashi to tabbas ajalinsa yake kira......fiddasu daga mahaifarsu ko hanasu wanzuwa suyi rayuwa irin ta kowanne jariri kuwa,daidai yake da kiran ajali yayin da yake nesa da ruhi.....ki fita daga harkar wadannan taurarin......suna dab da karo da naki taurarin.......tazarar dake tsakaninku kadance,faruwar hakan kuma daidai yake da LALACEWAR RAYUWARKI!.......SAURA QIRIS!.....KI KAUCE KI BASU HANYA.....BA WANI ABU ME CUTARWA DA YA ISA YA TARE HANYAR SHAWAGINSU!" ya fada a tsawace yana nunata da yatsa.
Tashin hankali!,kanta taji ya wani irin sarawa.....muddin ya kasa mata wannan aikin duk duniya bata jin akwai wanda zai iya yinsa
"Kayimin rai.....zan ninka maka abinda ya kamata a......"
"Dakata!" Ya fada a gigice.
"Wannan aikin ba kudi yake buqata ba.......aiki ne na tsira da rai........ran da muddin aka barshi ya dulmiya babu me iya fitowa dashi........KIBAR DA'IRATA HAR ABADA....KARKI SAKE DAWOMIN DA MAGANAR TSARARRUN TAURARI BIYU".
Wannan tunanin yana mata shawagi kiran fareeda ya shigo,ta saka idanunta akan kiran da wani irin yanayi,mamaki ya sanya batayi wani dogon nazari ba ta daga kiran tana sakawa a kunnenta.
"Ina kika shiga fareeda..... Ko kina shirin janyewa ne saga qudurinki?" Ta fadi tanajin kamar idan ta hada kai da fareeda din nasara zata zo mata da gaggawa cikin sauqi,dole tana da buqatar me tayata wannan yaqin.
Ba kalar neman da bata yiwa zuwaira ba amma ta kasa samunta......duk inda take tunanin idan taje zata sameta ta aika ba labarinta,abun yana daure mata kai.
"Ban fasa ba.....kuma sauka daga kan nufina ba.....hasalima tsakiyar aikin da nakeyi aka samu matsala da kuskure". Kanta ya sake sarawa,ta zauna sosai tana riqe wayar a kkunnenta sosai.
" Me ya faru kuma?". Sai data gyara muryarta da kyau sannan tayi magana.
"Nasa anyi attacking na matarsa.....cikin rashin sa'a aka sameshi.....yanzu haka anyi freezing komai na dukiyarmu......yasa kuma an dakatar da dad daga muqaminsa......yana maganar saina fito nayi iqirarin nina aika a kasheshi.....na bada haquri a media sannan zai sakar mana komai.....abinda yasa na kiraki.....inaso ki sakashi ya warware komai......ya janye kuma komai.....muddin wani abun ya sameni duk wani mmuradinmu zai tsaya cak.....don ina da babban shirin da zai kauda mana damuwoyinmu ni dake gaba daya".
Dif maamah din tayi,kwanyarta suna juya mata maganganun fareeda. Haka kawai taji hankalinta kamar ya kasa kama maganganun fareeda din,kaman akwai wani abu da ba daidai ba.
"Fareeda.....bansan qasar da suka kaishi ba.....yanzun haka matarsa ke dauke da cikin da nakejin gwara na nakasa da wanzuwarsa a tare da ita.......bansan inda suka ajeshi ba".
"Taiwan......yana wani asibitu na Taiwanese a taipei......ki kirashi tabbas zaki sameshi".
" Ki dakaceni tukunna.......fu'ad baya cikin mazan da akewa gaggawa haka kuma su karba da sauri".
"Me kike fada mariya?!" Fareeda ta fada a tsawace,a yanayin da take ciki bata qaunar sharhi qarin bayani ko dako......isar da saqonta da cimma burinta kadai take da buqata.
"Kinsan a wanne yanayi muke ciki da har zaki saka bataun JIRA a wannan zancan?......kinsan kowacce daqiqa guda da zata shude muna sake shiga hadari ne nida duk wanda ya dangancemu?......buqata ta gaggawa ce......kiyi hanzarin dakatar da d'anki daga aikata abinda yayi niyyar aiwatarwa......idan kuma ba haka ba to tabbassss bazan shiga uku ni kadai ba......zan shaidawa duniya da hannunki a cikin komai......dollars dina da kika karba kuma.....kada ki manta akwai evidence na amount account details date da time na yadda na saka miki komai.....saiki shirya maidosu" Daga wannan fareeda ta yanke kiran.
Wani sarawa kan maamah taji yayi......lallai idan fareeda ta ambaceta a wannan badaqalar ba abinda zaya hana mutane aminta dasa hannunta.....musamman mutanen dake da issue da ita irin ameenatu da sabreen.....sabreen din da har yanzu tana qarqashin awa saba'in da biyun data bata,awannin da batasan ta yadda zata fiddo fu'ad ba banda yanzun da kiran fareeda ya sanya tasan inda yake.
Karasashinta ya dawo da wani irin sanya ran lallai tana da dama.....damarmaki har guda biyu.....damar sanyashi ya janye kaman yadda fareeda ta buqata,a yadda duk wata kadara tata data mallaka ta narke daga auren fu'ad da sabreen......da kuma neman hanyoyin da zata rabasu batajin tana da adadin dollars din da zata maidawa fareeda kudinta.
Lalubar number dinsa ta fara yi tana jin yadda kanta yaketa sara mata da ciwo. Kira uku tayi,ana hudun sabreen data dauke wayar don ya sake samun nutsuwa taga kiran.
"Maamah" Da sunan yayi serving ba kaman sunan anni da yake suna na daban cikin wayar tasa ba. Qaramin murmushi ta saki,sannan ta taka zuwa bandaki a hankali ta maida qofan ta kulle.
"A yanzun yana buqatar hutu daga dukkan wata takura da zullumi na rayuwa.....yana buqatar yin nesa da kowacce kalar damuwa" Kalaman sabreen kenan da suka sauka a kunnenta suka sanya wayar hannun nata kusan subucewa daga hannun nata,kanta kuma yayi wani dummmm na wucin gadi kafin ta tattara qarfin halinta waje daya.
Magana takeson mata amma ta kasa furta komai,wacce irin HATSABIBIYA ce yarinyar?,a yanzun haka kenan tana taiwan tare dashi ta barta bata cikakken bacci?.
"Duk yadda kike tunanin cin nasara.....kina yiwa kanki qarya ne.....ni mariya a duk sanda nayi nufin cimma nasara akan wani abu.....ba wani wanda ko wani abu daya isa ya dakatar dani daga wannan nasarar....."
"Sai ubangijin da yayi ni yayi ki,ya kuma halicci nasarar........shin da gaske ne kuwa?.....anya ke kika haifi muhammad da musaddiq?" Sabreen tayi mata tambayar da bata taba tunanin zata iya mata ita ba....amma yau ta tsinci kanta da tambayar tata.
Wutace tsaf ta daukewa maamah tana jin jiri yana kamata daga zaune.
"Idanma ya tabbata ke dince.....to ki saka a ranki kin haifawa masoyansu ne su.......sun tashi daga mallakinki.....sun tashi daga ababen kulawarki,ubangji ya musu musaye da masoyansu na haqiqa....."
"Ki dakata da wannan shirmen......ki hadani da d'ana dashi nake buqatar magana" Sabreen bata tsaya sake sauraronta ba ta kashe kiran,ta kuma kashe wayarma gaba daya.
Iska me zafi ta furzar daga bakinta,mamakin maamah yana sake kasheta,a yanzun dai ya tabbata dari bisa dari......dukiya takeso......arziqin take da buqata bawai 'YA'YAN BA.
Mummunan tashi hankalin maamah yayi,ta soma sake gwada kiran number amma a kashe.
"Allah ya tsine miki......muddin banyi sanadinki ba a rayuwa nayi asara" Shine abinda maamah take maimaitawa sanda take yunqurin sake maimaita kiran number fu'ad din ana gaya mata a kashe layin yake.
Sam Allah ya dauke mata basirar kiran musaddiq......tunaninta yafi karkata ga ME ZAI FARU bayan awannin da fareeda ta debar mata tana jiranta?.
*_Hajja_*
Tun sanda suka gama wancan wayar da maamah ko sau daya taqi bawa kwanyarta hutu na neman mafita da hasashen abinda zai wakana......hakanan ta gaza dauke kunnuwanta daga jiran isowar jami'an tsaro gareta suyi awon gaba da ita kaman yadda take hasashe,duk kuwa da bokanta ya shaida mata ba wanda ya isa ya shigo ya kamata muddin ta tabbata a cikin gidanta,saidai idan qafa ta sanya ta fita.
Ta sake amanna da maganarsa ganin kwana dayar har biyu shuru,sai wannan ya bata daman zama tana tunanin matakin da zata dauka akan maamah.
Laila itace burinta......laila da ita take kwana take kuma tashi,yantuwar laila shine muradinta kafin ta waiwayo ga hanyoyin tozarta mariya.
Tsai tayi da ranta tana bitar kalaman da sukayi musaya a wayarsu ta qarshe,ta tsinci tsoro kadan da razana a muryar mariyan,ta yiwu akwai wani abu daban da batasan dashi ba.....ta yiwu ba mmariya bace ta fidda hotonsu.....ta tabbatar tunda hoton maqale yake da nata....duk da fuskarta bata fito sosai ba amma zai wahala mariyan tabari ya fita. Wata shawara ta tsirga mata.....taji a wannan karon ta shirya ayi tone tone tsakaninta da mariya muddin autarta zata dawo cikin hayyacin rayuwarta,wayarta ta dauka kanta tsaye ta fara kiran layin wayarta.
Kamar ana jira ta tsagaita da kiran fu'ad wani kiran ya danno mata waya. Hajja harira,ko kadan kiran bai sakata fargaba ba har sai data daga wayar suka fara musayar magana.
"Da baki wahalar da kanki kina tambayata meye yasa nayi kiranki ba......fuskata da sunana sunyi tambari a bakunan al'umma da kuma kowacce jarida......kina tunanin akwai wani faruwar abun kunya da zanyi shakkar fitarsa?....abun da koda ya fita tawa kunyatar qarama ce akan ta mahaifiyar data sadaukar da mutuncinta da rayukan 'ya'yanta saboda ta mallaki abun duniya?". Kaman babu jini cikin jikin maamah haka takeji......a yanzu takeson solving wannan issue din batabataso hajja ta afko cikin wannan da'irar.....tanaso a sanda hajja zata buqaci a fafata yaqin ta gama da issue din fareeda dana sabreen harma da ameenatu,a sannan zata gwadawa hajja yadda ake wasan kura da rayukan dan adam.
"Hajja......karki tunkari.fadan da bazaki.iya qarasashi ba......ki lallaba masarautar cikin gidanki dake gareki,ki qarasa mulkinki sannu a hankali,ki kuma jirayi randa naga damar 'yanta miki d'iyarki"
Wata dariya data saka numfashin maamah tsaiwa na wucin gadi ta saki,sai da tayi me isarta sannan tace.
"A a'ah......mariyatul kibdiyya......wai ni bakisan abokin mutuwa nake nema ba?....,to bari kiji.......daga yau zuwa gobe na baki ki maidomin da d'iyata gaba na,ko kuma wannan boyayyar fuskar dake gefena a bugun shafin farko na jarida da kowa keson ganinta ta bayyana kanta da kanta.....aikin fahimta ko?" Daga wannan hajja bata jira komai ba ta kashe kiran.
Daga zaunen da take amma sai taji tana jin jiri.......me yasa komai yake neman ya kwabe mata lokaci guda?,kowa adadin awanni yake deba mata cikin umarni da kuma gadara?,wai me yake faruwa ne?.
Daidai nan taji muryar driver dinta yana fadin.
"Mun iso gida.hajiya" Kanta ta daga tana kallon gidan,batasan sanda suka iso ba kaman yadda batasan sanda suka shigo gidan har ya iso parking lot ya tsaida motar ya kuma kasheta ba.
Hannu ta saka ta bude murfin motar,a hankali taja jikinta tana fita a motar,saidai ko Cilakken tsaiwa batayi ba ta yanke jiki ta fadi a wajen hankalinta yana gushewa.
*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
π π π π π π π π
_Zafafabiyar_
ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2
β±§Ιβ²Ιβ₯β³
ππΌππ 132
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
132
Da sallama farouq ya shigo,sabreen dake tsugunne gaban fu'ad din tana gyara masa nails dinshi na qafa duk da fes suke.....amma tsabar bayason tayi nesa dashi ya tsiro mata aikin ta matsa kadan tana amsawa.
"Sannu da aiki addanmu" Ya fada yana jawo kujera ya zauna yana dubanta. Murmushi tayi a kunyace tana amsawa.
"Yauwa BB....sannu da qoqari....Allah y qara zumunci.....ya saka da alkhairi".
" Ameen dai.....dama wani abun saboda ke akeyinsa ai ba don mutum ba" Ya qarasa fada yana jifan fu'ad da harara wanda yayi relax abinsa jikin kujera kaman badashi yake ba.
Miqewa tayi da zummar basu guri.
"Kin gama ne?" Ya fada muryarsa can qasan maqoshi. Kai ta girgiza tana satar kallon farouq tana masa alama dashi. Ya fahimci me take nufi amma ya basar,don haka ta buda baki.
"Zanyi waya dasu huda kafin ku kammala". Agogo ya kalla da narkakkun idanunsa.
" Minti goma ki dawo ki qarasamin"
"Okay sir" Ta fada a girmame ta qarasa tana daukan wayarta ta fice.
Farouq bai jira ta kammala fita din bama ya soma fesar da abinda ke ransa.
"Zuwa nayi na maka sallama". Dariya ya taso ma fu'ad amma ya danneta,sai ya miqe sosai ya zauna yana ware idanunsa akan farouq
"Ina zaka kuma?"
"Gida zanje ayimin aure.....bazan zauna na mutu na tashi a gafiyar lahira ba". Wannan karon dariya ta gasken gaske ya bawa fu'ad,har wanda ke parlor din zai iya jin sautinta,kalan dariyar daya jima rabonshi da irinta.
"Bafa inda zakaje dude.....ko zaka hadiyi zuciya saika gama jinyata ka cikasa ladanka".
"Lada irin naka ne banaso......ina samun ladanka kaima kana samun naka ladan ko?....bazan iya ba....ni yanzu wallahi kafi qarfina" Kai ya jinjina yana shafa sumarsa. Da gaske yasan farouq aure yakeso.....kuma koda shine yake a matsayin farouq din yana sanya auren mace kaman sabreen bayajin zai iya haqurin da yayi ma.......baiga abinda zaiwa farouq ba sama daya tabbatar da aurensu a daidai date din da aka saka.....baya jin zai yarda ya zama silar daga bikin farouq koda na kwana daya ne.
"Ka yiwa pilot nassar magana......ayi booking barinmu taiwan zuwa Nigeria.......inaso larabar nan mu koma gida". Waiwayowa farouq yayi yana kallonsa da mamaki.
"Ina zakaje kana jinya?,ina zakaje bincike kuma bai kammalu ba?". Murmushi ya saki me taushi yana duban farouq din,duba irin na 'yan uwantaka ta jini me cike da dumbin qauna.
"Bincike ya gama kammala farouq......fareeda keda alhakin komai......ta samu nasarar aiwatar da komai dinne ta silar maamah data bata full details din......abu daya da ban sani ba shine.....bata da masaniyar abinda fareeda zatayi dashi?,ko tana da masaniya?,tayi hakanne dukka cikin tsare tsarenta data dauki shekara da shekaru tana gudanarwa?" Ya qarasa maganar duk wata walwala da yake ciki tana sulalewa daga jikinsa. Ba farouq kadai ba,hatta sabreen data dawo da niyyar daukan slipper dinta ta zagaya koda veranda din dakunan saita tsaya tana komawa da baya. Wani irin tausayinsa yana sasuqar zuciyarta. Yadda walwala tayi qaura daga fuskarsa karo daya ya tabbatar mata a yanzu a rayuwarsa bashi da sauran wani ciwo daya wuce MAHAIFIYARSA. A jikinta ta dinga jin cewa......She has to put in effort to help him overcome his past,ya kamata ta sake matsawa sosai cikin rayuwarsa.....yana buqatarta fiye da yadda take hasashen zai kasance.
"No dude.....no.....kada kayi wannan tunanin.....ko yaya ne.....ko yaya kuke da maamah uwa ce.....bana tunanin kowanne kalan hali ne da ita zata iya bada qofa ko daman rabaka da rayuwarka". Idanunsa da suka sauya kala ya maida kan farouq yana dubansa.
"Farouq.....duk yadda zan gaya maka abinda ke nan gurin..." Yayi nuni da qirjinsa da yatsansa.
".....ba zaka fahimta ba.......mun rasa MAHAIFIYA.....MUN RASATA RASHI NA HAR ABADA......saidai na yadda nayi kuma imani,yana cikin rashin cikar kamalar ni'imar mutum cikin DUNIYARSA......cikakkiyar ni'ima tana lahira".
"Duk da haka dude please......ka ajiye wannan a side"
"Na ajiye farouq......fareeda zata girbi duk abinda ta jima tana shukawa.....she must pay.....bawai iya kaina kawai ba". Kai farouq ya jinjina,wani aikine daya shirya gudanarwa da kansa,sai gashi fu'ad din ya rigashi.
"But dude.....inaga kaman ka qarasa warkewa....."
"Noooooo......dole farouq dina ya shiga qwaryar manya as soon