Showing 216001 words to 219000 words out of 557259 words

Chapter 73 - 𝐃𝐔𝐍𝐈𝐘ATA BOOK1 AND 2 HAUSA NOVEL

HUGUMA   

03 Nov 2025

443

Dubansa yayi sanda yake qoqarin shigowa

"Reception zamu wuce.... Already wasu sun fara yin gaba,musaddiq da saddiq tun dazu suna ta wajen". Shi sai a sannan ya tuna ma.baiga kowa cikin su ba,ason ranshi farouq din ya barshi ya koma masauki ya kwanta ya rama baccin dake.kansa,ya kuma rage hayaniyar mutane da yakeji har cikin kansa,saidai kuma ya sani koda yace zai masa bayani ma farouq din ba fahimtarsa zaiyi ba,yadai fadi abu daya

"Ina fatan daga can duk wata hidima ya qare baku qirqiri komai ba kuma......don bazan iya jure zuwa wajen komai ba".

" Wanda baisan halinka bane zai wahalar da kansa shirya wani abu......walimar.ma saboda cika sunna ne da neman albarkar auren" Farouq ya amsa masa yana daga kiran abokinsa da yake gaya musu sun isa wajen

"Muma muna dab......ka jirani" Yace yana sauke wayar. Siririn murmushi kawai fuad ya saki,farouq.....farouq..... Idan ba farouq babu shi.......kaman yadda yasan idan babu shi babu farouq din.

Tunda momma bahijja ta tilastata tayi wanka,ta kuma shirya cikin wata sabuwar atamfar Hilton wax. Cikin kayan da momma ta zare cikin lefen ta bayar aka dinka ba tare da sanin sabreen din ba. Tun tana shiryawa taji shigowar uncle abdulhakeem da tun jiya suka iso suka kwana a tahir guests palace. Zancan duka ya shafi aurenta ne,wanda duk kalma daya da zata fita daga bakin uncle din nata sai taji kanta ya wani sara mata. Zazzafan mutum ne da ta jima bataga mutum me zafi da kafiya akan gaskiya ba irinsa. Ta jima tana tunanin idan ta kammala deal dinta ta tashi matsawa daga gurbin da take zuwa wani ta yaya zata bacewa idanunsa?,ta kuma zullewa duk wata tuhuma tashi?. Taji ya ambaci sunan su huda da nadra da tafi sati tana tunanin ina za'ayi da rayuwarsu?,amma tasan tayi kadan ta tsaya gabansu ta musu wannan tambayar,bata kuma samu jin abinda suke cewa ba sanadiyyar hayaniyar yan tafiya daurin auren data qaru. Ta gama shiryawar taji wani zazzabi ya sauko mata bayan ciwon kanta daya dinga gaba gaba saboda tunanin data matsawa kanta dashi,sai kawai ta lallaba can gadonsu nadra dake qarshe ta haye can ta qudundune.


𝐃𝐮𝐧𝐢𝐲𝐚𝐭𝐚 𝐧𝐚 𝐤𝐮𝐝𝐢 𝐧𝐞
𝟎𝟖𝟏𝟖𝟕𝟐𝟓𝟓𝟖𝟔𝟐

𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀
𝘡𝘢𝘧𝘢𝘧𝘢𝘣𝘪𝘺𝘢𝘳

̶B̶O̶O̶K ̶2

ⱧɄ₲Ʉ₥₳

𝙋𝘼𝙂𝙀 10


Page 10


Can cikin tsakiyar kanta maganganun mutane ke mata yawo sanda motar ke tafiya cikin nutsuwa saman lafiyayyar kwaltar dake shimfide a kanta. Muryoyin mutane daban daban da sukayi mata fadan shiga gidan miji wai a cewarsu

"Allah yasa dai ki iya zama......don zaman aure daban da zaman bariki,zaman gidan miji daban da yawon bariki" Muryar bibo kenan da nata salon fadan da yafi kama da turun mutuwa

"Da dadi ba dadi kiyi haquri ki zauna......Allah yasa mutuwa ce zata raba,kiji kiqi ji,ki gani kiqi gani" Muryar daada kenan wadda ta kama hannuwanta tana fada muryarta a sanyaye. Ko da can ba zatace ga wani mummunan abu da daada ta taba musu ba,ita dai barta da shariya da rashin shiga lamari da sabgar kowa cikin gidan. Idan ka ganta kuwa a ciki to tabbas abu yaci tura,amma bibo da yaabi koda dan wani akeyi suna iya ara su yafa tun usul.

"Mommaa......nadra.....haneefa.....huda" Sunayen data iya kirawa momma kenan sanda take yunqurin sakata a cikin motar da zata yi musu jagora zuwa inda zasuje.

"Ina sane dasu......kuna su din ba nauyinki bane" Ta amsa masa a tausashe.

Ta cikin lafayar jikinta take iya hangen yadda motar ke tsala gudu abinta,amma saboda lafiyar motar da irin tsarin da akayi mata zaka rantse ba gudun takeyi ba.

Ta maida idanunta ta lumshe,wasu hawaye da batasan sanda suka taru ba suka biyo kuncinta suka diga bayan hannunta dake ajiye saman cinyarta. Har yanzu dai ta kasa gasgata abinda take gani,har yanzu ta kasa gasgata abinda kunnuwanta da zuciyarta ke nanata mata.

Da gaske mutumin nan yaci galaba a kanta da dukka tsarikansa.....da gaske shike da nasara ba ita ba.......da gaske ya cinye wasan a wannan gabar.....saidai kuma hakan baya nufin zaita nasara kenan a kanta,hakan baya nufin ta fadi kenan har abada.....lallai zata canza labarin......zata canza qaddarar da dukkan iyawarta.

"Gidan mamarshi zamu fara shiga.......sai gidan riqonsa,kamar haka matar data shigo dazu tace ko?" Daada ta fadi tana dan duban momma bahijja da hannun sabreen yake cikin nata.

"Eh haka ne" Ta amsa mata idanunta sauke kan faffadan sabon gate din gidan maamah dake nuna zallar dukiyar dake narke cikin gidan.

A nutse jerin gwanon motocin suka cusa kai makekiyar harabar gidan data kasance mafarkin maamah na shekara da shekaru,gidan daya dauki hankula da bakunan dukkan jama'arta dake hulda da ita. Gidan da a cikin ranta ita kanta ta gamsu da dukiyar daya lashe,amma zuciyarta bata gama nutsuwa da hakan ba saboda har yanzu gidan alhj hamza kibiya da iyalinsa yafi nata girma yalwa da kuma tsari,ba tare data duba yawan da suka darata dashi ba,da kuma yawan al'umman da gidan ke dauka suke riqo a yanzu haka.

Tunda motar ta tsaya a parking lot na gidan gabanta yake wani irin faduwa,ta maida idonta ta lumshe tana sauraren bugun da zuciyarta keyi da bata taba jin irinsa ba,sai taji bugun har kusa da maqogoronta. Sake runtse idanunta tayi sanda momma bahijja ke fadin ta fito,tana jin bugun zuciyar na sake daduwa amma kuma ta rasa me ya kamata ta karanta?,wacce addu'a ce ta dace da irin wannan yanayin da takejin kanta a ciki?.

Riqon hannunta da momma din tayi shine ya sassauta mata abinda takeji kadan,ta sake riqe momma din itama da kyau ba tare tasan ta yadda zata gaya mata abinda takeji cikin qirjinta ba.

A dan hanzarce ta shigo dakin nata,sannan ta maida qofar ta kulle ta kuma murza key. Da dan hanzarin still ta isa gaban madubin nata dake manne da wasu lafiyayyun lockers. Ta murza daya daga ciki ta bude ta,sannan ta saka hannu ta ciro baqar ledar dake a ciki ta dora saman madubi. Ko ina a jikinta amsawa yakeyi da wani irin doki da son fara aiwatar da nata aikin,a yau batasan sau dubu nawa tana addu'ar samun wannan sa'ar ba......batasan sau nawa ta roqi samun nasara a wannan ranar ba,nasarar da indai ta rasata kamar wadancan kwanakin ta tabbatar komai zaizo mata da wahalar gaske.....batasan kuma ta yadda zata tari abun ba.

Kusan leda shidda ce,kowacce sai data kunceta sannan ta saka hannu ta fara ciro kayan ciki. Kusan tarkace ne a idanun me kallo,amma a wajen maamah gwara rashin million dubu da rasa daya daga cikin kayan. Wasu kwalabe ne masu dauke da wani irin baqin abu a ciki,wani kuma kore kore ne,saidai yana da dan qamshi qamshi kadan a ciki mara qarfi. Ta bude kowanne ta tsiyaya cikin tafin hannunta,ta kuma mulke hannun nata da kyau kamar yadda aka umarceta da tayi,sannan ta maida komai muhallinsa kamar bata taba komai ba cikin dakin.

Gaban madubin ta tsaya tana qoqarin controlling kanta da daidaita nutsuwarta. Idanun ta fes cikin fuskarta tana maganar zucci da kanta da kanta,wanda batayi wani nisa ba knocking din da ake mata ya isa kunnuwanta. Adan fusace tace tambaya don bata buqatar doguwar mu'amala da kowa har sai wadda tayi shirin saboda ita ta iso

"Zuwaira ce" Ta bata amsa a tsanake.

"Sun iso,suna falon qasa sun......."

"Gani nan" Ta tari numfashin zuwairan ba tare data jira sauran bayaninta ba. Ba sauran bayaninta take da buqatar ji ba,tunda taji abinda take buqatar jin,ta waiwaya tana zura takalmanta data cire tare da kallon tsadajjen mayafin data lullube jikinta dashi ta tabbatar ya zauna a jikinta......ya sanyata tayi kwarjini da wata irin kamala da sam zai wahala ka kawo wani abu me muni a kanta. Kyanta ya bayyana.....kamanninta da musaddiq sosai,yanayin jin dadin da kulawar data samu wadda take rainawa ta sake sanyawa jikinta ya murje sosai,hutu da quruciya sun bayyanar mata.

Murmushi ta sakarwa kanta da kanta,sannan ta juya a hankali tana fita a dakin.

Tun daga saman stairs din take raba idanunta tana son hangota. Bata wani sha wahala ba,ta hangeta zaune saman lallausan carpet din da aka qawata tsakiyar falon dashi. Qafafunta a tanqwashe suke,kanta a qasa cikin shigar laffayar da tazo mahadin lace din da aka zauna akyi dukka adon jikinsa da hannu(handmade lace),kamar yadda lafayar jikinta itama duk wani zare da duwatsun jiki da hannu aka gameshi. Abune na masu dashi,ba wani cikar jama'a masu yawa ko cinkoso,kowa yana zaune a nutse,yayin da gaisuwa ke wakana tsakaninsu momma da jama'ar da suka samu cikin falon.

Da wani irin kirki na gasken gaske saman fuskarta,faffadan murmushi da fara'a me nuna tsantsar maraba da baqo ta iso rukunin kujerun tana furta

"Lale maraba......sannunku da zuwa......sannunku da qoqari" Da murmushi a fuskar momma ta amshe maraban tana duban maamah tsaf tare da karantar yanayinta.

"Bari na zauna kusa da diyata" Ta fadi tana zama kujerar dake kusa da sabreen din.

Gaisuwa akayi cikin mutunci dason nuna ainihin zallar kirkinta,suka gabatar mata da amanar sabreen tare da dan qaramin jawabin girmama kowa ga sabreen din

"Itama diyata ce ai tunda yarona take aure,kuma in sha Allah zakuyi alfahari da hada alaqa damu,Allah ya bada zaman lafiya,shi kuma Allah ya tayashi riqo" Maamah ta furta cikin zaquwa da gajiya da bayanan. So take kawai ta isa ga muradinta.

"Am nace ba.....idan ba damuwa inason ganin diyata a kebance,minti biyar don Allah" Maamah ta fada tana murmushi. Ba tare da tunanin komai ba ko kawo komai ba momma bahijja tace

"Bismillah mana......haba hajiya ai diyarku ce" Daada ta fadi yadda momma din ta karbi sabreen yana burgeta.

Duk da tayi gaba zuwaira ke mata jagora zuwa wani daki na daban a saman benen.....amma saita dinga jin wani irin yanayi yana bibiyar gabobinta.

Kasa zama tayi,tana a tsaye sanda taji zuwaira taja musu qofar ta fice.

"Zauna mana.....ki yaye wannan lullubin kan naki......don fahimtata nakeso kiyi sosai tamkar yau ne karon farko da kika fara fahimta ko haddace wani abu a rayuwarki" Tayi maganar cikin jerarrun kalmomin da kana jinsu zakasan ko meye zata fada yana da matuqar muhimmanci a wajenta.

Sai data fara janye lullubin nata baya,sannan ta sulale a wajen ta zauna. Tana jin kamar babu wani sauran qwarin gwiwa daya rage mata a rayuwa,duk da yadda take kokawa da zuciyarta da qoqarin qarfafawa kanta gwiwa.

"To alhamdulillah.......komai ya kammala,kuma komai yazomin da sauqi fiye da yadda nayi zato ko kuma tsammani........ina fata baki manta meye manufar aurenmu ba?" A nutse sabreen din ta daga kai sannan ta zube mata idanunta saman fuskarta. Kallonta tayi na second kusan goma sannan ta gyada kai

"Da kyau.....da farko abinda zan fara gaya miki shine abinda na maimaita miki a baya.......qaidar contract dina na farko shine sirri.......inason sirri,don muddin aikin nan ya fita daga da'irar sirri zuwa wata da'ira ta daban.....to tamkar kin wargaza rayuwarki da hannunki ne......bayan taki rayuwar da kika wargaza kuma......kin wargaza ta 'yan uwanki suma...." Daga ma maamah hannu tayi da hanzari tana zare idanunta daga kanta

"Ki tsaya iya kan ameenatu kawai......huda,nadra da haneefa,tabasu ko sako sunansu cikin sabgarki da ameenatu tamkar ganganci ce"

"Da kyau!" Maamah ta furta tana sakin murmushi,abubuwa biyu zuwa uku suna jan hankalinta. Gyara zamanta tayi tana ci gaba da murmushi

"Ashe ameenatu ce....abu yayi kyau..ameenatu ta bata,wata ameenatun zata gyara,wannan abun yayimin dadi.......qwarin gwiwarki da rashin sarewarki ya burgeni......kariyar da kike bawa qannenki tana da yawa,kuma ita dai ta isa ta bani yaqini da tabbacin ba zaki bari a samu failure ba ko don saboda su......."

"Shiga maganarki kai tsaye" Sabreen ta fadi mata tana kauda kanta zuwa wani sashe na daban. Idanu maamah tadan zuba mata har yanzu tana murmushi,sai kuma ta miqa hannu ta zaro wata paper da abun rubutu ta ajiye a gabanta.

"Inaso ki rubuta adadin kudaden da kike da burin mallaka a rayuwarki......ni kuma zan mallaka miki su a madadin sadakin aikinki,zan kuma qara miki kwatankwacinsu muddin komai yayi daidai".

Fararen manyan idanunta ta daga ta watsawa maamah su,karon farko da idanun suka yiwa maamah din wani kwarjini da bata taba jin irinsa ba. Murmushin da ya subuce kuma a fuskar sabreen ya sanya mata kokwanto

"Ki fadi magana me muhimmanci saboda mutanen dake zaman jiranki a qasa" . Maganar tata tadan daure mata kai,a nata ganin ba wata magana da zata zama me muhimmanci a wajen sabreen sama da maganar kudin aikinta,wanda take ganin shi kadai ya isa ya bata azama akan aiwatar mata da komai. To amma akance......shi yaqi dan zamba ne,don haka ta gyada kai



𝗗𝘂𝗻𝗶𝘆𝗮𝘁𝗮 𝗻𝗮 𝗸𝘂𝗱𝗶 𝗻𝗲
𝟬𝟴𝟭𝟴𝟳𝟮𝟱𝟱𝟴𝟲𝟮


𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀

̶𝗕̶𝗢̶𝗢̶𝗞 ̶𝟮

ⱧɄ₲Ʉ₥₳

𝙋𝘼𝙂𝙀 𝟭𝟭


𝗣𝗮𝗴𝗲 𝟭𝟭


"𝗡𝗮𝗷𝗶 𝗱𝗮𝗱𝗶 𝗱𝗮 𝗸𝗶𝗸𝗮 𝘇𝗮𝗺𝗮 𝗺𝗲 𝗹𝘂𝗿𝗮 𝗮𝗸𝗮𝗻 𝗸𝗼𝗺𝗮𝗶,𝘄𝗮𝗻𝗻𝗮𝗻 𝘇𝗮𝗶 𝘀𝗮𝗻𝘆𝗮 𝗸𝗼𝗺𝗮𝗶 𝘆𝗮𝘇𝗼 𝗱𝗮 𝘀𝗮𝘂𝗾𝗶........𝗮𝗶𝗸𝗶𝗻𝗮 𝗺𝗲 𝘀𝗮𝘂𝗾𝗶 𝗻𝗲 𝗶𝗱𝗮𝗻 𝗸𝗶𝗻𝗯𝗶 𝘆𝗮𝗱𝗱𝗮 𝗻𝗮𝗰𝗲 𝗺𝗶𝗸𝗶,𝗰𝗶𝗸𝗶𝗻 𝘄𝗮𝘁𝗮𝗻𝗻𝗶 𝗸𝗮𝗱𝗮𝗻 𝗺𝗮 𝗸𝗶𝗻𝗮 𝗶𝘆𝗮 𝗸𝗮𝗺𝗺𝗮𝗹𝗮𝘄𝗮 𝗸𝗶 𝘄𝘂𝗰𝗲 𝗮𝗯𝗶𝗻𝗸𝗶,𝗮𝗸𝘄𝗮𝗶 𝗻𝗮 𝘀𝗮𝘄𝗮 𝗮 𝗮𝗯𝗶𝗻𝗰𝗶,𝘀𝗮𝗶𝗻𝗮 𝗿𝘂𝘄𝗮𝗻 𝘄𝗮𝗻𝗸𝗮,𝘀𝘂 𝗸𝗲𝗻𝗮𝗻 𝗱𝗮 𝗻𝗮𝗸𝗲 𝗱𝗮 𝗯𝘂𝗾𝗮𝘁𝗮𝗿 𝗮 𝗸𝗼𝘄𝗮𝗰𝗰𝗲 𝗿𝗮𝗻𝗮 𝗸𝗼𝗱𝗮 𝘀𝗮𝘂 𝗱𝗮𝘆𝗮 𝗻𝗮𝗰𝗶𝗻 𝘆𝗮 𝘀𝗵𝗶𝗴𝗮 𝗰𝗶𝗸𝗶𝗻𝘀𝗮,𝗻𝗮 𝘄𝗮𝗻𝗸𝗮𝗻 𝗸𝘂𝗺𝗮 𝘆𝗮 𝗸𝗮𝘀𝗮𝗻𝗰𝗲 𝗮 𝗰𝗶𝗸𝗶𝗻 𝗿𝘂𝘄𝗮𝗻 𝘄𝗮𝗻𝗸𝗮𝗻𝘀𝗮,𝗶𝗱𝗮𝗻 𝗻𝗮 𝘀𝗮𝗺𝘂 𝘄𝗮𝗻𝗻𝗮𝗻 𝘀𝗮𝘂 𝗱𝗮𝘆𝗮 𝘁𝗮𝗸 𝗮 𝗿𝗮𝗻𝗮 𝗺𝗮 𝘆𝗮 𝘄𝗮𝗱𝗮𝘁𝗮𝗿. 𝗜𝗻𝗱𝗮𝗶 𝗵𝗮𝗸𝗮𝗻 𝘆𝗮 𝘀𝗮𝗺𝘂 𝗶𝗻𝗮 𝗺𝗲 𝗺𝗶𝗸𝗶 𝗮𝗹𝗯𝗶𝘀𝗵𝗶𝗿 𝗱𝗶𝗻 𝗸𝘄𝗮𝗻𝗮 𝗰𝗮𝘀𝗮'𝗶𝗻 𝘄𝗮𝘁𝗮𝗻𝗻𝗶 𝘂𝗸𝘂 𝗸𝗮𝗰𝗮𝗹 𝗸𝗼𝗺𝗮𝗶 𝘇𝗮𝗶 𝘀𝗮𝘂𝘆𝗮 𝗱𝗮𝗶𝗱𝗮𝗶 𝗱𝗮 𝘆𝗮𝗱𝗱𝗮 𝗻𝗮𝗸𝗲𝘀𝗼......𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗿𝗮𝗻𝗮𝗿 𝗸𝗶𝗻 𝘇𝗮𝗺𝗮 '𝘆𝗮𝗻𝘁𝗮𝗰𝗰𝗶𝘆𝗮.....𝗮𝗸𝘄𝗮𝗶 𝗸𝗮𝘆𝗮𝗻 𝗮𝗶𝗸𝗶𝗻,𝗴𝗼𝗯𝗲 𝗯𝗮𝘀𝗮𝗶 𝗷𝗶𝗯𝗶 𝗯𝗮 𝘇𝗮𝗻 𝗮𝗶𝗸𝗼 𝗮𝗺𝗶𝗻𝘁𝗮𝗰𝗰𝗶𝘆𝗮𝘁𝗮,𝗸𝘂𝗺𝗮 𝘇𝗮𝘁𝗮 𝘁𝗮𝘆𝗮𝗸𝗶 𝘇𝗮𝗺𝗮 𝗻𝗮 𝘄𝗮𝗱𝗮𝗻𝗻𝗮𝗻 𝗸𝘄𝗮𝗻𝗮𝗸𝗶𝗻 𝗮 𝗺𝗮𝘇𝗮𝘂𝗻𝗶𝗻 '𝘆𝗮𝗿 𝗮𝗶𝗸𝗶 𝗵𝗮𝗿 𝗸𝗶 𝗸𝗮𝗺𝗺𝗮𝗹𝗮 𝗮𝗶𝗸𝗶𝗻𝗸𝗶 𝗸𝗶𝘆𝗶 𝗴𝗮𝗯𝗮........𝘆𝗮𝗱𝗱𝗮 𝘇𝗮𝗸𝗶 𝘇𝗮𝘂𝗻𝗮 𝗱𝗮 𝗳𝘂𝗮𝗱 𝗸𝘂𝗺𝗮 𝘄𝗮𝗻𝗻𝗮𝗻 𝘇𝗮𝗯𝗶𝗻𝗸𝗶 𝗻𝗲.......𝘀𝗮𝗶𝗱𝗮𝗶 𝗸𝘂𝗺𝗮 𝘇𝗮𝗻 𝗴𝘂𝘁𝘀𝘂𝗿𝗮 𝗺𝗶𝗸𝗶 𝗸𝗮𝗱𝗮𝗻 𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗵𝗮𝗹𝗮𝘆𝗲𝗻𝘀𝗮 𝗱𝗼𝗻 𝗸𝗶 𝗸𝗶𝘆𝗮𝘆𝗲 𝗸𝘂𝗺𝗮 𝗸𝗼𝗺𝗮𝗶 𝘆𝗮𝘇𝗼 𝗺𝗶𝗸𝗶 𝗱𝗮 𝘀𝗮𝘂𝗾𝗶......"

"𝗕𝗮𝗯𝘂 𝗯𝘂𝗾𝗮𝘁𝗮" 𝗧𝗮 𝗳𝗮𝗱𝗮 𝗸𝗮𝗻𝘁𝗮 𝘁𝘀𝗮𝘆𝗲,𝘀𝗮𝗻𝗻𝗮𝗻 𝘁𝗮 𝗺𝗶𝗾𝗲 𝘁𝘀𝗮𝘆𝗲 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝗴𝘆𝗮𝗿𝗮 𝗹𝘂𝗹𝗹𝘂𝗯𝗶𝗻𝘁𝗮. 𝗪𝗮𝗻𝗶 𝗶𝗿𝗶𝗻 𝗺𝗮𝗺𝗮𝗸𝗶 𝗸𝗲 𝗵𝗮𝗷𝗶𝗷𝗶𝘆𝗮 𝗱𝗮 𝘇𝘂𝗰𝗶𝘆𝗮𝗿𝘁𝗮 𝘀𝗮𝗻𝗱𝗮 𝘁𝗮𝗸𝗲 𝘀𝗮𝘂𝗸𝗼𝘄𝗮 𝗱𝗮𝗴𝗮 𝘀𝗮𝗺𝗮𝗻,𝗯𝗮𝗻𝗱𝗮 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝗸𝗮𝗺𝗮 𝗾𝗮𝗿𝗳𝗲𝗻 𝘀𝘁𝗮𝗶𝗿𝘀 𝗱𝗶𝗻 𝘄𝗮𝗹𝗮 𝗮𝗹𝗹𝗮 𝘇𝗮𝘁𝗮 𝗶𝘆𝗮 𝗵𝗮𝗿𝗱𝗲𝘄𝗮. 𝗔𝗻𝘆𝗮 𝗸𝘂𝘄𝗮 𝘄𝗮𝗻𝗻𝗮𝗻 𝗱𝗶𝗻 𝗨𝗪𝗔 𝗖𝗘?,𝗨𝗪𝗔 𝗖𝗘 𝗰𝗶𝗸𝗶𝗻 𝗵𝗮𝗹𝗶𝘁𝘁𝗮𝗿 𝗯𝗶𝗹'𝗮𝗱𝗮𝗺𝗮?,𝗸𝗼 𝗸𝘂𝘀𝗮 𝘂𝘄𝗮 𝗰𝗲 𝗰𝗶𝗸𝗶𝗻 𝘄𝗮𝗻𝗶 𝗷𝗶𝗻𝘀𝗶 𝗸𝗼 𝗵𝗮𝗹𝗶𝘁𝘁𝗮 𝘁𝗮 𝗱𝗮𝗯𝗮𝗻?. 𝗕𝗮𝘁𝗮𝘀𝗮𝗻 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝗯𝗶𝘆𝗲 𝗱𝗮 𝗶𝘁𝗮 𝗯𝗮 𝘀𝗮𝗶 𝗱𝗮𝘁𝗮𝗷𝗶 𝗺𝘂𝗿𝘆𝗮𝗿𝘁𝗮 𝘀𝗮𝗻𝗱𝗮 𝘁𝗮𝗸𝗲 𝘁𝘀𝘂𝗴𝘂𝗻𝗻𝗮𝘄𝗮 𝗴𝗮𝗯𝗮𝗻 𝗺𝗼𝗺𝗺𝗮 𝗯𝗮𝗵𝗶𝗷𝗷𝗮 𝗱𝗼𝗻 𝘁𝗮𝘀𝗮𝗻 𝘁𝗮 𝗾𝗮𝗿𝗮𝘀𝗼. 𝗕𝗮 𝘇𝗮𝘁𝗼 𝘁𝗮 𝘁𝘀𝗶𝗻𝗰𝗲𝘁𝗮 𝗮 𝗴𝗮𝗯𝗮𝗻𝘁𝗮 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝗳𝗮𝗱𝗶𝗻

"𝗟𝗮𝗹𝗹𝗮𝗶 𝘆𝗮𝗿𝗼𝗻𝗮 𝘆𝗮 𝗱𝗮𝗰𝗲,𝗻𝗮𝘆𝗶 𝗳𝗮𝗿𝗶𝗻𝗰𝗶𝗸𝗶 𝗱𝗮 𝘀𝗮𝗺𝘂𝗻 𝘀𝘂𝗿𝘂𝗸𝗮 𝗶𝗿𝗶𝗻 𝘄𝗮𝗻𝗻𝗮𝗻....𝗔𝗹𝗹𝗮𝗵 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝗺𝗶𝗸𝗶 𝗮𝗹𝗯𝗮𝗿𝗸𝗮" 𝗧𝗮 𝗾𝗮𝗿𝗮𝘀𝗮 𝗳𝗮𝗱𝗮 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝗮𝘇𝗮 𝗵𝗮𝗻𝗻𝘂𝗻𝘁𝗮 𝘀𝗮𝗺𝗮𝗻 𝗸𝗮𝗻 𝘀𝗮𝗯𝗿𝗲𝗲𝗻 𝗱𝗮 𝘀𝗶𝗴𝗮𝗿 𝘀𝗮𝗻𝘆𝗮 𝗮𝗹𝗯𝗮𝗿𝗸𝗮.

𝗬𝗮𝗺𝗺𝗺𝗺 𝘁𝗮𝗷𝗶 𝘄𝗮𝗻𝗶 𝗶𝗿𝗶𝗻 𝗮𝗯𝘂 𝘆𝗮𝗻𝗮 𝗯𝗶𝗻 𝗸𝗼𝘄𝗮𝗻𝗻𝗲 𝘀𝗮𝘀𝗵𝗲 𝗻𝗮 𝗷𝗶𝗸𝗶𝗻𝘁𝗮. 𝗖𝗶𝗸𝗶𝗻 𝗸𝗼𝘄𝗮𝗻𝗻𝗲 𝗵𝗮𝗿𝗯𝗮𝘄𝗮 𝗷𝗶𝗻𝗶 𝗱𝗮𝗸𝗲 𝘇𝗮𝗴𝗮𝘆𝗮𝘄𝗮 𝗴𝗮 𝗷𝗶𝗷𝗶𝘆𝗼𝘆𝗶𝗻𝘁𝗮 𝘄𝗮𝗻𝗶 𝗶𝗿𝗶𝗻 𝘀𝗮𝗾𝗼 𝗱𝗮 𝘀𝗮𝘂𝘆𝗲 𝘀𝗮𝘂𝘆𝗲 𝘀𝘂𝗸𝗮 𝗳𝗮𝗿𝗮 𝗮𝗳𝗸𝘂𝘄𝗮 𝗱𝗮 𝘄𝗮𝗻𝗶 𝗶𝗿𝗶𝗻 𝘀𝗮𝘂𝗿𝗶 𝗱𝗮 𝗸𝘂𝗺𝗮 𝗴𝗮𝗴𝗴𝗮𝘄𝗮 𝗺𝗲 𝘆𝗮𝘄𝗮𝗻 𝗴𝗮𝘀𝗸𝗲

"𝗔𝗹𝗹𝗮𝗵 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝗺𝗶𝗸𝗶 𝗮𝗹𝗯𝗮𝗿𝗸𝗮" 𝗧𝗮 𝘀𝗮𝗸𝗲 𝗺𝗮𝗶𝗺𝗮𝗶𝘁𝗮 𝗸𝗮𝗹𝗺𝗮𝗿 𝘀𝗮𝘂 𝘂𝗸𝘂 𝗱𝗼𝗻 𝘁𝗮𝗻𝗮𝘀𝗼𝗻 𝗮𝗱𝗮𝗱𝗶𝗻 𝘀𝗮𝗸𝗮𝗻𝗻𝗶𝗻 𝘀𝘂 𝗰𝗶𝗸𝗮 𝗸𝗮𝗳𝗶𝗻 𝘁𝗮 𝗱𝗮𝘂𝗸𝗲 𝗵𝗮𝗻𝗻𝘂𝗻 𝗻𝗮𝘁𝗮 𝗱𝗮𝗴𝗮 𝘀𝗮𝗺𝗮𝗻 𝗸𝗮𝗻𝘁𝗮

"𝗔𝗺𝗲𝗲𝗻 𝘆𝗮 𝗔𝗹𝗹𝗮𝗵......𝗮𝗺𝗲𝗲𝗻 𝘆𝗮 𝗿𝗮𝗯𝗯𝗮𝗹 𝗔𝗮𝗹𝗮𝗺𝗶𝗻" 𝗠𝘂𝘁𝗮𝗻𝗲𝗻 𝘄𝗮𝗷𝗲𝗻 𝗸𝗲 𝗮𝗺𝘀𝗮𝘄𝗮 𝗱𝗮𝘀𝗵𝗶.

𝗛𝗮𝗻𝗻𝘂𝗻 𝘁𝗮 𝗱𝗮𝘂𝗸𝗲 𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗸𝗮𝗻𝘁𝗮,𝘁𝗮 𝘀𝗮𝗻𝘆𝗮 𝗵𝗮𝗻𝗻𝘂𝘄𝗮𝗻𝘁𝗮 𝗱𝘂𝗸𝗸𝗮 𝗯𝗶𝘆𝘂𝗻 𝘁𝗮 𝗱𝗮𝗴𝗼𝘁𝗮 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝗳𝘂𝘀𝗸𝗮𝗻𝘁𝗮𝗿𝘁𝗮

"𝗧𝗮𝘀𝗵𝗶 𝗸𝗶 𝘄𝘂𝗰𝗲 𝗴𝗶𝗱𝗮𝗻𝗸𝗶......𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗻𝗮𝗻 𝗸𝘂 𝗸𝗮𝗶𝘁𝗮 𝗴𝗶𝗱𝗮𝗻𝘁𝗮 𝗸𝗮𝗶 𝘁𝘀𝗮𝘆𝗲......𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗯𝗮𝘆𝗮 𝗱𝗮 𝗸𝗮𝗻𝘀𝗵𝗶 𝘆𝗮 𝗿𝗮𝗸𝗮𝘁𝗮 𝗶𝗻𝗱𝗮 𝘆𝗮 𝗱𝗮𝗰𝗲 𝘁𝗮𝗷𝗲 𝗱𝗶𝗻.....𝗸𝗶𝗻𝗷𝗶 𝗱𝘂𝗸𝗸𝗮 𝗯𝗮𝘆𝗮𝗻𝗮𝗶𝗻𝗮 𝗸𝗼?" 𝗦𝗮𝗺𝘂𝗻 𝗸𝗮𝗻𝘁𝗮 𝘁𝗮𝘆𝗶 𝗱𝗮 𝗴𝘆𝗮𝗱𝗮 𝗺𝗮𝘁𝗮 𝗸𝗮𝗶 𝗱𝗮 𝘄𝗮𝗻𝗶 𝗶𝗿𝗶𝗻 𝗺𝘂𝗴𝘂𝗻 𝘀𝗮𝗻𝘆𝗶𝗻 𝗷𝗶𝗸𝗶 𝗱𝗮 𝗯𝗮𝘁𝗮 𝘁𝗮𝗯𝗮 𝗷𝗶𝗻 𝗶𝗿𝗶𝗻𝘀𝗮 𝗯𝗮,𝘀𝗮𝗶𝘁𝗮 𝗷𝗮𝘄𝗼𝘁𝗮 𝘁𝗮 𝗿𝘂𝗻𝗴𝘂𝗺𝗲𝘁𝗮 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝘀𝗮𝗸𝗲 𝘀𝗮𝗸𝗲 𝗺𝗮𝘁𝗮 𝘄𝗮𝘀𝘂 𝗮𝗱𝗱𝘂'𝗼'𝗶𝗻,𝗮𝗯𝗶𝗻𝗱𝗮 𝘆𝗮 𝘀𝗮𝗻𝘆𝗮 𝘁𝗮𝗷𝗶 𝗸𝗮𝗻𝘁𝗮 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝘄𝗮𝗻𝗶 𝗶𝗿𝗶𝗻 𝘀𝗮𝗿𝗮𝘄𝗮,𝘁𝗮𝗸𝗲 𝗰𝗶𝘄𝗼𝗻 𝗸𝗮𝗶 𝘆𝗮 𝘀𝗮𝘂𝗸𝗮𝗿 𝗺𝗮𝘁𝗮.

𝗦𝗮𝘂𝗸𝗲 𝗹𝗮𝗯𝘂𝗹𝗲 𝗮𝗺𝗻𝗮 𝘁𝗮𝘆𝗶 𝗮 𝗸𝗮𝗿𝗼 𝗻𝗮 𝗯𝗮𝗯𝘂 𝗮𝗱𝗮𝗱𝗶,𝘀𝗮𝗻𝗻𝗮𝗻 𝘁𝗮 𝗺𝗮𝗶𝗱𝗮 𝗱𝘂𝗯𝗮𝗻𝘁𝗮 𝗸𝗮𝗻 𝗮𝗻𝗻𝗶 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝗻𝗮𝗿𝗸𝗲 𝗳𝘂𝘀𝗸𝗮 𝗸𝗮𝗺𝗮𝗿 𝘇𝗮𝘁𝗮 𝘀𝗮𝗸𝗶 𝗸𝘂𝗸𝗮

"𝗔𝗻𝗻𝗶 𝗱𝗮𝗿𝗲 𝗳𝗮 𝘆𝗮 𝗿𝗶𝗴𝗮 𝘆𝗮𝘆𝗶,𝗵𝗮𝗿 𝘆𝗮𝗻𝘇𝘂 𝗯𝗮𝘀𝘂 𝘀𝗵𝗶𝗴𝗼 𝗱𝗮 𝗶𝘁𝗮 𝗯𝗮.....𝗸𝘂𝗺𝗮 𝘆𝗮𝗮 𝗺𝘂𝘀𝗮𝗱𝗱𝗶𝗾 𝘆𝗮𝗰𝗲 𝘀𝘂𝗻 𝘀𝗵𝗶𝗴𝗮 𝘄𝗮𝗷𝗲𝗻 𝗺𝗮𝗮𝗺𝗮𝗵....𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗰𝗮𝗻 𝗸𝘂𝗺𝗮 𝘀𝗮𝗶 𝗻𝗮𝗻". 𝗔 𝗻𝘂𝘁𝘀𝗲 𝗮𝗻𝗻𝗶 𝘁𝗮 𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗸𝗮𝗻𝘁𝗮 𝗱𝗮𝗴𝗮 𝘇𝗮𝗿𝗲 𝘄𝗮𝗿𝘄𝗮𝗿𝗮𝘆𝗲𝗻 𝗵𝗮𝗻𝗻𝘂𝗻𝘁𝗮 𝗱𝗮 𝘁𝗮𝗸𝗲𝘆𝗶 𝘁𝗮 𝗺𝗮𝗶𝗱𝗮 𝗸𝗮𝗻 𝗮𝗺𝗻𝗮

"𝗠𝗲 𝗸𝗶𝗸𝗲 𝗰𝗶 𝗻𝗲 𝗻𝗮 𝗯𝗮𝗸𝗮 𝘆𝗮𝗻𝗮 𝘇𝘂𝗯𝗮 𝗮𝗺𝗻𝗮?,𝗰𝗶 𝗱𝗮 𝘇𝘂𝗰𝗶?,𝘆𝗮𝘆𝗮𝗿𝗸𝗶 𝗰𝗲 𝗳𝗮?,𝗵𝗮𝗿 𝘀𝗮𝗶 𝗸𝗶𝗻 𝗴𝗮𝗷𝗶 𝗱𝗮 𝗴𝗮𝗻𝗶𝗻𝘁𝗮 𝘄𝗮𝘁𝗮𝗿𝗮𝗻𝗮.....𝘄𝗮𝘁𝗮𝗾𝗶𝗹𝗮 𝗱𝗮𝗿𝗲 𝗻𝗲 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝗺𝘂𝘀𝘂 𝘀𝘂𝗸𝗮 𝘄𝘂𝗰𝗲 𝗱𝗮 𝗶𝘁𝗮,𝗮𝗺𝗺𝗮 𝗸𝗼𝗺𝗮 𝗺𝗲𝘆𝗲 𝗻𝗮𝘀𝗮𝗻 𝗵𝗮𝗺𝗺𝗮𝗻𝗸𝘂 𝘇𝗮𝗶 𝗸𝗮𝘄𝗼𝘁𝗮 𝘁𝗮𝗯𝗯𝗮𝘀 𝗸𝗼𝗱𝗮 𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗯𝗮𝘆𝗮 𝗻𝗲" . 𝗧𝗮𝘆𝗶 𝗺𝗮𝗴𝗮𝗻𝗮𝗿 𝗰𝗶𝗸𝗶𝗻 𝘀𝗼𝗻 𝗸𝗮𝘄𝗮𝗿𝘄𝗮 𝗱𝗮 𝗮𝗺𝗻𝗮 𝘁𝘂𝗻𝗮𝗻𝗶𝗻 𝗸𝗼𝗺𝗮𝗶,𝗱𝘂𝗸 𝗱𝗮 𝗶𝘁𝗮𝗺𝗮 𝘁𝗮𝘀𝗼 𝗾𝘄𝗮𝗿𝗮𝗶 𝗮 𝘀𝗵𝗶𝗴𝗼 𝗱𝗮 𝗶𝘁𝗮𝗻,𝗱𝗼𝗻 𝗮𝗸𝘄𝗮𝗶 𝗺𝗮𝗴𝗮𝗻𝗴𝗮𝗻𝘂 𝗺𝗮𝘀𝘂 𝘆𝗮𝘄𝗮 𝗱𝗮 𝘁𝗮𝗸𝗲𝘀𝗼 𝘁𝗮𝘆𝗶 𝗱𝗮 𝗶𝘁𝗮.

"𝗔𝗺𝗺𝗮 𝗮𝗻𝗻𝗶 𝘆𝗮𝘂𝘀𝗵𝗲?,𝗻𝗶 𝗸𝗼 𝗴𝗼𝗯𝗲 𝗻𝗲 𝗴𝗮𝗻𝗶 𝗻𝗮𝗸𝗲𝘆𝗶 𝘁𝗮𝘆𝗶 𝗻𝗶𝘀𝗮"

"𝗦𝗮𝗶 𝗸𝗶𝘆𝗶 𝗳𝗶𝗳𝗳𝗶𝗸𝗲 𝗸𝗶𝗷𝗲 𝗮𝗶 𝘀𝗮𝗿𝗸𝗶𝗻 𝗴𝗮𝗿𝗮𝗷𝗲" 𝗦𝗮𝗱𝗱𝗶𝗾 𝗱𝗮𝗸𝗲 𝘀𝗵𝗶𝗴𝗼𝘄𝗮 𝗿𝗶𝗾𝗲 𝗱𝗮 𝗹𝗲𝗱𝗮 𝗮 𝗵𝗮𝗻𝗻𝘂𝗻𝘀𝗵𝗶 𝗱𝗮𝗸𝗲 𝗱𝗮𝘂𝗸𝗲 𝗱𝗮 𝘁𝗮𝗺𝗯𝗮𝗿𝗶𝗻 𝘄𝗮𝗻𝗶 𝗯𝗮𝗯𝗯𝗮𝗻 𝗸𝗮𝗺𝗳𝗮𝗻𝗶 𝗱𝗮 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝘀𝗵𝘂𝗵𝘂𝗿𝗮 𝘄𝗮𝗷𝗲𝗻 𝗳𝗶𝗱𝗱𝗮 𝘀𝘂𝘁𝘂𝗿𝘂 𝗻𝗮 𝗺𝗮𝗻𝘆𝗮𝗻 𝗺𝘂𝘁𝗮𝗻𝗲. 𝗝𝘂𝘆𝗮𝘄𝗮 𝘁𝗮𝘆𝗶 𝘁𝗮 𝗱𝘂𝗯𝗲𝘀𝗵𝗶 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝘀𝗮𝗸𝗲 𝗯𝗮𝘁𝗮 𝗿𝗮𝗶,𝘀𝗮𝗶 𝘁𝗮 𝘁𝘀𝘂𝗸𝗲 𝗯𝗮𝗸𝗶 𝗸𝗮𝘄𝗮𝗶 𝘁𝗮 𝗸𝗼𝗺𝗮 𝘁𝗮 𝘇𝗮𝘂𝗻𝗮 𝗯𝗮 𝘁𝗮𝗿𝗲 𝗱𝗮𝘁𝗮 𝘀𝗮𝗸𝗲 𝗰𝗲𝘄𝗮 𝗸𝗼𝗺𝗮𝗶 𝗯𝗮,𝗱𝗼𝗻 𝘁𝗮 𝘀𝗮𝗻 𝗺𝘂𝗱𝗱𝗶𝗻 𝘁𝗮𝗰𝗲 𝘇𝗮𝘁𝗮 𝘀𝗮𝗸𝗲 𝗺𝗮𝗴𝗮𝗻𝗮𝗿 𝘇𝗮𝘀𝘂 𝘆𝗶𝘁𝗮 𝘀𝗮'𝗶𝗻𝘀𝗮 𝗻𝗲 𝗸𝗮𝘄𝗮𝗶 𝗱𝗮 𝘀𝗮𝗱𝗱𝗶𝗾,𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗾𝗮𝗿𝘀𝗵𝗲 𝘆𝗮 𝘀𝗮𝗸𝗮𝘁𝗮 𝗸𝘂𝗸𝗮.

"𝗔𝗻𝗻𝗶 𝗸𝗲𝘆 𝗻𝗮 𝘀𝗮𝘀𝘀𝗮𝗻 𝗕𝗕 𝗳𝗮𝗿𝗼𝘂𝗾,𝘆𝗮𝗰𝗲 𝗻𝗮 𝘀𝗮𝗸𝗮 𝗺𝘂𝘀𝘂 𝗸𝗮𝘆𝗮𝗻 𝗻𝗮𝗻 𝗮 𝗰𝗶𝗸𝗶,𝗵𝗮𝗺𝗺𝗮 𝘇𝗮𝗶𝘇𝗼 𝘆𝗮 𝘀𝗵𝗶𝗿𝘆𝗮". 𝗪𝗮𝗶𝘄𝗮𝘆𝗮𝘄𝗮 𝘁𝗮𝘆𝗶 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝗯𝗮𝘄𝗮 𝗮𝗺𝗻𝗮 𝘂𝗺𝗮𝗿𝗻𝗶 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝗺𝗮𝘁𝗮 𝗻𝘂𝗻𝗶 𝗱𝗮 𝗶𝗻𝗱𝗮 𝘁𝗮 𝗮𝗷𝗶𝘆𝗲𝘀𝗵𝗶.


"𝗕𝗮 𝗶𝗻𝗱𝗮 𝘇𝗮𝗸𝗮𝗷𝗲 𝗳𝗮 𝘀𝗮𝗶𝗸𝗮 𝗸𝗮𝗺𝗺𝗮𝗹𝗮 𝘀𝗵𝗶𝗿𝘆𝗮𝘄𝗮 𝗻𝗮 𝗿𝗮𝗸𝗮𝗸𝗮 𝗸𝗮 𝘆𝗶𝘄𝗮 𝗮𝗻𝗻𝗶 𝘀𝗮𝗹𝗹𝗮𝗺𝗮......𝗱𝗼𝗻 𝗯𝗮 𝘇𝗮𝗸𝗮 𝗵𝗮𝗻𝗮𝗻𝗶 𝗸𝘄𝗮𝗻𝗰𝗶𝘆𝗮 𝗱𝗮 𝘄𝘂𝗿𝗶 𝗯𝗮 𝘆𝗮𝘂......𝘆𝗮𝗱𝗱𝗮 𝗻𝗮 𝗴𝗮𝗷𝗶 𝗱𝗶𝗻𝗻𝗮𝗻 𝗯𝗮𝗰𝗰𝗶 𝗻𝗮𝗸𝗲 𝗯𝘂𝗾𝗮𝘁𝗮 𝗺𝗲 𝘁𝘀𝗮𝗵𝗼.....𝗸𝗼 𝗳𝗮𝗻𝗻𝗮 𝗵𝗶𝗱𝗶𝗺𝗮𝗿𝗸𝗮 𝘁𝗮 𝗵𝗮𝗻𝗮𝗺𝗶𝗻 𝗷𝗶𝗻 𝗺𝘂𝗿𝘆𝗮𝗿𝘁𝗮" 𝗙𝗮𝗿𝗼𝘂𝗾 𝗱𝗮𝘆𝗮 𝗿𝗶𝗾𝗼 𝗳𝘂𝗮𝗱 𝘄𝗮𝗻𝗱𝗮 𝗸𝗲 𝗾𝗼𝗾𝗮𝗿𝗶𝗻 𝘄𝘂𝗰𝗲𝘄𝗮 𝗸𝗮𝗶 𝘁𝘀𝗮𝘆𝗲 𝗰𝗶𝗸𝗶𝗻 𝗴𝗶𝗱𝗮𝗻 𝘆𝗮 𝗳𝗮𝗱𝗮.

𝗪𝗮𝗶𝘄𝗮𝘆𝗼𝘄𝗮 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝘆𝗮 𝗸𝗮𝗹𝗹𝗶 𝗳𝗮𝗿𝗼𝘂𝗾

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login